< Matthieu 5 >
1 Or, voyant les foules, il monta sur la montagne; et lorsqu’il se fut assis, ses disciples s’approchèrent de lui;
Ganin taron mutane, sai ya hau kan gefen dutse ya zauna. Almajiransa kuwa suka zo wurinsa,
2 et ayant ouvert la bouche, il les enseignait, disant:
sai ya fara koya musu. Yana cewa,
3 Bienheureux les pauvres en esprit, car c’est à eux qu’est le royaume des cieux;
“Masu albarka ne waɗanda suke matalauta a ruhu, gama mulkin sama nasu ne.
4 bienheureux ceux qui mènent deuil, car c’est eux qui seront consolés;
Masu albarka ne waɗanda suke makoki, gama za a yi musu ta’aziyya.
5 bienheureux les débonnaires, car c’est eux qui hériteront de la terre;
Masu albarka ne waɗanda suke masu tawali’u, gama za su gāji duniya.
6 bienheureux ceux qui ont faim et soif de la justice, car c’est eux qui seront rassasiés;
Masu albarka ne waɗanda suke jin yunwa da ƙishirwa don gani an yi adalci, gama za a ƙosar da su.
7 bienheureux les miséricordieux, car c’est à eux que miséricorde sera faite;
Masu albarka ne waɗanda suke masu jinƙai, gama za a nuna musu jinƙai.
8 bienheureux ceux qui sont purs de cœur, car c’est eux qui verront Dieu;
Masu albarka ne waɗanda suke masu tsabtar zuciya, gama za su ga Allah.
9 bienheureux ceux qui procurent la paix, car c’est eux qui seront appelés fils de Dieu;
Masu albarka ne waɗanda suke masu ƙulla zumunci, gama za a kira su’ya’yan Allah.
10 bienheureux ceux qui sont persécutés à cause de la justice, car c’est à eux qu’est le royaume des cieux.
Masu albarka ne waɗanda ake tsananta musu don gani an yi adalci, gama mulkin sama nasu ne.
11 Vous êtes bienheureux quand on vous injuriera, et qu’on vous persécutera, et qu’on dira, en mentant, toute espèce de mal contre vous, à cause de moi.
“Masu albarka ne ku, sa’ad da mutane suke zaginku, suna tsananta muku, suna kuma faɗin kowace irin muguwar magana a kanku saboda ni.
12 Réjouissez-vous et tressaillez de joie, car votre récompense est grande dans les cieux; car on a persécuté ainsi les prophètes qui ont été avant vous.
Ku yi murna ku kuma yi farin ciki, domin ladarku mai yawa ne a sama, gama haka suka tsananta wa annabawan da suka riga ku.
13 Vous êtes le sel de la terre; mais si le sel a perdu sa saveur, avec quoi sera-t-il salé? Il n’est plus bon à rien qu’ à être jeté dehors et à être foulé aux pieds par les hommes.
“Ku ne gishirin duniya, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa? Ba shi da sauran amfani, sai dai a zubar da shi mutane kuma su tattaka.
14 Vous êtes la lumière du monde: une ville située sur une montagne ne peut être cachée.
“Ku ne hasken duniya. Birnin da yake a bisan tudu ba ya ɓoyuwa.
15 Aussi n’allume-t-on pas une lampe pour la mettre ensuite sous le boisseau, mais sur le pied de lampe; et elle luit pour tous ceux qui sont dans la maison.
Mutane ba sa ƙuna fitila su rufe ta da murfi. A maimako, sukan ajiye ta a kan wurin ajiye fitila, takan kuma ba da haske ga kowa a cikin gida.
16 Que votre lumière luise ainsi devant les hommes, en sorte qu’ils voient vos bonnes œuvres, et qu’ils glorifient votre Père qui est dans les cieux.
Haka ma, bari haskenku yă haskaka a gaban mutane, domin su ga ayyukanku masu kyau, su kuwa yabi Ubanku da yake cikin sama.
17 Ne pensez pas que je sois venu pour abolir la loi ou les prophètes: je ne suis pas venu pour abolir, mais pour accomplir;
“Kada ku yi tsammani na zo ne domin in kawar da Doka ko kuma Annabawa; ban zo domin in kawar da su ba ne, sai dai domin in ciccika su.
18 car, en vérité, je vous dis: Jusqu’à ce que le ciel et la terre passent, un seul iota ou un seul trait de lettre ne passera point de la loi, que tout ne soit accompli.
Gaskiya nake gaya muku, kafin sama da ƙasa sun shuɗe, babu ko ɗan wasali, babu wani ɗigo ta kowace hanya da zai ɓace daga Dokar, sai an cika kome.
