< Juges 19 >
1 Et il arriva en ces jours-là, quand il n’y avait point de roi en Israël, qu’un Lévite qui séjournait au fond de la montagne d’Éphraïm, prit une concubine de Bethléhem de Juda.
A kwanakin nan Isra’ila ba su da sarki. To, wani Balawe wanda yake zama a wani lungu na ƙasar tudu ta Efraim ya ɗauko wa kansa ƙwarƙwara daga Betlehem cikin Yahuda.
2 Et sa concubine lui étant infidèle se prostitua, et s’en alla d’avec lui à la maison de son père, à Bethléhem de Juda; et elle fut là quelque temps, quatre mois.
Amma ba tă yi aminci ba. Ta bar shi ta komo gidan mahaifiyarta a Betlehem, a Yahuda. Bayan ta zauna a can wajen wata huɗu,
3 Et son mari se leva, et alla après elle pour parler à son cœur, afin de la ramener, et il avait avec lui son jeune homme et une paire d’ânes. Et elle le fit entrer dans la maison de son père; et quand le père de la jeune femme le vit, il se réjouit de le rencontrer.
sai mijinta ya je wajenta biko don yă rarashe ta komo. Ya tafi tare bawansa da kuma jakuna biyu. Sai ta shigar da shi gidan mahaifinta, sa’ad da mahaifinta ya gan shi, ya marabce shi da murna.
4 Et son beau-père, le père de la jeune femme, le retint; et il demeura avec lui trois jours; et ils mangèrent et burent, et ils passèrent la nuit là.
Surukinsa, mahaifin yarinyar, ya sha kansa, yă dakata; saboda haka ya dakata tare da shi har kwana uku, yana ci yana sha, yana kuma kwanciya a can.
5 Et il arriva, le quatrième jour, qu’ils se levèrent de bonne heure le matin; et, comme il se levait pour s’en aller, le père de la jeune femme dit à son gendre: Fortifie ton cœur avec une bouchée de pain, et après, vous vous en irez.
A rana ta huɗu suka tashi da sassafe ya kuma yi shiri yă tafi, amma mahaifinta yarinyar ya ce wa surukinsa, “Ka ɗan ci wani abu don ka sami ƙarfi; sa’an nan ka tafi.”
6 Et ils s’assirent, et mangèrent et burent, eux deux ensemble; et le père de la jeune femme dit à l’homme: Consens, je te prie, et passe [ici] la nuit, et que ton cœur se réjouisse.
Saboda haka suka zauna su biyu suka ci suka sha tare. Bayan haka sai mahaifin yarinyar ya ce, “Don Allah ka kwana ka ji wa kanka daɗi.”
7 Et l’homme se leva pour s’en aller, mais son beau-père le pressa, et il revint et passa [encore] la nuit là.
Sa’ad da mutumin ya tashi zai tafi, sai surukinsa ya roƙe shi, saboda haka ya kwana a wannan dare.
8 Et le cinquième jour, il se leva de bonne heure le matin pour s’en aller; mais le père de la jeune femme dit: Je te prie, fortifie ton cœur. Et ils s’attardèrent jusqu’à ce que le jour baissa, et ils mangèrent eux deux.
Da sassafen kashegari rana ta biyar, ya tashi zai tafi, sai mahaifin yarinyar ya ce, “Ka ɗan zauna ka shaƙata sai rana ta yi sanyi mana!” Saboda haka su biyu suka zauna suka ci abinci tare.
9 Et l’homme se leva pour s’en aller, lui et sa concubine, et son serviteur. Et son beau-père, le père de la jeune femme, lui dit: Tu vois que le jour faiblit, le soir approche; je vous prie, passez la nuit; voici, le jour tombe, passe ici la nuit, et que ton cœur se réjouisse; et demain vous vous lèverez de bonne heure pour [aller] votre chemin, et tu t’en iras à ta tente.
Sa’ad da mutumin da ƙwarƙwaransa da bawansa, suka tashi don su tafi, surukinsa, mahaifin yarinyar ya ce, “Duba, rana ta kusan fāɗuwa, yamma ta riga ta yi, ka kwana a nan. Ka sāke kwana ka ji wa ranka daɗi. Kashegari da sassafe za ka iya tashi ka kama hanyarka zuwa gida.”
