< Jean 9 >
1 Et comme il passait, il vit un homme aveugle dès sa naissance.
Da Yesu yana wucewa, sai ya ga wani mutum makaho tun daga haihuwa.
2 Et ses disciples l’interrogèrent, disant: Rabbi, qui a péché: celui-ci, ou ses parents, pour qu’il soit né aveugle?
Sai almajiransa suka tambaye shi, “Mallam, wa yayi zunubi, mutumin ne ko iyayensa, har aka haife shi makaho?”
3 Jésus répondit: Ni celui-ci n’a péché, ni ses parents; mais c’est afin que les œuvres de Dieu soient manifestées en lui.
Yesu ya amsa, Ba mutumin ne ko iyayensa suka yi zunubi ba, amma domin aikin Allah ya bayyana a cikinsa.
4 Il me faut faire les œuvres de celui qui m’a envoyé, tandis qu’il est jour; la nuit vient, en laquelle personne ne peut travailler.
Dole mu yi aikin wanda ya aiko ni tunda rana. Dare na zuwa inda ba mai iya yin aiki.
5 Pendant que je suis dans le monde, je suis la lumière du monde.
Yayinda ina duniya, ni ne hasken duniya.”
6 Ayant dit ces choses, il cracha en terre et fit de la boue de son crachat, et mit la boue comme un onguent sur ses yeux,
Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, ya tofa yawu a kasa, ya kwaba kasar da yawunsa, sai ya shafe idanun mutumin da kasar.
7 et lui dit: Va, et lave-toi au réservoir de Siloé (ce qui est interprété Envoyé). Il s’en alla donc, et se lava, et revint voyant.
Ya ce masa, tafi, ka wanke a tafkin Siloam (ma'anarsa: aike).” Sai mutumin ya tafi, ya wanke, ya dawo yana gani.
8 Les voisins donc, et ceux qui, l’ayant vu auparavant, [savaient] qu’il était mendiant, dirent: N’est-ce pas celui qui était assis et qui mendiait?
Sai makwabtansa da mutanen da da suka gan shi tun can yana roko suka ce, “Ba wannan mutum ne wanda ya ke zaune yana roko ba?”
9 Quelques-uns disaient: C’est lui. D’autres disaient: Non, mais il lui ressemble. Lui dit: C’est moi-même.
Wadansu suka ce, “shi ne.” Wadansu suka ce, “A'a, amma yana kama da shi.” Amma shi ya ce, “Ni ne wannan mutum.”
10 Ils lui dirent donc: Comment ont été ouverts tes yeux?
Suka ce masa, “To yaya aka bude maka idanu?”
11 Il répondit et dit: Un homme, appelé Jésus, fit de la boue et oignit mes yeux, et me dit: Va à Siloé et lave-toi. Et je m’en suis allé, et je me suis lavé, et j’ai vu.
Sai ya amsa, “Mutumin da ake ce da shi Yesu shi ya kwaba kasa ya shafa mani a idanuna ya ce mani, 'je ka kogin Siluwam ka wanke.' Sai naje na wanke, sannan na samu gani.”
12 Ils lui dirent donc: Où est cet [homme]? Il dit: Je ne sais.
Suka ce masa, “Ina yake?” Ya amsa, “Ban sani ba.”
13 Ils amenèrent aux pharisiens celui qui auparavant avait été aveugle.
Suka kawo mutumnin da yake makaho a da wurin farisawa.
14 Or c’était un jour de sabbat que Jésus fit la boue, et qu’il ouvrit ses yeux.
A ranar asabar ne kwa Yesu ya kwaba kasa ya bude masa idanu.
15 Les pharisiens donc aussi lui demandèrent encore comment il avait recouvré la vue. Et il leur dit: Il a mis de la boue sur mes yeux, et je me suis lavé, et je vois.
Har yanzu farisawan suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Ya ce masu, “Ya sa mani kasa a idanuna, na wanke, kuma yanzu ina gani.”
