< Nombres 34 >

1 Et l’Éternel parla à Moïse, disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Commande aux fils d’Israël, et dis-leur: Quand vous serez entrés dans le pays de Canaan, ce sera ici le pays qui vous écherra en héritage, le pays de Canaan selon ses limites.
“Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
3 Votre côté méridional sera depuis le désert de Tsin, le long d’Édom, et votre frontière méridionale sera depuis le bout de la mer Salée, vers l’orient;
“‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
4 et votre frontière tournera au midi de la montée d’Akrabbim, et passera vers Tsin; et elle s’étendra au midi de Kadès-Barnéa, et sortira par Hatsar-Addar, et passera vers Atsmon;
tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
5 et la frontière tournera depuis Atsmon vers le torrent d’Égypte, et aboutira à la mer.
inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
6 Et, pour frontière occidentale, vous aurez la grande mer et [ses] côtes; ce sera là votre frontière occidentale.
“‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
7 Et ce sera ici votre frontière septentrionale: depuis la grande mer, vous marquerez pour vous la montagne de Hor;
“‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
8 depuis la montagne de Hor, vous tracerez jusqu’à l’entrée de Hamath, et la frontière aboutira vers Tsedad;
za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
9 et la frontière sortira vers Ziphron, et aboutira à Hatsar-Énan; ce sera là votre frontière septentrionale.
tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
10 Et vous vous tracerez, pour frontière orientale, depuis Hatsar-Énan à Shepham;
“‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
11 et la frontière descendra de Shepham vers Ribla, à l’orient d’Aïn; et la frontière descendra, et touchera l’extrémité de la mer de Kinnéreth, à l’orient;
Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
12 et la frontière descendra au Jourdain, et aboutira à la mer Salée. Ce sera là votre pays, selon ses limites, tout autour.
Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
13 Et Moïse commanda aux fils d’Israël, disant: C’est là le pays que vous recevrez en héritage par le sort, lequel l’Éternel a commandé de donner aux neuf tribus et à la demi-tribu;
Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
14 car la tribu des fils des Rubénites, selon leurs maisons de pères, et la tribu des fils des Gadites, selon leurs maisons de pères, et la demi-tribu de Manassé, ont pris leur héritage.
saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
15 Les deux tribus et la demi-tribu ont pris leur héritage en deçà du Jourdain de Jéricho, à l’orient, vers le levant.
Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
16 Et l’Éternel parla à Moïse, disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 Ce sont ici les noms des hommes qui vous partageront le pays: Éléazar le sacrificateur, et Josué, fils de Nun.
“Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
18 – Et vous prendrez un prince de chaque tribu, pour faire le partage du pays.
Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
19 Et ce sont ici les noms des hommes: pour la tribu de Juda, Caleb, fils de Jephunné;
“Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
20 et pour la tribu des fils de Siméon, Samuel, fils d’Ammihud;
Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
21 pour la tribu de Benjamin, Élidad, fils de Kislon;
Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
22 et pour la tribu des fils de Dan, un prince, Bukki, fils de Jogli;
Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
23 pour les fils de Joseph, pour la tribu des fils de Manassé, un prince, Hanniel, fils d’Éphod;
Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
24 et pour la tribu des fils d’Éphraïm, un prince, Kemuel, fils de Shiphtan;
Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
25 et pour la tribu des fils de Zabulon, un prince, Élitsaphan, fils de Parnac;
Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
26 et pour la tribu des fils d’Issacar, un prince, Paltiel, fils d’Azzan;
Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
27 et pour la tribu des fils d’Aser, un prince, Akhihud, fils de Shelomi;
Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
28 et pour la tribu des fils de Nephthali, un prince, Pedahel, fils d’Ammihud.
Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
29 Ce sont là ceux auxquels l’Éternel commanda de distribuer l’héritage aux fils d’Israël dans le pays de Canaan.
Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.

< Nombres 34 >