10 Mais l’homme ne voulut point passer la nuit, et il se leva, et s’en alla; et il vint jusque vis-à-vis de Jébus qui est Jérusalem, et, avec lui, la paire d’ânes bâtés, et sa concubine avec lui.
Amma bai so ya sāke kwana a can ba, mutumin ya tashi ya tafi ya bi ta Yebus (wato, Urushalima), tare da jakunansa biyu da aka yi musu shimfiɗa da kuma ƙwarƙwaransa.
11 Ils étaient tout près de Jébus, et le jour avait beaucoup baissé; et le serviteur dit à son maître: Allons, je te prie, et détournons-nous vers cette ville des Jébusiens, et passons-y la nuit.
Sa’ad da suka yi kusa da Yebus dare kuma ya riga ya yi, bawan ya ce wa maigidansa, “Mu dakata a birnin nan na Yebusiyawa mu kwana.”
12 Et son maître lui dit: Nous ne nous détournerons point vers une ville des étrangers, qui n’est pas des fils d’Israël; mais nous passerons jusqu’à Guibha.
Maigidansa ya ce, “A’a. Ba za mu shiga birnin baƙi waɗanda mutanensu ba Isra’ilawa ba. Za mu ci gaba zuwa Gibeya.”
13 Et il dit à son serviteur: Viens, et approchons-nous d’un de ces endroits, et passons la nuit à Guibha ou à Rama.
Ya kuma ce, “Zo, mu yi ƙoƙari mu kai Gibeya ko Rama mu kwana a ɗaya cikinsu.”
14 Et ils passèrent plus avant, et marchèrent, et le soleil se coucha, comme ils étaient près de Guibha, qui est à Benjamin.
Saboda haka suka ci gaba, rana tana fāɗuwa sa’ad da suka yi kusa da Gibeya a Benyamin.
15 Et ils se détournèrent pour entrer [et] pour passer la nuit à Guibha. Et il entra, et s’assit sur la place de la ville, et il n’y eut personne qui les reçoive dans sa maison pour passer la nuit.
A can suka dakata don su kwana, suka tafi suka zauna a dandali birnin, amma wani ya shigar da su gidansa da daren.
16 Et voici, sur le soir, un vieillard venait des champs, de son travail; et l’homme était de la montagne d’Éphraïm, et séjournait à Guibha; et les hommes du lieu étaient Benjaminites.
A wannan yamma sai ga wani tsoho daga ƙasar tudu ta Efraim, wanda yake zama a Gibeya (mutane wurin kuwa mutanen Benyamin ne), ya shigo daga wurin aiki a gonaki.
17 Et il leva ses yeux, et vit le voyageur sur la place de la ville; et le vieillard [lui] dit: Où vas-tu, et d’où viens-tu?
Sa’ad da ya duba ya ga matafiyin a dandalin birnin, sai tsohon ya yi tambaya ya ce, “Ina za ku? Ina kuka fito?”
18 Et il lui dit: Nous passons de Bethléhem de Juda vers le fond de la montagne d’Éphraïm; je suis de là, et je suis allé à Bethléhem de Juda, et j’ai à faire avec la maison de l’Éternel; et il n’y a personne qui me reçoive dans sa maison.
Balawen ya ce, “Muna fito daga Betlehem a Yahuda za mu wani lungu a ƙasar tudu ta Efraim inda nake da zama. Na tafi Betlehem a Yahuda, ga shi kuwa yanzu za ni gidan Ubangiji. Ba wanda ya shigar da ni gidansa.
19 Et pourtant j’ai de la paille et du fourrage pour nos ânes, et j’ai aussi du pain et du vin pour moi et pour ta servante, et pour le jeune homme qui est avec tes serviteurs; rien ne nous manque.
Muna da ƙara da abinci don jakunanmu, muna kuma da burodi da ruwan inabi dominmu da bayinka, ni, baiwarka da kuma saurayin nan tare da mu. Ba ma bukatar kome.”
20 Et le vieillard lui dit: Paix te soit! Seulement, que tous tes besoins soient à ma charge; mais ne passe pas la nuit sur la place.
Tsohon ya ce, “Na marabce ku a gidana. Bari ni ba ku duk abin da kuke bukata. Kada ku dai kwana a dandali.”
