< Job 35 >
1 Et Élihu reprit la parole et dit:
Sai Elihu ya ce,
2 Penses-tu que ceci soit fondé, que tu aies dit: Je suis plus juste que Dieu?
“Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
3 Car tu as demandé quel profit tu en as: Quel avantage en ai-je de plus que si j’avais péché?
Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
4 Je te répliquerai, moi, par des paroles, et à tes amis avec toi:
“Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
5 Regarde les cieux et vois, et contemple les nuées: elles sont plus hautes que toi.
Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
6 Si tu pèches, quel tort lui causes-tu? et si tes transgressions se multiplient, que lui as-tu fait?
In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
7 Si tu es juste, que lui donnes-tu, ou que reçoit-il de ta main?
In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
8 Pour un homme comme toi ta méchanceté [peut être quelque chose], et pour un fils d’homme, ta justice.
Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
9 On crie à cause de la multitude des oppressions, et on appelle au secours à cause du bras des grands;
“Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
10 Et on ne dit pas: Où est Dieu, mon créateur, qui donne des chants de joie dans la nuit,
Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
11 Qui nous rend plus instruits que les bêtes de la terre, et plus sages que les oiseaux des cieux?
wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
12 Alors on crie, et il ne répond pas, à cause de l’orgueil des méchants.
Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
13 Certainement ce qui est vanité Dieu ne l’écoute pas, et le Tout-puissant ne le regarde pas.
Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
14 Quoique tu dises que tu ne le vois pas, le jugement est devant lui; attends-le donc.
Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
15 Et maintenant, si sa colère n’a pas encore visité, [Job] ne connaît-il pas [sa] grande arrogance?
Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
16 Et Job ouvre sa bouche vainement; il entasse des paroles sans science.
Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”