< Juges 20 >

1 Et tous les fils d’Israël sortirent, depuis Dan jusqu’à Beër-Shéba, et le pays de Galaad; et l’assemblée se réunit comme un seul homme, vers l’Éternel, à Mitspa.
Sa’an nan dukan Isra’ilawa daga Dan zuwa Beyersheba kuma daga ƙasar Gileyad mutane kamar mutum guda suka fito suka taru a gaban Ubangiji a Mizfa.
2 Et les principaux de tout le peuple, toutes les tribus d’Israël, se présentèrent dans la congrégation du peuple de Dieu, 400 000 hommes de pied, tirant l’épée.
Shugabanni dukan kabilan mutane na kabilan Isra’ila suka zazzauna a wurarensu a taron jama’ar Allah, mayaƙa dubu ɗari huɗu masu ɗamara da takuba.
3 Et les fils de Benjamin apprirent que les fils d’Israël étaient montés à Mitspa. Et les fils d’Israël dirent: Dites comment ce mal est arrivé.
(Mutanen Benyamin suka ji cewa Isra’ilawa sun haura zuwa Mizfa.) Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Gaya mana yadda wannan mugun abu ya faru.”
4 Et le Lévite, le mari de la femme tuée, répondit et dit: J’étais venu à Guibha, qui est à Benjamin, moi et ma concubine, pour passer la nuit;
Sai Balawen, mijin matar da aka kashe ya ce, “Ni da ƙwarƙwarata mun zo Gibeya a Benyamin don mu kwana.
5 et les hommes de Guibha se levèrent contre moi, et entourèrent de nuit la maison, à cause de moi; ils avaient l’intention de me tuer, et ils ont humilié ma concubine, et elle est morte.
Da dad dare mutanen Gibeya suka bi ni suka kewaye gidan da niyya su kashe ni. Suka yi wa ƙwarƙwarata fyaɗe, har ta mutu.
6 Et j’ai saisi ma concubine et je l’ai coupée en morceaux, et je l’ai envoyée dans toutes les campagnes de l’héritage d’Israël; car ils ont commis une énormité et une infamie en Israël.
Na ɗauki ƙwarƙwarata na yayyanka gunduwa-gunduwa na aika da shi ga kowane yankin gādon Isra’ila, domin sun aikata mugu abu da abin kunya a Isra’ila.
7 Voici, vous tous, fils d’Israël, délibérez, et donnez ici [votre] avis.
To, dukanku Isra’ilawa, sai ku yi magana ku kuma yanke hukuncinku.”
8 Et tout le peuple se leva comme un seul homme, disant: Aucun de nous n’ira à sa tente, et aucun de nous ne se retirera dans sa maison;
Dukan mutane suka tashi kamar mutum ɗaya, suna cewa “Ba waninmu da zai tafi gida. Sam, babu ko ɗayanmu da zai koma gidansa.
9 et maintenant, voici ce que nous ferons à Guibha: nous la traiterons selon ce que le sort décidera;
Amma yanzu ga abin da za mu yi wa Gibeya. Za mu haura mu fāɗa yadda ƙuri’a ta nunar.
10 et nous prendrons 10 hommes sur 100, de toutes les tribus d’Israël, et 100 sur 1 000, et 1 000 sur 10 000, qui prendront des provisions pour le peuple, afin que, à leur arrivée, on traite Guibha de Benjamin selon toute l’infamie qu’elle a commise en Israël.
Za mu ɗauko mutum goma a kowane mutum ɗari daga dukan kabilan Isra’ila, da ɗari a dubu, da kuma dubu a dubu goma, domin a tanada wa mayaƙan. Sa’an nan, sa’ad da mayaƙan suka iso Geba a Benyamin, za su yi da su daidai bisa ga muguntar da suka yi a Isra’ila.”
11 Et tous les hommes d’Israël se rassemblèrent contre la ville, unis comme un seul homme.
Saboda haka dukan mutane Isra’ilawa suka taru suka kuma haɗu kamar mutum guda don su fāɗa wa birnin da yaƙi.
12 Et les tribus d’Israël envoyèrent des hommes dans toutes les familles de Benjamin, disant: Quel est ce mal qui est arrivé au milieu de vous?
Kabilan Isra’ila suka aika jakadu a ko’ina a cikin kabilar Benyamin cewa, “Wace irin mugunta ce wannan da kuka aikata?