21 Et il le fit entrer dans sa maison, et donna le fourrage aux ânes; et ils lavèrent leurs pieds, et mangèrent et burent.
Saboda haka sai kai shi zuwa gidansa ya ciyar da jakunansa. Bayan sun wanke ƙafafunsu, sai aka ba su abinci da abin sha.
22 Comme ils faisaient bonne chère, voici, les hommes de la ville, des hommes, fils de Bélial, entourèrent la maison, frappant à la porte; et ils parlèrent au vieillard, maître de la maison, disant: Fais sortir l’homme qui est entré dans ta maison, afin que nous le connaissions.
Yayinda suke jin wa kansu daɗi, sai waɗansu’yan iska daga birnin suka kewaye gidan. Suna bubbuga ƙofar, suna kira tsohon da yake da gidan suna cewa, “Ka fito mana da mutumin nan a gidanka domin mu yi jima’i da shi.”
23 Et le maître de la maison sortit vers eux, et leur dit: Non, mes frères, ne faites pas [ce] mal, je vous prie; après que cet homme est entré dans ma maison, ne faites pas cette infamie.
Maigidan ya fita waje ya ce musu, “A’a, abokaina, kada ku yi abin kunyan nan. Da yake mutumin nan baƙona ne, kada ku yi rashin kunyan nan.
24 Voici ma fille qui est vierge, et sa concubine: laissez-moi les faire sortir, et vous les humilierez, et vous leur ferez ce qu’il vous plaira; mais à cet homme ne faites pas cette chose infâme.
Duba, ga’yata da ba tă taɓa sanin namiji ba da kuma ƙwarƙwaransa. Zan fito muku da su a waje yanzu, za ku kuwa iya yin ko mene ne da kuke so da su. Amma wannan mutum, kada ku yi abin kunya.”
25 Mais ces gens ne voulurent pas l’écouter; et l’homme saisit sa concubine et la leur amena dehors; et ils la connurent et abusèrent d’elle toute la nuit jusqu’au matin; et ils la renvoyèrent comme l’aurore se levait.
Amma mutanen ba su saurare shi ba. Saboda haka mutumin ya ba da ƙwarƙwaransa, suka yi mata fyaɗe suka yi lalata da ita dukan dare, gari yana wayewa sai suka bar ta.
26 Et comme le matin arrivait, la femme vint et tomba à l’entrée de la maison de l’homme chez qui était son seigneur, [et y resta] jusqu’au jour.
Da safe matar ta koma gidan da maigidanta yake, ta fāɗi a ƙofa ta kwanta a can har rana ta yi.
27 Et son seigneur se leva le matin, et ouvrit la porte de la maison, et sortit pour aller son chemin; et voici, la femme, sa concubine, était tombée à l’entrée de la maison, ses mains sur le seuil.
Sa’ad da maigidanta ya tashi da safe ya buɗe ƙofar gidan don yă fita ya ci gaba da tafiyarsa, sai ga ƙwarƙwararsa, ta fāɗi a bakin ƙofar gidan da hannuwanta a madogarar ƙofar.
28 Et il lui dit: Lève-toi, et allons-nous-en. Mais personne ne répondit. Et l’homme la prit sur son âne, et se leva et s’en alla en son lieu.
Ya ce mata, “Tashi; mu tafi.” Amma ba amsa. Sai ya sa ta a kan jakinsa ya kama hanyar gida.
29 Et il entra dans sa maison, et prit le couteau, et saisit sa concubine, et la partagea selon ses os en douze morceaux, et l’envoya dans tous les confins d’Israël.
Da ya kai gida, sai ya ɗauki wuƙa ya yayyanka ƙwarƙwaransa gunduwa-gunduwa, kashi goma sha biyu ya aika da su a ko’ina a Isra’ila.
30 Et il arriva que tous ceux qui virent cela, dirent: Jamais chose pareille n’a eu lieu ni ne s’est vue, depuis le jour où les fils d’Israël sont montés du pays d’Égypte jusqu’à ce jour. Pensez à cela, prenez conseil, et parlez.
Duk wanda ya gani, sai ya ce, “Ba a taɓa gani ko yin irin wannan abu ba, tun lokacin da Isra’ilawa suka fito daga Masar. Ku yi tunani wannan! Ku kuma yi la’akari! Ku gaya mana abin da za mu yi!”