19 Quiconque donc aura supprimé l’un de ces plus petits commandements et aura enseigné ainsi les hommes, sera appelé le plus petit dans le royaume des cieux; et quiconque l’aura pratiqué et enseigné, celui-là sera appelé grand dans le royaume des cieux.
Duk wanda ya karya ɗaya daga cikin mafi ƙanƙanta na umarnan nan, ya kuma koya wa waɗansu su yi haka, za a ce da shi mafi ƙanƙanta a mulkin sama. Amma duk wanda ya aikata, ya kuma koyar da waɗannan umarnai, za a kira shi mai girma a cikin mulkin sama.
20 Car je vous dis que, si votre justice ne surpasse pas celle des scribes et des pharisiens, vous n’entrerez point dans le royaume des cieux.
Gama ina faɗa muku cewa in dai adalcinku bai fi na Farisiyawa da na malaman dokoki ba, faufau, ba za ku shiga mulkin sama ba.
21 Vous avez entendu qu’il a été dit aux anciens: « Tu ne tueras pas; et quiconque tuera, sera passible du jugement ».
“Kun dai ji an faɗa wa mutanen dā cewa, ‘Kada ka yi kisankai; kuma duk wanda ya yi kisankai za a hukunta shi.’
22 Mais moi, je vous dis que quiconque se met en colère légèrement contre son frère sera passible du jugement; et quiconque dira à son frère: “Raca”, sera passible [du jugement] du sanhédrin; et quiconque dira “fou”, sera passible de la géhenne du feu. (Geenna )
Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da ɗan’uwansa, za a hukunta shi. Kuma duk wanda ya ce wa ɗan’uwansa ‘Raka,’za a kai shi gaban Majalisa. Amma duk wanda ya ce, ‘Kai wawa!’ Zai kasance a hatsarin shiga jahannama ta wuta. (Geenna )
23 Si donc tu offres ton don à l’autel, et que là il te souvienne que ton frère a quelque chose contre toi,
“Saboda haka, in kana cikin ba da baikonka a kan bagade, a can kuwa ka tuna cewa ɗan’uwanka yana riƙe da kai a zuci,
24 laisse là ton don devant l’autel, et va d’abord, réconcilie-toi avec ton frère; et alors viens et offre ton don.
sai ka bar baikonka a can gaban bagade. Ka je ka shirya tukuna da ɗan’uwanka; sa’an nan ka zo ka ba da baikonka.
25 Mets-toi promptement d’accord avec ta partie adverse, pendant que tu es en chemin avec elle, de peur que ta partie adverse ne te livre au juge, et que le juge ne te livre au sergent, et que tu ne sois jeté en prison;
“Ka yi hanzari ka shirya al’amura da maƙiyinka wanda yake ƙararka a kotu. Ka yi haka, tun kana tare da shi a kan hanya, in ba haka ba, zai miƙa ka ga alƙali, alƙali kuma yă miƙa ka ga ɗan sanda, mai yiwuwa kuwa a jefa ka a kurkuku.
26 en vérité, je te dis: Tu ne sortiras point de là, jusqu’à ce que tu aies payé le dernier quadrant.
Gaskiya nake gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.
27 Vous avez entendu qu’il a été dit: « Tu ne commettras pas adultère ».
“Kun dai ji an faɗa, ‘Kada ka yi zina.’
28 Mais moi, je vous dis que quiconque regarde une femme pour la convoiter, a déjà commis adultère avec elle dans son cœur.
Amma ina gaya muku, duk wanda ya dubi mace, sa’an nan ya yi sha’awarta a zuci, ya riga ya yi zina ke nan da ita a zuciyarsa.
29 Mais si ton œil droit est pour toi une occasion de chute, arrache-le et jette-le loin de toi; car il est avantageux pour toi qu’un de tes membres périsse, et que tout ton corps ne soit pas jeté dans la géhenne. (Geenna )
In idonka na dama yana sa ka yin zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna )
30 Et si ta main droite est pour toi une occasion de chute, coupe-la et jette-la loin de toi; car il est avantageux pour toi qu’un de tes membres périsse, et que tout ton corps ne soit pas jeté dans la géhenne. (Geenna )
In kuma hannunka na dama yana sa ka yin zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna )
31 Il a été dit aussi: « Si quelqu’un répudie sa femme, qu’il lui donne une lettre de divorce ».
“An kuma faɗa, ‘Duk wanda ya saki matarsa, dole yă ba ta takardar saki.’
