< Nombres 13 >

1 Et l’Éternel parla à Moïse, disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Envoie des hommes, et ils reconnaîtront le pays de Canaan, que je donne aux fils d’Israël; vous enverrez un homme pour chaque tribu de ses pères, tous des princes parmi eux.
“Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
3 Et Moïse les envoya du désert de Paran, selon le commandement de l’Éternel. Tous ces hommes étaient des chefs des fils d’Israël.
Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
4 Et ce sont ici leurs noms: pour la tribu de Ruben, Shammua, fils de Zaccur;
Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
5 pour la tribu de Siméon, Shaphath, fils de Hori;
Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
6 pour la tribu de Juda, Caleb, fils de Jephunné;
Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
7 pour la tribu d’Issacar, Jighal, fils de Joseph;
Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
8 pour la tribu d’Éphraïm, Osée, fils de Nun;
Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
9 pour la tribu de Benjamin, Palti, fils de Raphu;
daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
10 pour la tribu de Zabulon, Gaddiel, fils de Sodi;
Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
11 pour la tribu de Joseph, pour la tribu de Manassé, Gaddi, fils de Susi;
Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
12 pour la tribu de Dan, Ammiel, fils de Guemalli;
Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
13 pour la tribu d’Aser, Sethur, fils de Micaël;
Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
14 pour la tribu de Nephthali, Nakhbi, fils de Vophsi;
Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
15 pour la tribu de Gad, Gueuël, fils de Maki.
Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
16 – Ce sont là les noms des hommes que Moïse envoya pour reconnaître le pays. Et Moïse appela Osée, fils de Nun, Josué.
Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
17 Et Moïse les envoya pour reconnaître le pays de Canaan, et leur dit: Montez de ce côté, par le midi; et vous monterez [dans] la montagne;
Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
18 et vous verrez le pays, ce qu’il est, et le peuple qui l’habite; s’il est fort ou faible, s’il est en petit nombre ou en grand nombre;
Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
19 et quel est le pays où il habite, s’il est bon ou mauvais; et quelles sont les villes dans lesquelles il habite, si c’est dans des camps ou dans des villes murées;
Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
20 et quel est le pays, s’il est gras ou maigre, s’il y a des arbres ou s’il n’y en a pas. Ayez bon courage, et prenez du fruit du pays. Or c’était le temps des premiers raisins.
Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
21 Et ils montèrent et reconnurent le pays, depuis le désert de Tsin jusqu’à Rehob, quand on vient à Hamath.
Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
22 Et ils montèrent par le midi, et vinrent jusqu’à Hébron; et là étaient Akhiman, Shéshaï et Thalmaï, enfants d’Anak. Et Hébron avait été bâtie sept ans avant Tsoan d’Égypte.
Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
23 Et ils vinrent jusqu’au torrent d’Eshcol, et coupèrent de là un sarment avec une grappe de raisin; et ils le portèrent à deux au moyen d’une perche, et des grenades et des figues.
Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
24 On appela ce lieu-là torrent d’Eshcol, à cause de la grappe que les fils d’Israël y coupèrent.
Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
25 Et ils revinrent de la reconnaissance du pays au bout de 40 jours.
A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
26 Et ils allèrent, et arrivèrent auprès de Moïse et d’Aaron, et de toute l’assemblée des fils d’Israël, au désert de Paran, à Kadès; et ils leur rendirent compte, ainsi qu’à toute l’assemblée, et leur montrèrent le fruit du pays.
Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
27 Et ils racontèrent à Moïse, et dirent: Nous sommes allés dans le pays où tu nous as envoyés; et vraiment il est ruisselant de lait et de miel, et en voici le fruit.
Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
28 Seulement, le peuple qui habite dans le pays est fort, et les villes sont fortifiées, très grandes; et nous y avons vu aussi les enfants d’Anak.
Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
29 Amalek habite le pays du midi; et le Héthien, le Jébusien et l’Amoréen habitent la montagne; et le Cananéen habite le long de la mer et sur le rivage du Jourdain.
Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
30 Et Caleb fit taire le peuple devant Moïse, et dit: Montons hardiment et prenons possession du [pays], car nous sommes bien capables de le faire.
Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
31 Mais les hommes qui étaient montés avec lui, dirent: Nous ne sommes pas capables de monter contre ce peuple, car il est plus fort que nous.
Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
32 Et ils décrièrent devant les fils d’Israël le pays qu’ils avaient reconnu, disant: Le pays par lequel nous avons passé pour le reconnaître est un pays qui dévore ses habitants, et tout le peuple que nous y avons vu est de haute stature.
Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
33 Et nous y avons vu les géants, fils d’Anak, qui est [de la race] des géants; et nous étions à nos yeux comme des sauterelles, et nous étions de même à leurs yeux.
Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”

< Nombres 13 >