< Luc 17 >

1 Or il dit à ses disciples: Il est impossible qu’il n’arrive pas des scandales; mais malheur à celui par qui ils arrivent!
Sai Yesu ya ce wa almajiransa, 'Babu shakka akwai sanadodin tuntube da za su sa mu yin zunubi amma kaiton wanda shine sanadin su!
2 Mieux lui vaudrait qu’on lui mette au cou une meule d’âne, et qu’il soit jeté dans la mer, que de scandaliser un de ces petits.
Zai gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi a cikin teku fiye da wanda zai zama sanadiyar tuntube ga wadannan kananan.
3 Prenez garde à vous-mêmes. Si ton frère pèche, reprends-le, et s’il se repent, pardonne-lui;
Ku kula da kanku. Idan dan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa, in kuwa ya tuba ka yafe masa.
4 et si sept fois le jour il pèche contre toi, et que sept fois il retourne à toi, disant: Je me repens, tu lui pardonneras.
Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!”
5 Et les apôtres dirent au Seigneur: Augmente-nous la foi.
Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.'
6 Et le Seigneur dit: Si vous avez de la foi comme un grain de moutarde, vous diriez à ce mûrier: Déracine-toi, et plante-toi dans la mer; et il vous obéirait.
Ubangiji kuwa ya ce, “In kuna da bangaskiya kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan durumin, 'Ka tuge, ka kuma dasu a cikin teku,' zai yi biyayya da ku.
7 Mais qui est celui d’entre vous, qui, ayant un esclave labourant ou paissant [le bétail], quand il revient des champs, dise: Avance-toi de suite et mets-toi à table?
Amma wanene a cikinku, idan yana da bawa mai yin masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce masa, 'Maza zo ka zauna ka ci abinci'?
8 Ne lui dira-t-il pas au contraire: Apprête-moi à souper et ceins-toi, et me sers jusqu’à ce que j’aie mangé et bu; et après cela, tu mangeras et tu boiras, toi?
Ba zai ce masa, 'Ka shirya mani wani abu domin in ci ka kuma yi damara, ka yi mini hidima har in gama ci da sha. Bayan haka sai ka ci ka sha'?
9 Est-il obligé à l’esclave de ce qu’il a fait ce qui avait été commandé? Je ne le pense pas.
Ba zai yi wa bawan nan godiya ba domin ya yi biyayya da abubuwan da aka umarce shi ya yi, ko zai yi haka?
10 Ainsi, vous aussi, quand vous aurez fait toutes les choses qui vous ont été commandées, dites: Nous sommes des esclaves inutiles; ce que nous étions obligés de faire, nous l’avons fait.
Haka kuma, idan kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, 'Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibi ne kurum.'”
11 Et il arriva qu’en allant à Jérusalem, il traversait la Samarie et la Galilée.
Wata rana yana tafiya zuwa Urushalima, sai ya bi iyakar kasar Samariya da Galili.
12 Et comme il entrait dans un village, dix hommes lépreux le rencontrèrent; et ils s’arrêtèrent de loin;
Yayin da yana shiga wani kauye kenan, sai wadansu kutare maza guda goma suka tarye shi suna tsaye daga nesa da shi
13 et ils élevèrent la voix, disant: Jésus, maître, aie pitié de nous!
sai suka daga murya suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka yi mana jinkai.”
14 Et les voyant, il leur dit: Allez, montrez-vous aux sacrificateurs. Et il arriva qu’en s’en allant ils furent rendus nets.
Da ya gan su, ya ce masu, “Ku je ku nuna kanku a wurin firistoci.” Ya zama sa'adda suke tafiya, sai suka tsarkaka.
15 Or l’un d’entre eux, voyant qu’il était guéri, revint sur ses pas, glorifiant Dieu à haute voix;
Daya daga cikinsu da ya ga an warkar da shi, ya koma, yana ta daukaka Allah da murya mai karfi.
16 et il se jeta sur sa face aux pieds de Jésus, lui rendant grâces. Et c’était un Samaritain.
Ya fadi a gaban Yesu, yana masa godiya. Shi kuwa Basamariye ne.
17 Et Jésus, répondant, dit: Les dix n’ont-ils pas été rendus nets? Et les neuf, où sont-ils?
Yesu ya amsa ya ce, “Ba goma ne aka tsarkake ba? Ina sauran taran?
18 Il ne s’en est point trouvé qui soient revenus pour donner gloire à Dieu, si ce n’est cet étranger.
Babu wani da ya dawo ya girmama Allah sai wannan bakon kadai?”