32 Mais moi, je vous dis que quiconque répudiera sa femme, si ce n’est pour cause de fornication, la fait commettre adultère; et quiconque épousera une femme répudiée, commet adultère.
Amma ina gaya muku, duk wanda ya saki matarsa in ba a kan laifin zina ba, ya sa ta zama mazinaciya ke nan, kuma duk wanda ya auri macen da mijinta ya sake, shi ma yana zina ne.
33 Vous avez encore entendu qu’il a été dit aux anciens: « Tu ne te parjureras pas, mais tu rendras justement au Seigneur tes serments ».
“Har wa yau dai kun ji an faɗa wa mutane a dā, ‘Kada ka karya alkawarinka, sai dai ka cika alkawaran da ka yi wa Ubangiji.’
34 Mais moi, je vous dis de ne pas jurer du tout; ni par le ciel, car il est le trône de Dieu;
Amma ina gaya muku, Kada ku yi rantsuwa sam, ko da sama, domin kursiyin Allah ne;
35 ni par la terre, car elle est le marchepied de ses pieds; ni par Jérusalem, car elle est la ville du grand Roi.
ko da ƙasa, domin matashin ƙafafunsa ne; ko kuma da Urushalima, domin birnin Babban Sarki ne.
36 Tu ne jureras pas non plus par ta tête, car tu ne peux faire blanc ou noir un cheveu.
Kada kuma ka rantse da kanka, domin ba za ka iya mai da ko gashi ɗaya yă zama fari ko baƙi ba.
37 Mais que votre parole soit: Oui, oui; non, non; car ce qui est de plus vient du mal.
Abin da ya kamata ku ce kawai, shi ne, I, ko A’a. Abin da ya wuce haka kuwa daga wurin Mugun nan yake.
38 Vous avez entendu qu’il a été dit: « Œil pour œil, et dent pour dent ».
“Kun dai ji an faɗa, ‘Ido domin ido, haƙori kuma domin haƙori.’
39 Mais moi, je vous dis: Ne résistez pas au mal; mais si quelqu’un te frappe sur la joue droite, présente-lui aussi l’autre;
Amma ina gaya muku, Kada ku yi tsayayya da mugun mutum. In wani ya mare ka a kumatun dama, juya masa ɗayan ma.
40 et à celui qui veut plaider contre toi et t’ôter ta tunique, laisse-lui encore le manteau;
In kuma wani yana so yă yi ƙararka yă ƙwace rigarka, to, ba shi mayafinka ma.
41 et si quelqu’un veut te contraindre de faire un mille, vas-en deux avec lui.
In wani ya tilasta ka yin tafiya mil ɗaya, to, tafi tare da shi mil biyu.
42 Donne à qui te demande, et ne te détourne pas de qui veut emprunter de toi.
Ka ba wa duk wanda ya roƙe ka abu, kada kuma ka hana wa wanda yake neman bashi daga gare ka.
43 Vous avez entendu qu’il a été dit: « Tu aimeras ton prochain, et tu haïras ton ennemi ».
“Kun dai ji an faɗa, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka, ka kuma ƙi abokin gābanka.’
44 Mais moi, je vous dis: Aimez vos ennemis, [bénissez ceux qui vous maudissent, faites du bien à ceux qui vous haïssent], et priez pour ceux qui [vous font du tort et] vous persécutent,
Amma ina gaya muku, ku ƙaunaci abokan gābankukuma ku yi wa waɗanda suke tsananta muku addu’a,
45 en sorte que vous soyez les fils de votre Père qui est dans les cieux; car il fait lever son soleil sur les méchants et sur les bons, et envoie sa pluie sur les justes et sur les injustes.
don ku zama’ya’yan Ubanku na sama. Shi yakan sa ranarsa ta haskaka a kan mugaye da masu kirki; yakan kuma sako ruwan sama a bisa masu adalci da marasa adalci.
46 Car si vous aimez ceux qui vous aiment, quelle récompense avez-vous? Les publicains même n’en font-ils pas autant?
In masoyarku kawai kuke ƙauna, wace lada ce gare ku? Ko masu karɓar haraji ma ba haka suke yi ba?
47 Et si vous saluez vos frères seulement, que faites-vous de plus [que les autres]? Les nations même ne font-elles pas ainsi?
In kuwa kuna gai da’yan’uwanku ne kaɗai, me kuke yi fiye da waɗansu? Marasa bin Allah ma ba haka suke yi ba?
48 Vous, soyez donc parfaits, comme votre Père céleste est parfait.
Saboda haka sai ku zama cikakku, yadda Ubanku na sama yake cikakke.