< Jonas 3 >

1 Et la parole de l’Éternel [vint] à Jonas une seconde fois, disant:
Sa’an nan sai maganar Ubangiji ta zo wa Yunana sau na biyu.
2 Lève-toi, va à Ninive, la grande ville, et crie-lui selon le cri que je te dirai.
“Tafi babban birnin nan Ninebe, ka yi masa shelar saƙon da na ba ka.”
3 Et Jonas se leva et s’en alla à Ninive, selon la parole de l’Éternel. Or Ninive était une fort grande ville, de trois journées de chemin.
Sai Yunana ya yi biyayya da maganar Ubangiji, ya tafi Ninebe. Ninebe birni ne da yake da muhimmanci, wanda sai an ɗauki kwana uku kafin a iya zaga shi.
4 Et Jonas commença à entrer dans la ville, le chemin d’un jour; et il cria et dit: Encore 40 jours, et Ninive sera renversée.
A rana ta fari, Yunana ya kama tafiya yana ratsa birnin. Sai ya yi shela cewa, “Nan da kwana arba’in za a hallaka Ninebe?”
5 Et les hommes de Ninive crurent Dieu, et proclamèrent un jeûne, et se vêtirent de sacs, depuis les plus grands d’entre eux jusqu’aux plus petits.
Mutanen Ninebe kuwa suka gaskata Allah. Aka yi shela a yi azumi, sai dukansu daga babba har zuwa ƙaraminsu, suka sa tufafin makoki.
6 Car la parole parvint au roi de Ninive, et il se leva de son trône, et ôta de dessus lui son manteau, et se couvrit d’un sac et s’assit sur la cendre.
Da saƙon Yunana ya kai kunnen sarkin Ninebe, sai ya tashi daga kujerar mulkinsa, ya tuɓe alkyabbarsa, ya sa rigar makoki, ya zauna cikin toka.
7 Et il fit crier et dire dans Ninive, par un édit du roi et de ses grands, disant: Que les hommes, et les bêtes, le gros et le menu bétail, ne goûtent de rien; qu’ils ne paissent pas et ne boivent pas d’eau;
Sai ya yi umarni a Ninebe cewa, “Bisa ga umarnin sarki da fadawansa. “Kada a bar wani mutum ko dabba, garke ko shannu, su ɗanɗana wani abu; kada a bari su ci ko su sha.
8 et que les hommes et les bêtes soient recouverts de sacs. Et qu’ils crient à Dieu avec force; et qu’ils reviennent, chacun, de leur mauvaise voie et de la violence qui est en leurs mains.
Bari kowane mutum da dabba yă yafa rigunan makoki. Kowa yă roƙi Allah da gaske, kowa kuma yă bar mugayen ayyukan da yake yi.
9 Qui sait? Dieu reviendra et se repentira, et reviendra de l’ardeur de sa colère, et nous ne périrons pas.
Wa ya sani? Ko Allah zai ji tausayinmu da kuma juyayinmu yă janye zafin fushinsa don kada mu hallaka.”
10 Et Dieu vit leurs œuvres, qu’ils revenaient de leur mauvaise voie; et Dieu se repentit du mal qu’il avait parlé de leur faire, et il ne le fit pas.
Da Allah ya ga abin da suka yi, da kuma yadda suka juya daga mugayen hanyoyinsu sai ya ji tausayinsu, bai kawo hallaka a kansu yadda ya yi shirin yi ba.

< Jonas 3 >