16 Quelques-uns donc d’entre les pharisiens dirent: Cet homme n’est pas de Dieu, car il ne garde pas le sabbat. D’autres disaient: Comment un homme pécheur peut-il faire de tels miracles? Et il y avait de la division entre eux.
Wadansu daga cikin farisawa suka ce, “Wannan mutum ba daga Allah yake ba domin ba ya kiyaye ranar Asabar. “Wadansu suka ce, “Yaya mai zunubi zai yi irin wadannan alamu?” Sai rabuwa ta shiga tsakanin su.
17 Ils disent donc encore à l’aveugle: Toi, que dis-tu de lui, sur ce qu’il t’a ouvert les yeux? Et il dit: C’est un prophète.
Sai suka tambayi makahon kuma, “Me kake cewa game da shi dashike ya bude maka idanu?” Makahon ya ce, “shi annabi ne.”
18 Les Juifs donc ne crurent pas qu’il avait été aveugle et qu’il avait recouvré la vue, jusqu’à ce qu’ils aient appelé les parents de celui qui avait recouvré la vue.
Har yanzu kam Yahudawan basu yarda da makantarsa ba da ganin gari da ya samu, sai da suka kirayo iyayen shi wanda ya sami ganin garin.
19 Et ils les interrogèrent, disant: Celui-ci est-il votre fils, que vous dites être né aveugle? Comment donc voit-il maintenant?
Su ka tambayi iyayen, “Wannan shine yaronku da kuka ce an haife shi makaho? Yaya yanzu ya ke iya gani?”
20 Ses parents [leur] répondirent et dirent: Nous savons que celui-ci est notre fils, et qu’il est né aveugle;
Sai iyayen suka amsa masu, “Mun san wannan yaronmu ne kuma a makaho aka haife shi.
21 mais comment il voit maintenant, nous ne le savons pas; et qui lui a ouvert les yeux, nous ne le savons pas, nous; il a de l’âge, interrogez-le, il parlera de ce qui le concerne.
Yadda ya ke gani yanzu, bamu sani ba, kuma wanda ya bude masa idanu, bamu sani ba. Ku tambaye shi, ba yaro ba ne. Zai iya magana don kansa.”
22 Ses parents dirent ces choses, parce qu’ils craignaient les Juifs; car les Juifs étaient déjà convenus que si quelqu’un le confessait comme le Christ, il serait exclu de la synagogue.
Iyayensa sun fadi wadannan abubuwan, domin suna ji tsoron Yahudawan. Gama Yahudiyawan sun rigaya sun yarda duk wanda yace Yesu Almasihu ne, za a fitar dashi daga majami'a.
23 C’est pourquoi ses parents dirent: Il a de l’âge, interrogez-le.
Domin wannan ne, iyayensa suka ce, “Ai shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
24 Ils appelèrent donc, pour la seconde fois, l’homme qui avait été aveugle, et lui dirent: Donne gloire à Dieu; nous savons que cet homme est un pécheur.
Suka sake kiran mutumin dake makaho karo na biyu, suka ce masa, “Ka girmama Allah. Mu kam mun sani wannan mutum mai zunubi ne.”
25 Il répondit donc: S’il est un pécheur, je ne sais; je sais une chose, c’est que j’étais aveugle, et que maintenant je vois.
Sai wannan mutum ya amsa, “Ban sani ba ko shi mai zunubi ne. Abu guda daya na sani: da Ni makaho ne, amma yanzu ina gani.”
26 Et ils lui dirent encore: Que t’a-t-il fait? Comment a-t-il ouvert tes yeux?
Sai su ka ce masa, “Me ya yi maka? Ta yaya ya bude idanunka?”
27 Il leur répondit: Je vous l’ai déjà dit, et vous n’avez pas écouté. Pourquoi voulez-vous encore l’entendre? Voulez-vous aussi, vous, devenir ses disciples?
