< Marc 14 >
1 Or, deux jours après, c’était la Pâque et les Pains sans levain. Et les principaux sacrificateurs et les scribes cherchaient comment ils pourraient se saisir de lui par ruse, et le faire mourir;
Idin Ketarewa da bukin gurasa mara yisti sauran kwana biyu kenan, sai shugabanin firistoci da malaman attaura suka nemi yadda zasu kama Yesu a asirce domin su kashe shi.
2 car ils disaient: Non pas pendant la fête, de peur qu’il n’y ait du tumulte parmi le peuple.
Suna cewa amma “Ba a lokacin idin ba, domin kada su haddasa hargitsi a tsakanin mutane”.
3 Et comme il était à Béthanie dans la maison de Simon le lépreux, et qu’il était à table, une femme vint, ayant un vase d’albâtre [plein] d’un parfum de nard pur et de grand prix; et, ayant brisé le vase, elle le répandit sur sa tête.
Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana shirin liyafa kenan sai ga wata mace dauke da kwalbar turare mai tamanin kwarai, ta shafa masa a kansa.
4 Et quelques-uns étaient [là], qui s’indignaient en eux-mêmes et disaient: À quoi bon la perte de ce parfum?
wasu dake tare da Yesu suka husata, suna kwalbarta da cewa
5 Car ce parfum aurait pu être vendu plus de 300 deniers, et être donné aux pauvres; et ils la reprenaient vivement.
“Ai wannan turare ne mai tsada, ina laifin a sayar a raba wa talakawa kudin? ina dalilin wannan almubazaranci?
6 Mais Jésus dit: Laissez-la; pourquoi lui donnez-vous du déplaisir? Elle a fait une bonne œuvre envers moi;
Sai Yesu yace masu “Ku kyaleta, don me kuke tsauta mata,
7 car vous avez toujours les pauvres avec vous, et quand vous voudrez, vous pourrez leur faire du bien; mais moi, vous ne m’avez pas toujours.
ai Idan kuna da niyyar taimakon talakawa ko matalauta, suna nan tare da ku ko a yaushe amma ni bazan kasance da ku kullum ba.
8 Ce qui était en son pouvoir, elle l’a fait; elle a anticipé [le moment] d’oindre mon corps pour ma sépulture.
Macen nan tayi aiki nagari domin shirya jikina ga jana'iza.
9 Et en vérité, je vous dis: en quelque lieu que cet évangile soit prêché dans le monde entier, on parlera aussi de ce que cette femme a fait, en mémoire d’elle.
hakika, Ina gaya maku, duk inda za'a yi bishara a duniya baza a mance da matan nan da hidimar da ta tayi mini ba.”
10 Et Judas Iscariote, l’un des douze, s’en alla vers les principaux sacrificateurs pour le leur livrer;
Da jin haka sai Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin manzannin ya ruga zuwa wurin baban firist domin ya bashe shi a garesu,
11 et ceux-ci, l’ayant entendu, s’en réjouirent et promirent de lui donner de l’argent; et il cherchait comment il le livrerait commodément.
Da mayan firistoci suka ji haka suka yi murna matuka tare da alkawarin kudi ga Yahuza, shi kuwa sai ya fara neman zarafin da zai mika Yesu a gare su.
12 Et le premier jour des pains sans levain, lorsqu’on sacrifiait la pâque, ses disciples lui disent: Où veux-tu que nous allions préparer [ce qu’il faut], afin que tu manges la pâque?
A ranar farko ta bukin gurasa marar yisti da kuma hadayar ragon Idin ketarewa, almajiransa suka ce masa “Ina zamu shirya liyafar domin idin ketarewa?
13 Et il envoie deux de ses disciples et leur dit: Allez à la ville; et un homme portant une cruche d’eau viendra à votre rencontre; suivez-le.
Ya aiki biyu daga cikin almajiransa da cewa “Ku shiga cikin birnin, zaku tarar da wani mutum dauke da tullun ruwa.
