< Josué 17 >

1 Et le lot échut à la tribu de Manassé (or il était le premier-né de Joseph), à Makir, premier-né de Manassé, père de Galaad; comme il était un homme de guerre, Galaad et Basan furent à lui.
Wannan shi ne gādon da aka ba wa kabilar Manasse, a matsayin ɗan farin Yusuf. Manasse yana da ɗan farin mai suna Makir. Makir shi ne mahaifin mutanen Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan gama Makiriyawa jarumai ne ƙwarai.
2 Et [le lot] échut aux autres fils de Manassé, selon leurs familles, aux fils d’Abiézer, et aux fils de Hélek, et aux fils d’Asriel, et aux fils de Sichem, et aux fils de Hépher, et aux fils de Shemida. Ce sont là les fils de Manassé, fils de Joseph, les mâles, selon leurs familles.
Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manasse rabon gādonsu bisa ga iyalansu, wato, Abiyezer, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer da Shemida. Waɗannan su ne’ya’yan Manasse, maza, ɗan Yusuf bisa ga iyalansu.
3 Et Tselophkhad, fils de Hépher, fils de Galaad, fils de Makir, fils de Manassé, n’eut point de fils, mais seulement des filles; et ce sont ici les noms de ses filles: Makhla, et Noa, Hogla, Milca, et Thirtsa;
Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse ba shi da’ya’ya maza, sai dai mata. Ga sunayensu, Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.
4 et elles se présentèrent devant Éléazar, le sacrificateur, et devant Josué, fils de Nun, et devant les princes, disant: L’Éternel a commandé à Moïse de nous donner un héritage au milieu de nos frères. Et [Josué] leur donna, selon le commandement de l’Éternel, un héritage au milieu des frères de leur père.
Suka je wurin Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin, suka ce musu, “Ubangiji ya umarci Musa cewa yă ba mu gādonmu tare da’yan’uwanmu maza.” Saboda haka Yoshuwa ya ba su gādo tare da’yan’uwan mahaifinsu maza bisa ga umarnin Ubangiji.
5 Et il échut dix parts à Manassé, outre le pays de Galaad et de Basan, qui est au-delà du Jourdain;
Dalilin ke nan Manasse ya sami kashi goma ban da ƙasar Gileyad da Bashan a gabashin Urdun,
6 car les filles de Manassé reçurent un héritage au milieu de ses fils; et le pays de Galaad fut pour les autres fils de Manassé.
domin’ya’ya mata na kabilar Manasse sun sami gādo tare da’ya’ya maza. Aka ba wa sauran mutanen kabilar Manasse ƙasar Gileyad.
7 Et le territoire de Manassé allait d’Aser à Micmethath, qui est devant Sichem; et la frontière allait à droite vers les habitants d’En-Tappuakh.
Iyakar ƙasar Manasse ta tashi daga Asher zuwa Mikmetat a gabashin Shekem. Iyakar kuma ta miƙe har zuwa kudu wadda ta ƙunshi mutanen da suke zaune a En Taffuwa.
8 La campagne de Tappuakh était à Manassé; mais Tappuakh, sur la frontière de Manassé, était aux fils d’Éphraïm.
(Manasse ne yake da ƙasar Taffuwa, amma garin Taffuwa kansa, a kan iyakar Manasse ta mutanen Efraim ce.)
9 Et la frontière descendait au torrent de Kana, au midi du torrent. Ces villes-là étaient à Éphraïm, au milieu des villes de Manassé. Et le territoire de Manassé était au nord du torrent, et aboutissait à la mer.
Sa’an nan iyakar ta ci gaba ta yi kudu zuwa Rafin Kana. Akwai garuruwan da suke kudancin rafin, waɗanda suke Efraim, ko da yake suna cikin yankin Manasse. Iyakar Manasse ta miƙe zuwa arewa ta bi gefen rafin ta kuma ƙarasa a Bahar Rum.
