< Proverbes 16 >
1 La préparation du cœur est à l’homme, mais de l’Éternel est la réponse de la langue.
Ga mutum ne shirye-shiryen zuciya suke, amma daga Ubangiji ne amshin harshe kan zo.
2 Toutes les voies d’un homme sont pures à ses propres yeux, mais l’Éternel pèse les esprits.
Dukan hanyoyin mutum sukan yi kamar marar laifi ne gare shi, amma Ubangiji yakan auna manufofi.
3 Remets tes affaires à l’Éternel, et tes pensées seront accomplies.
Ka miƙa wa Ubangiji dukan abin da kake yi, shirye-shiryenka kuwa za su yi nasara.
4 L’Éternel a tout fait pour lui-même, et même le méchant pour le jour du malheur.
Ubangiji yana yin kome domin amfaninsa, har ma da mugaye domin ranar masifa.
5 Tout cœur orgueilleux est en abomination à l’Éternel; certes, il ne sera pas tenu pour innocent.
Ubangiji yana ƙyamar dukan zuciya mai girman kai. Ka tabbata da wannan. Ba za su kuɓuta daga hukunci ba.
6 Par la bonté et par la vérité, propitiation est faite pour l’iniquité, et par la crainte de l’Éternel on se détourne du mal.
Ta wurin ƙauna da aminci akan yi kafarar zunubi; ta wurin tsoron Ubangiji mutum kan guji mugunta.
7 Quand les voies d’un homme plaisent à l’Éternel, il met ses ennemis mêmes en paix avec lui.
Sa’ad da hanyoyin mutum sun gamshi Ubangiji, yakan sa abokan gāban mutumin ma su zauna lafiya da shi.
8 Mieux vaut peu avec justice, que beaucoup de revenu sans ce qui est juste.
Gara ka sami kaɗan ta hanyar adalci da sami riba mai yawa ta hanyar rashin gaskiya.
9 Le cœur de l’homme se propose sa voie, mais l’Éternel dispose ses pas.
’Yan Adam sukan yi shirye-shiryensu a zukatansu, amma Ubangiji ne yake da ikon cika matakansa.
10 Un oracle est sur les lèvres du roi, sa bouche n’erre pas dans le jugement.
Leɓunan sarki kan yi magana kamar ta wurin ikon Allah, kuma bai kamata bakinsa ya yi kuskure a yanke shari’a ba.
11 La balance et les plateaux justes sont de l’Éternel; tous les poids du sac sont son ouvrage.
Ma’aunai da magwajin gaskiya daga Ubangiji ne; dukan ma’aunai da suke cikin jaka yinsa ne.
12 C’est une abomination pour les rois de faire l’iniquité; car, par la justice, le trône est rendu ferme.
Sarakuna suna ƙyamar abin da ba shi da kyau, gama an kafa kujerar sarauta ta wurin adalci ne.
13 Les lèvres justes sont le plaisir des rois, et le [roi] aime celui qui parle droitement.
Sarakuna sukan ji daɗi leɓuna masu yin gaskiya; sukan darjanta mutumin da yake faɗin gaskiya.
14 La fureur du roi, ce sont des messagers de mort; mais l’homme sage l’apaisera.
Fushin sarki ɗan saƙon mutuwa ne, amma mai hikima yakan faranta masa rai.
15 Dans la lumière de la face du roi est la vie, et sa faveur est comme un nuage de pluie dans la dernière saison.
Sa’ad da fuskar sarki ta haska, yana nufin rai ke nan; tagomashinsa yana kamar girgijen ruwa a bazara.
16 Combien acquérir la sagesse est meilleur que l’or fin, et acquérir l’intelligence, préférable à l’argent!
Ya ma fi kyau ka sami hikima fiye da zinariya, ka zaɓi fahimi a maimakon azurfa!
17 Le chemin des hommes droits, c’est de se détourner du mal; celui-là garde son âme qui veille sur sa voie.
Buɗaɗɗiyar hanyar masu aikata gaskiya kan guje wa mugunta; duk wanda yake lura da hanyarsa yakan lura da ransa.
18 L’orgueil va devant la ruine, et l’esprit hautain devant la chute.
Girmankai yakan zo kafin hallaka, girman kai yakan zo kafin fāɗuwa.
19 Mieux vaut être humble d’esprit avec les débonnaires, que de partager le butin avec les orgueilleux.
Gara ka zama ɗaya daga cikin matalauta masu sauƙinkai, da ka raba ganima da masu girman kai.
20 Celui qui prend garde à la parole trouvera le bien, et qui se confie en l’Éternel est bienheureux.
Duk wanda ya mai da hankali ga umarni yakan yi nasara, kuma mai albarka ne wanda yake dogara ga Ubangiji.
21 L’homme sage de cœur sera appelé intelligent, et la douceur des lèvres accroît la science.
Akan ce da masu hikima a zuciya hazikai, kuma kalmomi masu daɗi kan inganta umarni.
22 L’intelligence est une fontaine de vie pour ceux qui la possèdent, mais l’instruction des fous est folie.
Fahimi shi ne maɓulɓular rai ga waɗanda suke da shi, amma wauta kan kawo hukunci ga wawaye.
23 Le cœur du sage rend sa bouche sensée, et, sur ses lèvres, accroît la science.
Zuciyar mai hikima kan bi da bakinsa, kuma leɓunansa kan inganta umarni.
24 Les paroles agréables sont un rayon de miel, douceur pour l’âme et santé pour les os.
Kalmomi masu daɗi suna kama da kakin zuma, mai zaƙi ga rai da kuma warkarwa ga ƙasusuwa.
25 Il y a telle voie qui semble droite à un homme, mais des voies de mort en sont la fin.
Akwai hanyar da ta yi kamar daidai ga mutum, amma a ƙarshe takan kai ga mutuwa.
26 L’âme de celui qui travaille, travaille pour lui, car sa bouche l’y contraint.
Marmarin cin abinci yakan yi wa ɗan ƙodago aiki; yunwarsa kan sa ya ci gaba.
27 L’homme de Bélial creuse, [à la recherche] du mal, et sur ses lèvres il y a comme un feu brûlant.
Mutumin banza yakan ƙulla mugunta, kuma jawabinsa yana kama da wuta mai ƙuna.
28 L’homme pervers sème les querelles, et le rapporteur divise les intimes amis.
Fitinannen mutum yakan zuga tashin hankali, mai gulma kuma yakan raba abokai na kusa.
29 L’homme violent entraîne son compagnon et le fait marcher dans une voie qui n’est pas bonne.
Mutum mai tā-da-na-zaune-tsaye yakan ruɗi maƙwabcinsa ya kai shi a hanyar da ba ta da kyau.
30 Celui qui ferme ses yeux pour machiner la perversité, celui qui pince ses lèvres, accomplit le mal.
Duk wanda ya ƙyifce da idonsa yana ƙulla maƙarƙashiya ce; duk wanda ya murguɗa leɓunansa yana niyya aikata mugunta ke nan.
31 Les cheveux blancs sont une couronne de gloire s’ils se trouvent dans la voie de la justice.
Furfura rawani ne mai daraja; akan same ta ta wurin yin rayuwa ta adalci.
32 Qui est lent à la colère vaut mieux que l’homme fort, et qui gouverne son esprit vaut mieux que celui qui prend une ville.
Gara ka zama mai haƙuri da ka zama jarumi, ya fi kyau ka iya mallakar kanka fiye da mallakar birane.
33 On jette le sort dans le giron, mais toute décision est de par l’Éternel.
Akan jefa ƙuri’a a kan cinya, amma kowace shawara mai kyau daga Ubangiji ne.