14 Et où qu’il entre, dites au maître de la maison: Le maître dit: Où est mon logis où je mangerai la pâque avec mes disciples?
Duk gidan da ya shiga ku bishi, sai ku cewa mai gidan, malam yace “ina bukatar masauki domin hidimar idin ketarewa tare da almajiraina?”'
15 Et lui vous montrera une grande chambre garnie, toute prête; apprêtez-nous là [ce qu’il faut].
Zai kuwa nuna maku babban bene gyararre. Sai ku yi mana shiri a can.”
16 Et ses disciples s’en allèrent et entrèrent dans la ville, et trouvèrent [tout] comme il leur avait dit; et ils apprêtèrent la pâque.
Da shigar almajiran cikin birnin, sai kome ya kasance yadda ya fada, su kuwa suka yi shirye shiryen idin ketarewar.
17 Et le soir étant venu, il vient avec les douze.
Da maraice ta yi, sai ya tare da sha biyun.
18 Et comme ils étaient à table et qu’ils mangeaient, Jésus dit: En vérité, je vous dis que l’un d’entre vous qui mange avec moi, me livrera.
Yayin da suke zazzaune a teburin suna cin abincin, sai Yesu ya ce “Hakika ina gaya maku wani da ke ci tare da ni a nan zai bashe ni”.
19 Et ils commencèrent à s’attrister et à lui dire l’un après l’autre: Est-ce moi? Et un autre: Est-ce moi?
Sai suka damu suka tambaye shi daya bayan daya suna cewa “Hakika bani bane ko?”
20 Mais répondant, il leur dit: C’est l’un d’entre les douze qui trempe avec moi au plat.
Yesu ya amsa masu da cewa “Daya daga cikin sha biyu ne, wanda ke sa hannu tare da ni yanzu cikin tasar”.
21 Le fils de l’homme s’en va, selon qu’il est écrit de lui; mais malheur à cet homme par qui le fils de l’homme est livré! Il aurait été bon pour cet homme-là qu’il ne soit pas né.
Dan Mutum zai tafi ne yadda nassi ya umarta game da shi amma kaiton wanda zai bashe shi! “zai, fiye masa, dama ba a haife shi ba”.
22 Et comme ils mangeaient, Jésus, ayant pris un pain [et] ayant béni, le rompit et le leur donna, et dit: Prenez; ceci est mon corps.
Lokacin da suke cin abincin, Yesu ya dauki gurasa ya sa albarka, ya gutsuttsura ta, sai ya basu yana cewa “Wannan jikinana ne”.
23 Et ayant pris la coupe [et] ayant rendu grâces, il la leur donna; et ils en burent tous.
Ya kuma dauki koko, yayi godiya, ya basu, su kuwa suka sha daga kokon.
24 Et il leur dit: Ceci est mon sang, le [sang] de la nouvelle alliance, qui est versé pour plusieurs.
Ya ce “Wannan jinina ne na alkawari da an zubar ga yawancin mutane”.
25 En vérité, je vous dis que je ne boirai plus du fruit de la vigne, jusqu’à ce jour où je le boirai nouveau dans le royaume de Dieu.
Hakika, bazan kara sha daga wannan ruwan inabi ba sai a ranar da zan sha sabo cikin mulkin Allah.”
26 Et ayant chanté une hymne, ils sortirent [et s’en allèrent] à la montagne des Oliviers.
Bayan sun raira wakar yabo ga Allah, sai suka tafi wurin dutsen zaitun.
27 Et Jésus leur dit: Vous serez tous scandalisés; car il est écrit: « Je frapperai le berger, et les brebis seront dispersées »;
Yesu ya ce masu dukkan ku zaku yi tuntube harma ku fadi saboda ni gama rubuce take cewa “Zan buge makiyayin, tumakin kuwa za su watse;
28 mais après que je serai ressuscité, j’irai devant vous en Galilée.
Amma bayan tashina, zai yi gaba in riga ku zuwa Galili.
29 Et Pierre lui dit: Si même tous étaient scandalisés, je ne le serai pourtant pas, moi.
Bitrus ya ce masa “ko dukkansu sun fadi, faufau banda ni”.
