< Job 7 >

1 L’homme n’a-t-il pas une vie de labeur sur la terre? Et ses jours ne sont-ils pas comme les jours d’un mercenaire?
“Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
2 Comme l’esclave soupire après l’ombre, et comme le mercenaire attend son salaire,
Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
3 Ainsi j’ai eu pour partage des mois de déception, et des nuits de misère me sont assignées.
Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
4 Si je me couche, alors je dis: Quand me lèverai-je et quand l’obscurité prendra-t-elle fin? et je suis excédé d’agitations jusqu’au point du jour.
Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
5 Ma chair est couverte de vers et de croûtes de terre, ma peau se retire et suppure.
Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
6 Mes jours s’en vont plus vite qu’une navette, et finissent sans espérance.
“Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
7 Souviens-toi que ma vie n’est qu’un souffle: mon œil ne reverra pas le bien;
Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
8 L’œil qui me regarde ne me reverra plus; tes yeux sont sur moi, et je ne suis plus.
Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
9 La nuée disparaît et s’en va; ainsi celui qui descend au shéol n’en remonte pas, (Sheol h7585)
Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol h7585)
10 Il ne revient plus dans sa maison, et son lieu ne le reconnaît plus.
Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
11 Aussi je ne retiendrai pas ma bouche; je parlerai dans la détresse de mon esprit, je discourrai dans l’amertume de mon âme.
“Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
12 Suis-je une mer, suis-je un monstre marin, que tu établisses des gardes autour de moi?
Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
13 Quand je dis: Mon lit me consolera, ma couche allégera ma détresse,
Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
14 Alors tu m’effraies par des songes, tu me terrifies par des visions,
duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
15 Et mon âme choisit la suffocation, – plutôt la mort que mes os:
Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
16 J’en suis dégoûté; je ne vivrai pas à toujours. Laisse-moi, car mes jours sont vanité.
Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
17 Qu’est-ce que l’homme que tu fasses grand cas de lui, et que ton cœur s’occupe de lui,
“Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
18 Et que tu le visites chaque matin, que tu l’éprouves à tout moment?
har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
19 Pourquoi ne détournes-tu pas les yeux de moi, et ne me laisses-tu pas tranquille jusqu’à ce que j’aie avalé ma salive?
Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
20 J’ai péché; – que t’ai-je fait? Toi qui observes l’homme, pourquoi m’as-tu placé pour être l’objet de tes coups, de sorte que je suis un fardeau à moi-même?
In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
21 Et pourquoi ne pardonnes-tu pas ma transgression, et ne fais-tu point passer mon iniquité? Car maintenant je me coucherai dans la poussière, et tu me chercheras, et je ne serai plus.
Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”

< Job 7 >