13 Et maintenant, livrez-nous ces hommes, fils de Bélial, qui sont à Guibha, afin que nous les fassions mourir et que nous ôtions le mal du milieu d’Israël. Mais [les fils de] Benjamin ne voulurent pas écouter la voix de leurs frères, les fils d’Israël;
Yanzu fa sai ku fitar da waɗannan’yan iskan da suka aikata wannan abu na Gibeya don mu kashe su mu kawar da mugunta daga Isra’ila!” Amma mutanen Benyamin ba su saurari’yan’uwansu Isra’ilawa ba.
14 et les fils de Benjamin se rassemblèrent de leurs villes à Guibha, pour sortir en guerre contre les fils d’Israël.
Daga biranensu suka tattaru a Gibeya don su yaƙi Isra’ilawa.
15 Et en ce jour-là furent dénombrés les fils de Benjamin qui vinrent de leurs villes: 26 000 hommes tirant l’épée, sans les habitants de Guibha, qui furent dénombrés: 700 hommes d’élite.
Nan da nan mutanen Benyamin suka tattara mayaƙa dubu ashirin da shida masu takuba daga biranensu, ban da mayaƙa ɗari bakwai da aka zaɓa daga mazauna a Gibeya.
16 De tout ce peuple, il y avait 700 hommes d’élite qui étaient gauchers; tous ceux-là lançaient avec la fronde une pierre contre un cheveu, et ne manquaient pas.
Cikin dukan mayaƙan nan akwai zaɓaɓɓu mutane ɗari bakwai waɗanda su bahagwai ne, kowanne yana iya harbin gashin guda na kai da majajjawa ba kuskure.
17 Et les hommes d’Israël furent dénombrés, sauf Benjamin: 400 000 hommes tirant l’épée, tous gens de guerre.
Isra’ila kuwa, ban da Benyamin, sun tara mayaƙa masu takobi dubu ɗari huɗu, dukansu gwanayen yaƙi ne.
18 Et les fils d’Israël se levèrent, et montèrent à Béthel, et interrogèrent Dieu, et dirent: Qui de nous montera le premier pour livrer bataille aux fils de Benjamin? Et l’Éternel dit: Juda, le premier.
Sai Isra’ilawa suka haura zuwa Betel suka nemi nufin Allah, suka ce, “Wane ne a cikinmu zai fara fāɗa wa mutanen Benyamin?” Ubangiji ya ce, “Yahuda ce za tă fara.”
19 Et les fils d’Israël se levèrent le matin, et campèrent contre Guibha.
Kashegari sai Isra’ilawa suka tashi suka kafa sansani kusa da Gibeya.
20 Et les hommes d’Israël sortirent en guerre contre Benjamin, et les hommes d’Israël se rangèrent en bataille contre eux devant Guibha.
Mutanen Isra’ila suka fita yaƙi da mutane Benyamin suka kuma ja dāgār yaƙi a Gibeya.
21 Et les fils de Benjamin sortirent de Guibha; et en ce jour-là ils étendirent morts par terre 22 000 hommes de ceux d’Israël.
Mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya suka kashe mutum dubu ashirin da biyu na Isra’ilawa a dāgār yaƙi a ranar.
22 Et le peuple, les hommes d’Israël, se fortifièrent, et se rangèrent de nouveau en bataille dans le lieu où ils s’étaient rangés le premier jour.
Amma mutanen Isra’ila suka ƙarfafa juna, suka sāke koma inda suka ja dāgā a rana ta farko.
23 Et les fils d’Israël montèrent, et ils pleurèrent devant l’Éternel jusqu’au soir, et ils interrogèrent l’Éternel, disant: M’approcherai-je de nouveau pour livrer bataille aux fils de Benjamin, mon frère? Et l’Éternel dit: Montez contre lui.
Isra’ilawa suka haura suka yi kuka a gaban Ubangiji, har yamma, suka nemi nufin Ubangiji. Suka ce, “Mu sāke koma yaƙi da mutanen Benyamin,’yan’uwanmu?” Ubangiji ya ce, “Ku haura ku fāɗa musu.”
24 Et les fils d’Israël s’avancèrent contre les fils de Benjamin, le second jour;
Sai Isra’ilawa suka matsa kusa da Benyamin a rana ta biyu.
25 et Benjamin sortit contre eux de Guibha, le second jour; et de nouveau ils étendirent morts par terre 18 000 hommes des fils d’Israël, tous tirant l’épée.
A wannan lokaci, da mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya don su yaƙe su, sai suka sāke kashe Isra’ilawa dubu goma sha takwas, dukansu ɗauke da takuba.
