< Job 40 >
1 Et l’Éternel répondit à Job et dit:
Ubangiji ya ce wa Ayuba,
2 Celui qui conteste avec le Tout-puissant l’instruira-t-il? Celui qui reprend Dieu, qu’il réponde à cela!
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
3 Et Job répondit à l’Éternel et dit:
Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
4 Voici, je suis une créature de rien, que te répliquerai-je? Je mettrai ma main sur ma bouche.
“Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
5 J’ai parlé une fois, et je ne répondrai plus; et deux fois, et je n’ajouterai rien.
Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
6 Et l’Éternel répondit à Job du milieu du tourbillon et dit:
Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
7 Ceins tes reins comme un homme; je t’interrogerai, et tu m’instruiras!
“Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
8 Veux-tu donc anéantir mon jugement? Me démontreras-tu inique afin de te justifier?
“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
9 As-tu un bras comme Dieu, et tonneras-tu de ta voix comme lui?
Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
10 Pare-toi, je te prie, de grandeur et de magnificence; revêts-toi de majesté et de gloire!
Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
11 Répands les fureurs de ta colère, et regarde tout ce qui s’élève et abaisse-le;
Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
12 Regarde tout ce qui s’élève [et] humilie-le, et écrase sur place les méchants;
Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
13 Cache-les ensemble dans la poussière, lie leurs faces dans un lieu caché:
Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
14 Alors moi aussi je te célébrerai, parce que ta droite te sauve!
Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
15 Vois le béhémoth, que j’ai fait avec toi: il mange l’herbe comme le bœuf.
“Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
16 Regarde donc: sa force est dans ses reins, et sa puissance dans les muscles de son ventre.
Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
17 Il courbe sa queue comme un cèdre; les nerfs de sa cuisse sont entrelacés;
Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
18 Ses os sont des tubes d’airain, ses membres sont des barres de fer!
Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
19 Il est la première des voies de Dieu: celui qui l’a fait lui a fourni son épée.
Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
20 Car les montagnes lui apportent [sa] pâture, là où se jouent toutes les bêtes des champs.
Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
21 Il se couche sous les lotus dans une retraite de roseaux et de marécages;
Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
22 Les lotus le couvrent de leur ombre, les saules de la rivière l’environnent.
Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
23 Voici, que le fleuve déborde avec violence, il ne se précipite pas; il est plein d’assurance si un Jourdain se jette contre sa gueule.
Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
24 Le prendra-t-on en face? Lui percera-t-on le nez dans une trappe?
Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?