10 Le midi était à Éphraïm, et le nord à Manassé, et la mer était sa frontière; et au nord, ils touchaient à Aser, et à l’orient, à Issacar.
Ƙasar a wajen kudu ta Efraim ce, ta wajen arewa kuma ta Manasse ce. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Asher yana wajen arewa, Issakar kuma a wajen gabas.
11 Et Manassé avait, dans Issacar et dans Aser, Beth-Shean et les villages de son ressort, et Jibleam et les villages de son ressort, et les habitants de Dor et les villages de son ressort, et les habitants d’En-Dor et les villages de son ressort, et les habitants de Thaanac et les villages de son ressort, et les habitants de Meguiddo et les villages de son ressort: les trois districts montueux.
A yanki tsakanin Issakar da Asher, Manasse yana da waɗannan wurare, Bet-Sheyan, Ibileyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan En Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta’anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta (Na uku cikin jerin shi ne Nafot).
12 Mais les fils de Manassé ne purent pas déposséder [les habitants de] ces villes-là, et le Cananéen voulut habiter dans ce pays.
Duk da haka mutanen Manasse ba su iya mallakar garuruwan nan ba, domin Kan’aniyawa sun nace da zama a wannan yanki.
13 Et il arriva que, quand les fils d’Israël furent devenus forts, ils rendirent le Cananéen tributaire; mais ils ne le dépossédèrent pas entièrement.
Da Isra’ilawa suka yi ƙarfi, sai suka sa Kan’aniyawa suka zama masu yin musu aiki, amma ba su iya korarsu duka ba.
14 Et les fils de Joseph parlèrent à Josué, disant: Pourquoi m’as-tu donné en héritage un seul lot et une seule part, à moi qui suis un peuple nombreux, selon que l’Éternel m’a béni jusqu’à présent?
Mutanen Yusuf kuwa suka ce wa Yoshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo ɗaya kawai? Ga shi muna da yawa kuma Ubangiji ya albarkace mu sosai.”
15 Et Josué leur dit: Si tu es un peuple nombreux, monte à la forêt, et coupe-la pour t’y [faire de la place] dans le pays des Phéréziens et des Rephaïm, si la montagne d’Éphraïm est trop étroite pour toi.
Yoshuwa ya ce musu, “In kuna da yawa sosai, in kuma ƙasar kan tudu ta Efraim ba ta ishe ku ba, sai ku je cikin jeji, ku nema wa kanku ƙasa a ƙasar Ferizziyawa da Refahiyawa.”
16 Et les fils de Joseph dirent: Nous ne pouvons pas acquérir la montagne, et il y a des chars de fer chez tous les Cananéens qui habitent le pays de la vallée, chez ceux de Beth-Shean et des villages de son ressort, et chez ceux de la vallée de Jizreël.
Mutanen Yusuf suka amsa suka ce, “Ƙasar kan tudu ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan’aniyawan da suke zama a filin, da waɗanda suke Bet-Sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke Kwarin Yezireyel, duk suna da keken yaƙin ƙarfe.”
17 Et Josué parla à la maison de Joseph, à Éphraïm et à Manassé, disant: Tu es un peuple nombreux, et tu as une grande puissance; tu n’auras pas un seul lot,
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Yusuf, wa Efraim da Manasse, “Kuna da yawa, kuna kuma da ƙarfi sosai. Ba wuri ɗaya kaɗai za ku samu gādo ba,
18 mais la montagne sera à toi; comme c’est une forêt, tu la couperas, et elle sera à toi jusqu’à ses extrémités; car tu déposséderas le Cananéen, quoiqu’il ait des chars de fer [et] qu’il soit fort.
amma har da ƙasar kan tudu ma, ko da yake jeji ne, ku je ku gyara shi, duk yă zama naku. Ko da yake Kan’aniyawa suna da kekunan yaƙi na ƙarfe, suna kuma da ƙarfi, duk da haka za ku kore su.”

< Josué 17 >