26 Et tous les fils d’Israël et tout le peuple montèrent et vinrent à Béthel, et pleurèrent et demeurèrent là devant l’Éternel, et jeûnèrent ce jour-là jusqu’au soir; et ils offrirent des holocaustes et des sacrifices de prospérités devant l’Éternel.
Sa’an nan Isra’ilawa, dukan mutane, suka haura zuwa Betel, a can suka zauna suna kuka a gaban Ubangiji. Suka yi azumi a wannan rana har yamma suka miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama ga Ubangiji.
27 Et les fils d’Israël interrogèrent l’Éternel (et l’arche de l’alliance de Dieu était là, en ces jours;
Isra’ilawa suka nemi nufin Ubangiji (A kwanakin nan akwatin alkawarin Allah yana can,
28 et Phinées, fils d’Éléazar, fils d’Aaron, se tenait devant elle, en ces jours), et ils dirent: Sortirai-je encore de nouveau pour livrer bataille aux fils de Benjamin, mon frère, ou cesserai-je? Et l’Éternel dit: Montez; car demain je les livrerai en ta main.
Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, kuwa yana hidima a gabansa.) Suka ce, “Mu sāke haura mu yi yaƙi da mutanen Benyamin’yan’uwanmu, ko a’a?” Ubangiji ya ce, “Ku je, gama gobe zan ba da su a hannuwanku.”
29 Et Israël plaça des embuscades contre Guibha, tout autour.
Sa’an nan Isra’ila ta yi kwanto kewaya da Gibeya.
30 Et les fils d’Israël montèrent, le troisième jour, contre les fils de Benjamin; et ils se rangèrent contre Guibha, comme les autres fois.
Suka haura su kara da mutanen Benyamin a rana ta uku suka ja dāgā a Gibeya kamar dā.
31 Et les fils de Benjamin sortirent à la rencontre du peuple; ils furent attirés loin de la ville, et commencèrent à frapper quelques-uns du peuple, qui furent tués comme les autres fois, environ 30 hommes d’Israël, sur les routes, dont l’une monte à Béthel, et l’autre à Guibha, par la campagne.
Mutanen Benyamin suka fito su same su aka kuma jawo su nesa da birnin. Suka fara karkashe Isra’ilawa kamar dā, har aka kashe wajen mutum talatin a filaye da kuma a hanyoyi, wadda take zuwa Betel da kuma wadda take zuwa Gibeya.
32 Et les fils de Benjamin dirent: Ils sont battus devant nous comme la première fois. Et les fils d’Israël dirent: Fuyons, et nous les attirerons loin de la ville, sur les routes.
Yayinda mutanen Benyamin suna cewa, “Muna cin nasara a kansu kamar dā,” Isra’ilawa kuwa suna cewa, “Mu yi ta jan da baya mu janye su daga birni zuwa kan hanyoyi.”
33 Et tous les hommes d’Israël se levèrent de leur lieu, et se rangèrent à Baal-Thamar; et l’embuscade d’Israël s’élança de son lieu, de la prairie de Guibha.
Dukan mutanen Isra’ila suka taso daga wurarensu suka ja dāgā a Ba’al-Tamar, Isra’ilawan da suka yi kwanto a yammancin Geba kuwa suka fito.
34 Et 10 000 hommes d’élite de tout Israël vinrent contre Guibha, et la bataille fut rude; et ceux [de Benjamin] ne savaient pas que le mal les atteignait.
Sa’an nan jarumai Isra’ila dubu goma suka yi gaba suka kai wa Gibeya hari. Yaƙi kuwa ya yi zafi har mutane Benyamin ba su san masifa tana dab da su ba.
35 Et l’Éternel battit Benjamin devant Israël, et les fils d’Israël étendirent morts en ce jour-là 25 100 hommes de Benjamin, tous tirant l’épée.
Ubangiji kuwa ya fatattake mutanen Benyamin a gaban Isra’ila; a ranar kuwa Isra’ilawa sun kashe mutum 25,100 na mutanen Benyamin, dukansu ɗauke da takuba.
36 Et les fils de Benjamin virent qu’ils étaient battus. – Or les hommes d’Israël firent place à ceux de Benjamin, car ils se confiaient en l’embuscade qu’ils avaient placée contre Guibha.
