< Nombres 2 >

1 Et l’Éternel parla à Moïse et à Aaron, disant:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
2 Les fils d’Israël camperont chacun près de sa bannière, sous les enseignes de leurs maisons de pères; ils camperont autour de la tente d’assignation, à distance, vis-à-vis.
“Duk sa’ad da Isra’ilawa suka yi sansani, kowane mutum zai sauka a inda tutar ƙungiyar kabilarsa take. Sansanin zai kasance a kewaye da Tentin Sujada.”
3 [Voici] ceux qui camperont à l’orient, vers le levant, [sous] la bannière du camp de Juda, selon leurs armées: le prince des fils de Juda, Nakhshon, fils d’Amminadab,
Kabilar Yahuda za su yi sansani bisa ga ƙa’idarsu a gabas, wajen fitowar rana. Shugaban mutanen Yahuda kuwa shi ne Nashon ɗan Amminadab.
4 et son armée; et ses dénombrés, 74 600.
Yawan mutanen sashensa 74,600 ne.
5 – Et ceux qui camperont près de lui, sont la tribu d’Issacar: le prince des fils d’Issacar, Nethaneël, fils de Tsuar,
Kabilar Issakar za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Netanel ɗan Zuwar.
6 et son armée; et ses dénombrés, 54 400.
Yawan mutanen sashensa 54,400 ne.
7 – [Avec eux] sera la tribu de Zabulon: le prince des fils de Zabulon, Éliab, fils de Hélon,
Kabilar Zebulun za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Eliyab ɗan Helon.
8 et son armée; et ses dénombrés, 57 400.
Yawan mutanen sashensa 57,400 ne.
9 – Tous les dénombrés du camp de Juda, 186 400, selon leurs armées; ils partiront les premiers.
Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Yahuda bisa ga sashensu sun kai 186,400. Su ne za su ja gaba.
10 La bannière du camp de Ruben, selon ses armées, sera vers le midi: le prince des fils de Ruben, Élitsur, fils de Shedéur,
A kudu, a nan ne sashe sansanin mutanen Ruben a ƙarƙashin ƙa’idarsu, za su yi sansani. Shugaban mutanen Ruben shi ne Elizur ɗan Shedeyur.
11 et son armée; et ses dénombrés, 46 500.
Yawan mutanen sashensa 46,500 ne.
12 – Et ceux qui camperont près de lui, sont la tribu de Siméon: le prince des fils de Siméon, Shelumiel, fils de Tsurishaddaï,
Kabilar Simeyon za su yi sansani biye da su. Shugaban mutanensa shi ne Shelumiyel ɗan Zurishaddai.
13 et son armée; et ses dénombrés, 59 300.
Yawan mutanen sashensa 59,300 ne.
14 – Et [avec eux] sera la tribu de Gad: le prince des fils de Gad, Éliasaph, fils de Rehuel,
Kabilar Gad za su zama na biye. Shugaban mutanensa shi ne Eliyasaf ɗan Reyuwel.
15 et son armée; et ses dénombrés, 45 650.
Yawan mutanen sashensa 45,650 ne.
16 – Tous les dénombrés du camp de Ruben, 151 450, selon leurs armées; et ils partiront les seconds.
Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Ruben, bisa ga sashensu sun kai 151,450. Su ne za su zama na biyu in za a tashi.
17 Et la tente d’assignation partira, le camp des Lévites étant au milieu des camps; comme ils auront campé, ainsi ils partiront, chacun à sa place, selon leurs bannières.
Sa’an nan Lawiyawa ɗauke da Tentin Sujada za su kasance a tsakiyar sansani sa’ad da aka tashi tafiya. Za su kama hanya kamar yadda aka dokace su su zauna a sansani, kowa a wurinsa a ƙarƙashin ƙa’idarsu.
18 La bannière du camp d’Éphraïm, selon ses armées, sera vers l’occident: le prince des fils d’Éphraïm, Élishama, fils d’Ammihud,
Ta wajen yamma kuma sashen Efraim za su yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugaban mutanensa, shi ne Elishama ɗan Ammihud.
19 et son armée; et ses dénombrés, 40 500.
Yawan mutanen sashensa 40,500 ne.
20 – Et près de lui la tribu de Manassé: le prince des fils de Manassé, Gameliel, fils de Pedahtsur,
Kabilar Manasse ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Gamaliyel ɗan Fedazur.
21 et son armée; et ses dénombrés, 32 200.
Yawan mutanen sashensa 32,200 ne.
22 – Et [avec eux] sera la tribu de Benjamin: le prince des fils de Benjamin, Abidan, fils de Guidhoni,
Na biye da su su ne mutanen Benyamin. Shugaban mutanensu kuwa Abidan ɗan Gideyoni.
23 et son armée; et ses dénombrés, 35 400.
Yawan mutanen sashensa 35,400 ne.
24 – Tous les dénombrés du camp d’Éphraïm, 108 100, selon leurs armées; et ils partiront les troisièmes.
Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 108,100 ne. Su ne za su zama na uku sa’ad da za a tashi.
25 La bannière du camp de Dan, selon ses armées, sera vers le nord: le prince des fils de Dan, Akhiézer, fils d’Ammishaddaï,
A arewa za a sami sashen sansanin Dan, a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugabansu shi ne Ahiyezer ɗan Ammishaddai.
26 et son armée; et ses dénombrés, 62 700.
Yawan mutanen sashensa 62,700 ne.
27 – Et ceux qui camperont près de lui, sont la tribu d’Aser: le prince des fils d’Aser, Paghiel, fils d’Ocran,
Kabilar Asher ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Fagiyel ɗan Okran.
28 et son armée; et ses dénombrés, 41 500.
Yawan mutanen sashensa 41,500 ne.
29 – Et [avec eux] sera la tribu de Nephthali: le prince des fils de Nephthali, Akhira, fils d’Énan,
Kabilar Naftali za su zama na biye da su. Shugaban mutanen kuwa shi ne Ahira ɗan Enan.
30 et son armée; et ses dénombrés, 53 400.
Yawan mutanen sashensa 53,400 ne
31 – Tous les dénombrés du camp de Dan, 157 600; ils partiront les derniers, selon leurs bannières.
Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 157,600. Su ne za su zama na ƙarshe, ƙarƙashin ƙa’idarsu.
32 Ce sont là les dénombrés des fils d’Israël, selon leurs maisons de pères. Tous les dénombrés des camps, selon leurs armées, furent 603 550.
Waɗannan su ne Isra’ilawan da aka a ƙidaya bisa ga iyalansu. Dukansu da suke a sansani, mutane 603,550 ne.
33 Mais les Lévites ne furent pas dénombrés parmi les fils d’Israël, ainsi que l’Éternel l’avait commandé à Moïse.
Ba a dai ƙidaya Lawiyawa tare da sauran Isra’ilawa ba yadda Ubangiji ya umarci Musa.
34 Et les fils d’Israël firent selon tout ce que l’Éternel avait commandé à Moïse: ainsi ils campèrent selon leurs bannières, et ainsi ils partirent, chacun selon leurs familles, selon leurs maisons de pères.
Saboda haka Isra’ilawa suka yi duk ko mene ne da Ubangiji ya umarci Musa. Ta haka ne suka yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu kowanne tare da kabilarsa da danginsa.

< Nombres 2 >