< Job 37 >
1 À cause de cela aussi mon cœur tremble, et tressaille comme s’il sortait de sa place.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 Écoutez donc le bruit éclatant de sa voix et le grondement qui sort de sa bouche!
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 Il le dirige sous tous les cieux, et son éclair, jusqu’aux extrémités de la terre:
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 Après lui une voix rugit. Il tonne de sa voix majestueuse, et il ne retient pas ses éclairs quand il fait entendre sa voix.
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 Dieu tonne merveilleusement de sa voix, faisant de grandes choses que nous ne comprenons pas.
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 Car il dit à la neige: Tombe sur la terre! et aussi aux averses de pluie, et aux averses des pluies de sa force.
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 Il met un sceau sur la main de tout homme, afin que tous les hommes connaissent son œuvre.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 Les bêtes sauvages rentrent dans leurs gîtes, et demeurent dans leurs repaires.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 Des chambres [du midi] vient le tourbillon, et des vents du nord, le froid.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 Au souffle de Dieu se forme la glace, et la largeur des eaux se resserre.
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 Il charge d’eau le nuage; sa lumière dissipe les nuées;
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 Et sous sa conduite elles tournoient en tout sens, pour accomplir leur œuvre, tout ce qu’il leur commande sur la face du cercle de la terre,
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 Soit qu’il les fasse venir comme verge, ou pour sa terre, ou en bonté.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 Écoute ceci, Job; tiens-toi là, et discerne les œuvres merveilleuses de Dieu.
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 Sais-tu comment Dieu les a disposées et comment il fait briller l’éclair de sa nuée?
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 Comprends-tu le balancement des nuages, les œuvres merveilleuses de celui qui est parfait en connaissance, –
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 Pourquoi tes vêtements sont chauds quand il donne du repos à la terre par le vent du midi?
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 As-tu étendu avec lui la voûte céleste, aussi ferme qu’un miroir de fonte?
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 Fais-nous savoir ce que nous lui dirons! Nous ne savons préparer [des paroles], à cause de [nos] ténèbres.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 Lui racontera-t-on que je parle? Si quelqu’un lui parle, il sera sûrement englouti.
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 Et maintenant on ne voit pas la lumière brillante, elle est [cachée] dans les nues; mais le vent passe et les [chasse, et] produit un ciel clair.
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 L’or vient du nord; – par-devers Dieu est la majesté terrible.
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 Le Tout-puissant, nous ne le trouvons pas; grand en force, en jugement et en beaucoup de justice, il n’opprime pas.
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 C’est pourquoi les hommes le craindront; aucun des sages de cœur ne le contemplera.
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”