Sa’an nan Benyamin suka ga an ci su. To, mutanen Isra’ila sun yi ta ja da baya daga mutanen Benyamin domin suna dogara ga waɗanda sa su yi kwanto kusa da Gibeya ne.
37 Et l’embuscade se hâta, et se jeta sur Guibha; et l’embuscade se porta en avant, et frappa toute la ville par le tranchant de l’épée.
Mutanen da suke kwanto suka yi wuf suka ruga cikin Gibeya, suka bazu suka kuma karkashe dukan waɗanda suke a birnin.
38 Et le signal convenu entre les hommes d’Israël et l’embuscade était qu’ils fassent monter de la ville une épaisse colonne de fumée.
Mutanen Isra’ila sun riga sun shirya da’yan kwanton cewa su murtuke hayaƙi daga birnin,
39 Et les hommes d’Israël avaient tourné visage dans la bataille, et Benjamin avait commencé de frapper à mort une trentaine d’hommes parmi les hommes d’Israël, car ils disaient: Certainement il est complètement battu devant nous comme dans la première bataille.
a sa’an nan ne mutanen Isra’ila za su juya su fāɗa wa mutane Benyamin da yaƙi. Mutanen Benyamin sun fara karkashe mutum talatin na Isra’ila, sai suka ce, “Muna cin nasara a kansu kamar dā.”
40 Et quand l’incendie commença à monter de la ville comme une colonne de fumée, Benjamin se tourna en arrière, et voici, toute la ville montait [en fumée] vers les cieux.
Amma da alamar hayaƙi ya fara murtukewa daga birnin, sai mutanen Benyamin suka juya suka ga hayaƙi yana murtukewa ko’ina a cikin birnin zuwa sararin sama.
41 Et les hommes d’Israël tournèrent visage: et les hommes de Benjamin furent épouvantés; car ils virent que le mal les avait atteints.
Sa’an nan mutanen Isra’ila suka juyo musu, mutanen Benyamin kuwa suka tsorata domin sun gane masifa ta zo musu.
42 Et ils tournèrent le dos devant les hommes d’Israël, vers le chemin du désert, et la bataille les serra de près. Et ceux qui sortirent des villes les détruisirent au milieu d’eux.
Saboda haka suka tsere a gaban Isra’ila zuwa wajen hamada, amma ba su iya tsere wa yaƙin ba. Mutanen Isra’ila da suka fito daga cikin birnin suka karkashe su a can.
43 Ils environnèrent Benjamin, le poursuivirent, le foulèrent aux pieds là où il voulait se reposer, jusque vis-à-vis de Guibha, vers le soleil levant.
Suka kewaye mutanen Benyamin, suka kore su, suka fatattake su a wajajen Gibeya a gabashi.
44 Et il tomba de Benjamin 18 000 hommes, tous hommes vaillants.
Mutum dubu goma sha takwas na mutanen Benyamin suka mutu dukansu kuwa jarumai ne.
45 Et ils tournèrent le dos, et s’enfuirent au désert, vers le rocher de Rimmon; et [les Israélites] en grappillèrent sur les routes 5 000 hommes, et ils les serrèrent de près en les poursuivant jusqu’à Guidhom, et en frappèrent 2 000 hommes.
Da suka juya suka juya suka tsere zuwa wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, Isra’ilawa suka kashe mutum dubu biyar a kan hanyoyi. Suka yi ta matsa wa mutanen Benyamin har zuwa Gidom suka kashe mutum dubu biyu kuma.
46 Et tous ceux de Benjamin qui tombèrent en ce jour-là, furent 25 000 hommes tirant l’épée, tous hommes vaillants.
A ranar kuwa mutanen Benyamin dubu ashirin da biyar ne aka kashe, dukansu jarumai.
47 Et 600 hommes tournèrent le dos et s’enfuirent au désert, vers le rocher de Rimmon, et ils demeurèrent au rocher de Rimmon quatre mois.
Amma mutane ɗari shida suka juya suka tsere wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, inda suka zauna wata huɗu.
48 Et les hommes d’Israël retournèrent vers les fils de Benjamin et les frappèrent par le tranchant de l’épée, et les hommes de chaque ville, et les bêtes, et tout ce qui fut trouvé; même toutes les villes qu’ils rencontrèrent, ils les livrèrent au feu.
Mutanen Isra’ila suka koma wurin mutanen Benyamin suka kashe dukan waɗanda suke a birnin, tare da dabbobi da kome da suka samu. Dukan garuruwan da suka samu sun ƙone su ƙaf.

< Juges 20 >