< Marc 8 >

1 En ces jours-là, comme il y avait là une fort grande foule, et qu’ils n’avaient rien à manger, [Jésus], ayant appelé à lui ses disciples, leur dit:
A kwanakin nan, akwai wani gagaruman taron mutane, kuma basu da abincin ci. Yesu ya kirawo almajiransa yace masu,
2 Je suis ému de compassion envers la foule, car voici trois jours déjà qu’ils demeurent auprès de moi, et ils n’ont rien à manger;
“Ina tausayin taron mutanen nan domin kwana uku kenan suna nan tare da ni babu abinci.
3 et si je les renvoie à jeun dans leurs maisons, ils tomberont en défaillance par le chemin; car quelques-uns d’entre eux sont venus de loin.
Idan na salame su su koma gidajensu ba tare da sun ci abinci ba, za su galabaita a hanya domin gidajensu na da nisa.”
4 Et ses disciples lui répondirent: D’où pourra-t-on les rassasier de pain, ici, dans le désert?
Almajiransa suka amsa masa cewa, “A ina za mu iya samu gurasa a wannan jeji da zai ishi wadannan mutane haka?”
5 Et il leur demanda: Combien avez-vous de pains? Et ils dirent: Sept.
Ya tambaye su, “gurasa nawa kuke da su?” Sai suka ce, “Bakwai.”
6 Et il commanda à la foule de s’asseoir sur la terre. Et ayant pris les sept pains, il rendit grâces et les rompit et les donna à ses disciples pour les mettre devant la foule: et ils les mirent devant elle.
Ya umarci mutanen da su zauna. Ya dauki gurasar bakwai, bayan da ya yi godiya, ya kakarya gurasar, sa'annan ya umarci almajiransa da su raba wa mutanen. Su kuwa suka raba masu.
7 Ils avaient aussi quelques petits poissons; et ayant béni, il dit qu’ils les mettent aussi devant [la foule].
Suna kuma da kananan kifaye kadan. Bayan da ya yi godiya akan su, ya umurci almajiran su rabawa mutanen.
8 Et ils mangèrent et furent rassasiés; et ils ramassèrent, des morceaux qui étaient de reste, sept corbeilles.
Sun ci sun koshi. Suka tattara ragowar, har sun cika kwanduna bakwai.
9 Or ceux qui avaient mangé étaient environ 4 000. Et il les renvoya.
Akwai maza kimanin dubu hudu a wurin. Yesu ya sallame su.
10 Et aussitôt, montant dans un bateau avec ses disciples, il vint aux quartiers de Dalmanutha.
Nan take, ya shiga jirgin ruwa da almajiransa zuwa shiyyar Dalmanuta.
11 Et les pharisiens sortirent et se mirent à disputer avec lui, demandant de lui un signe du ciel, pour l’éprouver.
Sai Farisawa suka zo suka fara gardama da shi. Suna nema ya nuna masu alama daga sama, domin su gwada shi.
12 Et, soupirant en son esprit, il dit: Pourquoi cette génération demande-t-elle un signe? En vérité, je vous dis: il ne sera point donné de signe à cette génération.
Ya ja numfashi a ruhunsa yana cewa, “Don me wannan tsarar tana neman alama. Hakika ina gaya maku, babu wata alama da za a ba wannan tsarar.”
13 Et les laissant, il remonta de nouveau dans le bateau et s’en alla à l’autre rive.
Sai ya bar su ya sake shiga jirgin zuwa hayin tafkin.
14 Et ils avaient oublié de prendre des pains, et ils n’avaient qu’ un seul pain avec eux dans le bateau.
A lokacin nan, almajiransa sun manta su dauki gurasa. Domin gurasa daya ce tak a garesu cikin jirgin ruwan.
15 Et il leur enjoignit, disant: Voyez, gardez-vous du levain des pharisiens et du levain d’Hérode.
Ya gargade su, “ku yi hattara da yisti na Farisawa da Yisti na Hirudus.”
16 Et ils raisonnaient entre eux, [disant]: C’est parce que nous n’avons pas de pains.
Almajiran suka fara tattaunawa a tsakaninsu, “Saboda ba mu da gurasa ne.”
17 Et Jésus, le sachant, leur dit: Pourquoi raisonnez-vous sur ce que vous n’avez pas de pains? N’entendez-vous pas encore, et ne comprenez-vous pas? Avez-vous encore votre cœur endurci?
Yesu yana sane da wannan, sa'annan ya ce masu, “Don me kuke tattaunawa akan rashin gurasa? Har yanzu baku gane ba? Har yanzu ba ku da sane? Ko zuciyar ku ta duhunta ne?”
18 Ayant des yeux, ne voyez-vous pas? et ayant des oreilles, n’entendez-vous pas? et n’avez-vous point de mémoire?
Kuna da idanu, ba ku gani? Kuna da kunnuwa, ba ku ji? Ba ku tuna ba?
19 Quand je rompis les cinq pains aux 5 000, combien avez-vous recueilli de paniers pleins de morceaux? Ils lui disent: Douze.
Da na kakkarya gurasar a cikin mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka samu ragowa? Suka ce masa, “Goma sha biyu.”