19 Et il lui dit: Lève-toi, et t’en va; ta foi t’a guéri.
Sai ya ce masa, “Tashi, kayi tafiyarka. Bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 Or, étant interrogé par les pharisiens quand viendrait le royaume de Dieu, il leur répondit et dit: Le royaume de Dieu ne vient pas de manière à attirer l’attention;
Da Farisawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai bayyana, Yesu ya amsa masu ya ce, “Mulkin Allah ba lura ake yi da shi ba.
21 et on ne dira pas: Voici, il est ici; ou, voilà, il est là. Car voici, le royaume de Dieu est au milieu de vous.
Ba kuwa za a ce, 'Gashi nan!' Ko kuwa, 'Ga shi can ba!' domin mulkin Allah yana tsaknaninku.”
22 Et il dit aux disciples: Les jours viendront où vous désirerez de voir l’un des jours du fils de l’homme, et vous ne le verrez pas.
Yesu ya ce wa almajiran, “Kwanaki na zuwa da za ku yi begen ganin rana daya cikin ranakun Dan Mutum, amma ba zaku gani ba.
23 Et on vous dira: Voici, il est ici; ou, voilà, il est là. N’y allez pas, et ne les suivez pas.
Za su ce maku, 'Duba can! 'Duba nan!' Amma kada ku je kuna dubawa, ko kuwa ku bi su.
24 Car comme l’éclair qui brille, luit de l’un des côtés de dessous le ciel jusqu’à l’autre côté de dessous le ciel, ainsi sera le fils de l’homme en son jour.
Kamar yadda walkiya take haskakawa daga wannan bangaren sararin sama zuwa wancan bangaren, haka ma dan mutum zai zama a ranar bayyanuwarsa.
25 Mais auparavant il faut qu’il souffre beaucoup, et qu’il soit rejeté par cette génération.
Amma lalle sai ya sha wahaloli dabam dabam tukuna, mutanen zamanin nan kuma su ki shi.
26 Et comme il arriva aux jours de Noé, ainsi en sera-t-il aux jours du fils de l’homme aussi:
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka kuma zai faru a lokacin bayyanar Dan Mutum.
27 on mangeait, on buvait, on se mariait, on donnait en mariage, jusqu’au jour où Noé entra dans l’arche; et le déluge vint, et les fit tous périr.
Ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har zuwa ga ranar da Nuhu ya shiga jirgi - ruwan tufana kuma ya zo, ya hallaka su duka.
28 De même aussi, comme il arriva aux jours de Lot: on mangeait, on buvait, on achetait, on vendait, on plantait, on bâtissait;
Haka ma aka yi a zamanin Lutu, ana ci, ana sha, ana saye, ana sayarwa, ana shuke-shuke da gine-gine.
29 mais, au jour où Lot sortit de Sodome, il plut du feu et du soufre du ciel, qui les fit tous périr;
Amma a ranar da Lutu, ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da kibiritu daga sama, aka hallaka su duka.
30 il en sera de même au jour où le fils de l’homme sera manifesté.
Haka kuma zai zama a ranar bayyanuwar Dan Mutum.
31 En ce jour-là, que celui qui sera sur le toit et qui aura ses effets dans la maison, ne descende pas pour les emporter; et pareillement que celui qui sera aux champs ne retourne pas en arrière.
A ranar nan fa, wanda yake kan soro kada ya sauka domin daukan kayansa daga cikin gida. Haka kuma wanda yake gona kada ya dawo.
32 Souvenez-vous de la femme de Lot.
Ku tuna fa da matar Lutu.
33 Quiconque cherchera à sauver sa vie, la perdra; et quiconque la perdra, la gagnera.
Duk mai son ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai same shi.
34 Je vous dis qu’en cette nuit-là deux seront sur un même lit, l’un sera pris et l’autre laissé;
Ina gaya maku, a wannan dare za a sami mutum biyu a gado daya. Za a dauka daya, a kuma bar dayan.
35 deux femmes moudront ensemble, l’une sera prise et l’autre laissée;
Za a sami mata biyu suna nika tare. Za a dauka daya a bar daya.”
36 [deux seront aux champs, l’un sera pris et l’autre laissé].
[“Za a ga mutum biyu a gona. Za a dauki daya a bar daya.”]
37 Et répondant, ils lui disent: Où, Seigneur? Et il leur dit: Là où est le corps, là aussi s’assembleront les aigles.
Sai suka tambaye shi, “Ina, Ubangiji?” Sai ya ce masu, “Duk in da gangar jiki yake, a nan ungulai sukan taru.”

< Luc 17 >