< Josué 12 >
1 Et ce sont ici les rois du pays, que les fils d’Israël frappèrent et dont ils possédèrent le pays, de l’autre côté du Jourdain, vers le soleil levant, depuis le torrent de l’Arnon jusqu’à la montagne de l’Hermon, et toute la plaine au levant:
Waɗannan su ne sarakunan ƙasashen da Isra’ilawa suka ci da yaƙi, suka kuma mallaki ƙasarsu a gabashin Urdun, daga kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon haɗe da dukan gefen gabas na Araba.
2 Sihon, roi des Amoréens, qui habitait à Hesbon, dominant depuis Aroër qui est sur le bord du torrent de l’Arnon et depuis le milieu du torrent, sur la moitié de Galaad, jusqu’au Jabbok, torrent qui est la frontière des fils d’Ammon;
Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Ya yi mulki daga Arower wadda take iyakar kwarin Arnon, daga tsakiyar kwarin har zuwa, Kogin Yabbok, wanda yake iyakar Ammonawa. Wannan ya haɗa da rabin Gileyad.
3 et [sur] la plaine, jusqu’à la mer de Kinnéreth, vers le levant, et jusqu’à la mer de la plaine, la mer Salée, au levant, du côté de Beth-Jeshimoth, et au midi, sous les pentes du Pisga;
Ya kuma yi mulki a kan gabashin Araba daga tekun Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri), zuwa Bet-Yeshimot da kuma kudu zuwa gangaren dutsen Fisga.
4 et le territoire d’Og, roi de Basan, du reste des Rephaïm, qui habitait à Ashtaroth et à Édréhi;
Haka ma suka ci sashen Og sarkin Bashan, ɗaya daga cikin Refahiyawa na ƙarshe da ya yi mulki a Ashtarot da Edireyi.
5 et il dominait sur la montagne de l’Hermon, et sur Salca, et sur tout Basan, jusqu’à la frontière des Gueshuriens et des Maacathiens, et [sur] la moitié de Galaad, [jusqu’à la] frontière de Sihon, roi de Hesbon.
Mulkinsa ya taso daga Dutsen Hermon, da Saleka, da dukan Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa haɗe da rabin Gileyad, zuwa kan iyakar Heshbon ta sarki Sihon.
6 Moïse, serviteur de l’Éternel, et les fils d’Israël, les frappèrent; et Moïse, serviteur de l’Éternel, en donna la possession aux Rubénites, et aux Gadites, et à la demi-tribu de Manassé.
Sai Musa, bawan Ubangiji da Isra’ilawa suka ci Sihon da Og da yaƙi. Musa bawan Ubangiji kuwa ya ba da ƙasarsu ga mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse.
7 Et ce sont ici les rois du pays, que Josué et les fils d’Israël frappèrent en deçà du Jourdain, vers l’occident, depuis Baal-Gad, dans la vallée du Liban, jusqu’à la montagne de Halak qui s’élève vers Séhir; et Josué en donna la possession aux tribus d’Israël, selon leurs distributions,
Waɗannan su ne sarakuna da kuma ƙasashen da Yoshuwa da Isra’ilawa suka ci da yaƙi a yammancin Urdun, daga Ba’al-Gad a Kwarin Lebanon zuwa Dutsen Halak wanda ya miƙe zuwa Seyir. Yoshuwa ya raba ƙasarsu ta zama gādo ga Isra’ilawa bisa ga yadda aka raba su kabila-kabila.
8 dans la montagne, et dans le pays plat, et dans la plaine, et sur les pentes des montagnes, et dans le désert, et dans le midi: le Héthien, l’Amoréen, et le Cananéen, le Phérézien, le Hévien, et le Jébusien: –
Ƙasar ta haɗa da ƙasar kan tudu, filayen arewanci, Araba, gangaren Dutse, da jejin, da kuma Negeb, wato, ƙasashen Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa, da Yebusiyawa.
9 le roi de Jéricho, un; le roi d’Aï, qui est à côté de Béthel, un;
Sarkin Yeriko, ɗaya sarkin Ai (kusa da Betel), ɗaya
10 le roi de Jérusalem, un; le roi de Hébron, un;
sarkin Urushalima, ɗaya sarkin Hebron, ɗaya
11 le roi de Jarmuth, un; le roi de Lakis, un;
sarkin Yarmut, ɗaya sarkin Lakish, ɗaya
12 le roi d’Églon, un; le roi de Guézer, un;
sarkin Eglon, ɗaya sarkin Gezer, ɗaya
13 le roi de Debir, un; le roi de Guéder, un;
sarkin Debir, ɗaya sarkin Bet-Gader, ɗaya
14 le roi de Horma, un; le roi d’Arad, un;
sarkin Horma, ɗaya sarkin Arad, ɗaya
15 le roi de Libna, un; le roi d’Adullam, un;
sarkin Libna, ɗaya sarkin Adullam, ɗaya
16 le roi de Makkéda, un; le roi de Béthel, un;
sarkin Makkeda, ɗaya sarkin Betel, ɗaya
17 le roi de Tappuakh, un; le roi de Hépher, un;
sarkin Taffuwa, ɗaya sarkin Hefer, ɗaya
18 le roi d’Aphek, un; le roi de Lassaron, un;
sarkin Afek, ɗaya sarkin Sharon, ɗaya
19 le roi de Madon, un; le roi de Hatsor, un;
sarkin Madon, ɗaya sarkin Hazor, ɗaya
20 le roi de Shimron-Meron, un; le roi d’Acshaph, un;
sarkin Shimron Meron, ɗaya sarkin Akshaf, ɗaya
21 le roi de Thaanac, un; le roi de Meguiddo, un;
sarkin Ta’anak, ɗaya sarkin Megiddo, ɗaya
22 le roi de Kédesh, un; le roi de Jokneam, au Carmel, un;
sarkin Kedesh, ɗaya sarkin Yokneyam a Karmel, ɗaya
23 le roi de Dor, des hauteurs de Dor, un; le roi de Goïm, à Guilgal, un;
sarkin Dor (A Nafot Dor), ɗaya sarkin Goyim a Gilgal, ɗaya
24 le roi de Thirtsa, un; tous les rois étaient 31.
sarki Tirza, ɗaya. Duka-duka dai sarakuna talatin da ɗaya ne.