20 Et quand [je rompis] les sept aux 4 000, combien avez-vous recueilli de corbeilles pleines de morceaux? Et ils dirent: Sept.
Kuma da na kakarya gurasa bakwai a cikin mutane dubu hudu, kwanduna nawa kuka dauka cike da ragowar? Suka ce masa, “bakwai.”
21 Et il leur dit: Comment ne comprenez-vous pas?
Ya ce masu, “har yanzu baku gane ba?”
22 Et il vient à Bethsaïda; et on lui amène un aveugle, et on le prie pour qu’il le touche.
Sun zo Baitsaida. Mutanen wurin suka kawo masa wani makaho, sai suka roke shi ya taba shi.
23 Et ayant pris la main de l’aveugle, il le mena hors de la bourgade; et lui ayant craché sur les yeux, il posa les mains sur lui et lui demanda s’il voyait quelque chose.
Yesu ya rike hanun makahon, ya jagorance shi zuwa bayan kauyen. Da ya tofa yawunsa a idon mutumin, kuma ya dora hanunsa akan mutumin, sai ya tambaye shi “kana ganin wani abu kuwa?”
24 Et ayant regardé, [l’homme] dit: Je vois des hommes, car je vois comme des arbres qui marchent.
Ya daga ido sai ya ce, “ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa.”
25 Puis Jésus lui mit encore les mains sur les yeux et le fit regarder; et il fut rétabli, et voyait tout clairement.
Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau.
26 Et il le renvoya dans sa maison, disant: N’entre pas dans la bourgade, et ne le dis à personne dans la bourgade.
Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, “kada ka shiga cikin garin”
27 Et Jésus s’en alla, et ses disciples, aux villages de Césarée de Philippe; et chemin faisant, il interrogea ses disciples, leur disant: Qui disent les hommes que je suis?
Yesu da almajiransa sun shiga kauyukan kaisariya ta Filibi. Da suke kan hanya, sai ya tambaye su, “Shin wanene mutane ke ce da ni?”
28 Et ils répondirent: Jean le baptiseur; et d’autres: Élie; et d’autres: L’un des prophètes.
Suka amsa masa suka ce, Yahaya mai Baftisma. Wasu suka ce, “Iliya”. wadansu kuma, 'Daya daga cikin anabawa”.
29 Et il leur demanda: Et vous, qui dites-vous que je suis? Et Pierre, répondant, lui dit: Tu es le Christ.
Ya tambaye su, “Amma me ku ke ce da ni?” Bitrus ya ce, “Kai ne Almasihu.”
30 Et il leur défendit expressément de dire cela de lui à personne.
Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa game da shi.
31 Et il commença à les enseigner: Il faut que le fils de l’homme souffre beaucoup, et qu’il soit rejeté des anciens et des principaux sacrificateurs et des scribes, et qu’il soit mis à mort, et qu’il ressuscite après trois jours.
Sai ya fara koya masu cewa, dole ne Dan Mutum ya sha wahala, dattawa da marubuta da manyan Firistoci zasu ki shi, a kuma kashe shi. Bayan kwana uku, zai tashi daga matattu.
32 Et il tenait ce discours ouvertement. Et Pierre, le prenant à part, se mit à le reprendre.
Ya fadi wannan afili. Sai Birus ya ja shi gefe ya fara tsauta masa.
33 Mais lui, se retournant et regardant ses disciples, reprit Pierre, disant: Va arrière de moi, Satan, car tes pensées ne sont pas aux choses de Dieu, mais à celles des hommes.
Amma Yesu ya juya ya dubi almajiransa sa'annan ya tsautawa Bitrus yana cewa, “Ka koma bayana Shaidan, domin kana kula da abubuwan mutane ne kawai, ba na Allah ba.”
34 Et ayant appelé la foule avec ses disciples, il leur dit: Quiconque veut venir après moi, qu’il se renonce soi-même, et qu’il prenne sa croix, et me suive:
Sai ya kira taron jama'ar da almajiransa a wuri daya, ya ce masu, “Duk wanda yake so ya bini, dole ne ya musunci kansa, ya dauki giciyensa ya biyo ni.
35 car quiconque voudra sauver sa vie la perdra; et quiconque perdra sa propre vie pour l’amour de moi et de l’évangile la sauvera.
Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi, amma duk wadda ya rasa ransa domina da kuma bishara zai cece shi.
36 Car que profitera-t-il à un homme s’il gagne le monde entier, et qu’il fasse la perte de son âme;
Me zai amfani mutum idan ya sami dukan duniya sannan ya rasa ransa.
37 ou que donnera un homme en échange de son âme?
Me mutum zai bayar amaimakon ransa?
38 Car quiconque aura honte de moi et de mes paroles parmi cette génération adultère et pécheresse, le fils de l’homme aura aussi honte de lui, quand il viendra dans la gloire de son Père, avec les saints anges.
Duk wanda ke jin kunyata ko maganata a wannan mazinaciyar tsara mai zunubi, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa a lokacin da ya dawo cikin daukakar Ubansa da Malaiku masu tsarki.”

< Marc 8 >