30 Et Jésus lui dit: En vérité, je te dis qu’aujourd’hui, cette nuit-ci, avant que le coq ait chanté deux fois, toi, tu me renieras trois fois.
Yesu yace masa “Hakika ina gaya maka, cikin wannan dare kafin carar zakara ta biyu zaka yi musun sani na sau uku”.
31 Mais [Pierre] disait encore plus fortement: Quand il me faudrait mourir avec toi, je ne te renierai point. Et ils dirent tous aussi la même chose.
Amma Bitrus ya sake cewa “Koda za'a kasheni tare da kai ba zan yi musun sanin ka ba”. Dukkan su kuwa suka yi wannan Alkawari.
32 Et ils viennent en un lieu dont le nom était Gethsémané. Et il dit à ses disciples: Asseyez-vous ici, jusqu’à ce que j’aie prié.
Suka isa wani wuri da ake kira Getsamani, sai Yesu ya ce wa almajiransa “Ku dakata anan domin zan je inyi addu'a”.
33 Et il prend avec lui Pierre et Jacques et Jean; et il commença à être saisi d’effroi et fort angoissé.
Sai ya dauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya. Ya fara jin wahala mutuka tare da damuwa kwarai.
34 Et il leur dit: Mon âme est saisie de tristesse jusqu’à la mort; demeurez ici et veillez.
Sai ya ce masu “Raina na shan wahala harma kamar in mutu. Ku dakata a nan, ku zauna a fadake”.
35 Et s’en allant un peu plus avant, il se jeta contre terre, et il priait que, s’il était possible, l’heure passe loin de lui.
Da Yesu yayi gaba kadan, sai ya fadi kasa yayi addu'a yana cewa idan mai yiwuwa ne “A dauke masa wannan sa'a daga gare shi.
36 Et il disait: Abba, Père, toutes choses te sont possibles; fais passer cette coupe loin de moi; toutefois non pas ce que je veux, moi, mais ce que tu veux, toi!
Ya ce “Ya Abba Uba, kome mai yuwane gare ka, ka dauke mini kokon wahalan nan, duk da haka ba nufina ba sai dai naka”.
37 Et il vient, et les trouve dormant; et il dit à Pierre: Simon, tu dors? Tu n’as pu veiller une heure?
Da komowarsa ya same su suna barci, sai ya ce wa Bitrus, Siman barci kake? Ashe, ba za ka iya zama a fadake ko da sa'a daya ba?
38 Veillez et priez, afin que vous n’entriez pas en tentation; l’esprit est prompt, mais la chair est faible.
Ku zauna a fadake, kuyi addu'a kada ku fada cikin jaraba. Lalle ruhu na da niyya amma jiki raunana ne.
39 Et il s’en alla de nouveau, et il pria, disant les mêmes paroles.
Sai ya sake komawa, yayi addu'a, yana maimaita kalmominsa na farko.
40 Et s’en étant retourné, il les trouva de nouveau dormant (car leurs yeux étaient appesantis); et ils ne savaient que lui répondre.
Har wa yau kuma ya sake dawowa, ya same su suna barci don barci ya cika masu idanu kwarai, sun kuwa kasa ce masa kome.
41 Et il vient pour la troisième fois et leur dit: Dormez dorénavant et reposez-vous; il suffit, l’heure est venue; voici, le fils de l’homme est livré entre les mains des pécheurs.
Ya sake komowa karo na uku yace masu “har yanzu barci kuke yi kuna hutawa? Ya isa haka! Lokaci yayi, an bada Dan Mutum ga masu zunubi”.
42 Levez-vous, allons; voici, celui qui me livre s’est approché.
Ku tashi mutafi kun ga, ga mai bashe ni nan ya kusato.”
43 Et aussitôt, comme il parlait encore, Judas, l’un des douze, se trouve là, et avec lui une grande foule avec des épées et des bâtons, de la part des principaux sacrificateurs et des scribes et des anciens.