Ya amsa, “Na rigaya na gaya maku, amma ba ku ji ba! Don me kuke so ku sake ji? Ko kuma kuna so ku zama almajiransa, haka ne?
28 Ils l’injurièrent et dirent: Toi, tu es le disciple de celui-là; mais nous, nous sommes disciples de Moïse.
Sai suka kwabe shi suka ce, “kai ne almajirinsa, amma mu almajiran Musa ne.
29 Pour nous, nous savons que Dieu a parlé à Moïse; mais, pour celui-ci, nous ne savons d’où il est.
Mun sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum, bamu san ko daga ina ne ya zo ba.”
30 L’homme répondit et leur dit: En ceci pourtant il y a une chose étrange, que vous ne sachiez pas d’où il est, et il a ouvert mes yeux.
Mutumin ya amsa masu ya ce, “Tirkashi, baku san inda ya fito ba, duk da haka shi ya bude mani idanu.
31 Or, nous savons que Dieu n’écoute pas les pécheurs; mais si quelqu’un est pieux envers Dieu et fait sa volonté, celui-là il l’écoute.
Mun san da cewa Allah baya jin masu zunubi, amma idan wani mai ibada ne yana kuma yin nufinsa, to yana jin sa.
32 Jamais on n’entendit dire que quelqu’un ait ouvert les yeux d’un aveugle-né. (aiōn )
Tunda duniya ta fara ba a taba jin cewa wani ya bude idanun wanda aka haifa makaho ba. (aiōn )
33 Si celui-ci n’était pas de Dieu, il ne pourrait rien faire.
In mutumin nan ba daga Allah yake ba, ba zai iya yin komai ba.”
34 Ils répondirent et lui dirent: Tu es entièrement né dans le péché, et tu nous enseignes! Et ils le chassèrent dehors.
Suka amsa suka ce masa, “an haife ka cikin zunubai, yanzu kana so ka yi mana koyarwa?” Sai suka fitar da shi.
35 Jésus apprit qu’ils l’avaient chassé dehors, et l’ayant trouvé, il lui dit: Crois-tu au Fils de Dieu?
Yesu ya ji cewa sun fitar da shi daga majami'a. Da ya same shi sai ya ce masa, “Kana bada gaskiya ga Dan Allah?”
36 Il répondit et dit: Qui est-il, Seigneur, afin que je croie en lui?
Sai ya amsa masa yace, “Wanene shi, Ubangiji, da zan bada gaskiya gare shi?”
37 Et Jésus lui dit: Et tu l’as vu, et celui qui te parle, c’est lui.
Yesu yace masa, “Ai ka gan shi, shine wanda yake magana da kai.”
38 Et il dit: Je crois, Seigneur! Et il lui rendit hommage.
Mutumin ya ce, “Ubangiji, Na bada gaskiya.” Sai ya yi masa sujada.
39 Et Jésus dit: Moi, je suis venu dans ce monde pour [le] jugement, afin que ceux qui ne voient pas, voient; et que ceux qui voient deviennent aveugles.
Yesu ya ce, “Don hukunci na zo wannan duniya domin wadanda ba su gani su gani, saboda kuma wadanda suke gani su zama makafi.”
40 Et quelques-uns d’entre les pharisiens qui étaient avec lui entendirent ces choses, et lui dirent: Et nous, sommes-nous aussi aveugles?
Wadansu Farisawa wadanda suke tare da shi suka ji wadannan abubuwan, suka tambaye shi, “Muma makafi ne?”
41 Jésus leur dit: Si vous étiez aveugles, vous n’auriez pas de péché; mais maintenant vous dites: Nous voyons! – votre péché demeure.
Yesu ya ce masu, “Inda ku makafi ne, da ba ku da zunubi, amma yanzu kun ce, 'Muna gani', don haka zunubinku ya tabbata.