< Proverbes 2 >

1 Mon fils, si tu reçois mes paroles et que tu caches par-devers toi mes commandements
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2 pour rendre ton oreille attentive à la sagesse, si tu inclines ton cœur à l’intelligence,
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3 si tu appelles le discernement, si tu adresses ta voix à l’intelligence,
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4 si tu la cherches comme de l’argent et que tu la recherches comme des trésors cachés,
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5 alors tu comprendras la crainte de l’Éternel et tu trouveras la connaissance de Dieu.
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6 Car l’Éternel donne la sagesse; de sa bouche [procèdent] la connaissance et l’intelligence:
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7 il réserve de sains conseils pour les hommes droits; il est un bouclier pour ceux qui marchent dans l’intégrité,
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8 protégeant les sentiers de juste jugement et gardant la voie de ses saints.
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9 Alors tu discerneras la justice et le juste jugement et la droiture, toute bonne voie.
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
10 Si la sagesse entre dans ton cœur et si la connaissance est agréable à ton âme,
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
11 la réflexion te préservera, l’intelligence te protégera:
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
12 Pour te sauver du mauvais chemin, de l’homme qui prononce des choses perverses,
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
13 [de ceux] qui abandonnent les sentiers de la droiture pour marcher dans les voies de ténèbres,
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
14 qui se réjouissent à mal faire, qui s’égaient en la perversité du mal,
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
15 dont les sentiers sont tortueux et qui s’égarent dans leurs voies;
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
16 Pour te sauver de la femme étrangère, de l’étrangère qui use de paroles flatteuses,
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
17 qui abandonne le guide de sa jeunesse, et qui a oublié l’alliance de son Dieu;
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
18 – car sa maison penche vers la mort, et ses chemins vers les trépassés:
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19 aucun de ceux qui entrent auprès d’elle ne revient ni n’atteint les sentiers de la vie;
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
20 – afin que tu marches dans la voie des gens de bien, et que tu gardes les sentiers des justes.
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
21 Car les hommes droits habiteront le pays, et les hommes intègres y demeureront de reste;
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
22 mais les méchants seront retranchés du pays, et les perfides en seront arrachés.
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.

< Proverbes 2 >