Nan da nan, kafin ya rufe baki sai ga Yahuza, daya daga cikin sha biyun da taron jama'a rike da takkuba da kulake. Manyan firistoci da malaman attaura da shugabanni suka turo su.
44 Et celui qui le livrait leur avait donné un signe, disant: Celui que j’embrasserai, c’est lui; saisissez-le, et emmenez-le sûrement.
Mai bashe shi din nan ya riga ya kulla da su cewa “Wanda zan yi wa sumba shine mutumin, ku kama shi ku tafi da shi a tsare.
45 Et quand il fut venu, aussitôt s’approchant de lui, il dit: Rabbi, Rabbi! et il l’embrassa avec empressement.
Da isowarsa kuwa, sai ya zo wurin Yesu ya ce “Ya malam!”. Sai ya sumbace shi.
46 Et ils mirent les mains sur lui et se saisirent de lui.
Su kuwa suka kama shi, suka tafi da shi.
47 Et l’un de ceux qui étaient là présents, ayant tiré l’épée, frappa l’esclave du souverain sacrificateur, et lui emporta l’oreille.
Amma daya daga cikin na tsaye ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya yanke masa kunne.
48 Et Jésus, répondant, leur dit: Êtes-vous sortis comme après un brigand, avec des épées et des bâtons, pour me prendre?
Sai Yesu ya ce “kun fito kamar masu kama yan fashi da takkuba da kulake, domin ku kama ni?
49 J’étais tous les jours avec vous, enseignant dans le temple, et vous ne vous êtes pas saisis de moi; mais c’est afin que les écritures soient accomplies.
Lokacin da nake koyarwa a Haikali, kowace rana da ku, baku kama ni ba. Amma anyi haka ne domin a cika abinda Nassi ya fada.”
50 Et tous le laissèrent et s’enfuirent.
Daga nan duk wadanda suke tare da Yesu suka yashe shi, suka tsere.
51 Et un certain jeune homme le suivit, enveloppé d’une toile de fin lin sur le corps nu; et ils le saisissent;
Wani saurayi, daga shi sai mayafi ya bi shi, suka kai masa cafka.
52 et, abandonnant la toile de fin lin, il leur échappa tout nu.
Shi kuwa ya bar masu mayafin ya gudu tsirara.
53 Et ils amenèrent Jésus au souverain sacrificateur; et tous les principaux sacrificateurs et les anciens et les scribes s’assemblent auprès de lui.
Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. a can suka tara dattawa duk da manyan firistoci da shugabanni da marubuta, suka taru a wurinsa.
54 Et Pierre le suivit de loin, jusque dans l’intérieur du palais du souverain sacrificateur, et il s’assit avec les huissiers, et se chauffait près du feu.
Bitrus kuwa ya bi shi daga nesa har cikin gidan babban firist. Ya zauna tare da dogaran Haikalin, yana jin dumin wuta.
55 Or les principaux sacrificateurs et tout le sanhédrin cherchaient [quelque] témoignage contre Jésus, pour le faire mourir; et ils n’en trouvaient point.
Sai, manyan firistoci da duk 'yan majalisa Yahudawa suka nemi shaidar da za a tabbatar a kan Yesu, don su samu su kashe shi. Amma basu samu ba.
56 Car plusieurs portaient de faux témoignages contre lui; et les témoignages ne s’accordaient pas.
Da yawa kuma suka yi masa shaidar Zur (Karya), amma bakin su bai zama daya ba.
57 Et quelques-uns s’élevèrent et portèrent un faux témoignage contre lui, disant:
Sai wadansu kuma suka taso suka yi masa shaidar zur (karya) suka ce.
58 Nous l’avons entendu disant: Moi, je détruirai ce temple qui est fait de main, et en trois jours j’en bâtirai un autre qui ne sera pas fait de main.
“Mun ji ya ce, wai zai rushe haikalin nan da mutane suka gina, ya sake gina wani cikin kwana uku, ba kuwa ginin mutum ba”.
