< Proverbes 22 >
1 Une bonne renommée est préférable à de grandes richesses, et la bonne grâce à l’argent et à l’or.
An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
2 Le riche et le pauvre se rencontrent: l’Éternel les a tous faits.
Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
3 L’homme avisé voit le mal et se cache; mais les simples passent outre et en portent la peine.
Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
4 La fin de la débonnaireté, de la crainte de l’Éternel, c’est la richesse, et la gloire, et la vie.
Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
5 Il y a des épines, des pièges, sur la voie du pervers; celui qui garde son âme s’en éloigne.
A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
6 Élève le jeune garçon selon la règle de sa voie; même lorsqu’il vieillira, il ne s’en détournera point.
Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
7 Le riche gouverne les pauvres, et celui qui emprunte est serviteur de l’homme qui prête.
Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
8 Qui sème l’injustice moissonnera le malheur, et la verge de son courroux prendra fin.
Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
9 [Celui qui a] l’œil bienveillant sera béni, car il donne de son pain au pauvre.
Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
10 Chasse le moqueur, et la querelle s’en ira, et les disputes et la honte cesseront.
Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
11 Celui qui aime la pureté de cœur a la grâce sur les lèvres, [et] le roi est son ami.
Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
12 Les yeux de l’Éternel gardent la connaissance, mais il renverse les paroles du perfide.
Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
13 Le paresseux dit: Il y a un lion là dehors, je serai tué au milieu des rues!
Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
14 La bouche des étrangères est une fosse profonde; celui contre qui l’Éternel est irrité y tombera.
Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
15 La folie est liée au cœur du jeune enfant; la verge de la correction l’éloignera de lui.
Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
16 Celui qui opprime le pauvre, ce sera pour l’enrichir; celui qui donne au riche, ce sera pour le faire tomber dans l’indigence.
Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
17 Incline ton oreille et écoute les paroles des sages, et applique ton cœur à ma science;
Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
18 car c’est une chose agréable si tu les gardes au-dedans de toi: elles seront disposées ensemble sur tes lèvres.
gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
19 Afin que ta confiance soit en l’Éternel, je te [les] ai fait connaître à toi, aujourd’hui.
Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
20 Ne t’ai-je pas écrit des choses excellentes en conseils et en connaissance,
Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
21 pour te faire connaître la sûre norme des paroles de vérité, afin que tu répondes des paroles de vérité à ceux qui t’envoient?
ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
22 Ne pille pas le pauvre, parce qu’il est pauvre, et ne foule pas l’affligé à la porte;
Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
23 car l’Éternel prendra en main leur cause, et dépouillera l’âme de ceux qui les dépouillent.
gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
24 Ne sois pas l’ami de l’homme colère, et n’entre pas chez l’homme violent;
Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
25 de peur que tu n’apprennes ses sentiers, et que tu n’emportes un piège dans ton âme.
in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
26 Ne sois point parmi ceux qui frappent dans la main, parmi ceux qui se rendent caution pour des dettes:
Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
27 si tu n’avais pas de quoi payer, pourquoi voudrais-tu qu’on prenne ton lit de dessous toi?
gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
28 Ne recule pas la borne ancienne que tes pères ont faite.
Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
29 As-tu vu un homme diligent dans son travail? il se tiendra devant les rois, il ne se tiendra pas devant des gens obscurs.
Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.