59 Et ainsi non plus leur témoignage ne s’accordait pas.
Duk da haka, sai shaidar tasu bata zo daya ba.
60 Et le souverain sacrificateur, se levant devant tous, interrogea Jésus, disant: Ne réponds-tu rien? De quoi ceux-ci témoignent-ils contre toi?
Sai babban firist ya mike a tsakanin su, ya tambayi Yesu yace “Ba ka da wata amsa game da shaidar da mutanen nan suke yi a kanka?
61 Et il garda le silence, et ne répondit rien. Le souverain sacrificateur l’interrogea encore, et lui dit: Toi, tu es le Christ, le Fils du Béni?
Amma yayi shiru abinsa, bai ce kome ba. Sai babban firist din ya sake tambayarsa “To, ashe kai ne Allmasihu Dan Madaukaki?
62 Et Jésus dit: Je le suis; et vous verrez le fils de l’homme assis à la droite de la puissance, et venant avec les nuées du ciel.
Yesu ya ce “Nine. Za ku kuwa ga Dan Mutum zaune dama ga mai iko, yana kuma zuwa cikin gajimare”.
63 Et le souverain sacrificateur, ayant déchiré ses vêtements, dit: Qu’avons-nous encore besoin de témoins?
Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa yace “Wacce shaida kuma zamu nema?
64 Vous avez entendu le blasphème: que vous en semble? Et tous le condamnèrent comme méritant la mort.
Kun dai ji sabon da yayi! Me kuka gani? Duk suka yanke masa hukunci akan ya cancanci kisa.
65 Et quelques-uns se mirent à cracher contre lui, et à lui couvrir le visage, et à lui donner des soufflets, et à lui dire: Prophétise. Et les huissiers le frappaient de leurs mains.
Wadansu ma suka fara tottofa masa yau, suka daure masa idanu, suka bubbuge shi suna cewa “Yi annabci” Dogaran kuma suka yi ta marinsa.
66 Et comme Pierre était en bas, dans la cour, une des servantes du souverain sacrificateur vient,
Bitrus kuwa na kasa a filin gida, sai wata baranyar babban firist ta zo.
67 et, apercevant Pierre qui se chauffait, elle le regarda et dit: Et toi, tu étais avec le Nazarénien Jésus.
Da ta ga Bitrus na jin dumi, ta yi masa kallon gaske ta ce “Kaima ai tare kake da banazaren nan Yesu”.
68 Et il le nia, disant: Je ne sais ni n’entends ce que tu dis. Et il sortit dehors dans le vestibule; et le coq chanta.
Amma ya musa ya ce “Ni ban ma san abinda kike fada ba balle in fahimta”. Sai ya fito zaure. Sai zakara yayi cara.
69 Et la servante, l’apercevant encore, se mit à dire à ceux qui étaient là: Celui-ci est de ces gens-là.
Sai baranyar ta ganshi, ta sake ce wa wadanda ke tsaitsaye a wurin, “Wannan ma daya daga cikinsu ne”.
70 Et il le nia de nouveau. Et encore un peu après, ceux qui étaient là présents dirent à Pierre: Certainement tu es de ces gens-là; car aussi tu es Galiléen.
Amma ya sake musawa, jim kadan sai na tsaitsayen suka ce wa Bitrus “Lalle kai ma dayansu ne don ba Galile ne kai”.
71 Et il se mit à faire des imprécations et à jurer: Je ne connais pas cet homme dont vous parlez.
Sai ya fara la'anta kansa yana ta rantsuwa yana ce wa “Ban ma san mutumin nan da kuke fada ba”.
72 Et le coq chanta pour la seconde fois. Et Pierre se ressouvint de la parole que Jésus lui avait dite: Avant que le coq chante deux fois, tu me renieras trois fois. Et en y pensant, il pleura.
Nan da nan sai zakara ya yi cara ta biyu, Bitrus kuwa ya tuna da maganar Yesu a gare shi cewa “Kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi musun sani na sau uku”. Da ya tuno haka, sai ya fashe da kuka.