< Job 33 >
1 Mais toutefois, Job, je te prie, écoute ce que je dis, et prête l’oreille à toutes mes paroles.
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 Voici, j’ai ouvert ma bouche, ma langue parle dans mon palais.
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 Mes paroles seront selon la droiture de mon cœur, et ce que je sais mes lèvres le diront avec pureté.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 L’Esprit de Dieu m’a fait, et le souffle du Tout-puissant m’a donné la vie.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 Si tu le peux, réponds-moi; arrange [des paroles] devant moi, tiens-toi là!
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Voici, je suis comme toi quant à Dieu, je suis fait d’argile, moi aussi.
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 Voici, ma terreur ne te troublera pas, et mon poids ne t’accablera pas.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 Certainement tu as dit à mes propres oreilles, et j’ai entendu le son de [tes] discours:
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 Moi, je suis net, sans transgression; je suis pur, et il n’y a pas d’iniquité en moi;
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 Voici, il trouve des occasions d’inimitié contre moi, il me considère comme son ennemi;
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 Il a mis mes pieds dans les ceps, il observe toutes mes voies.
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 Voici, je te répondrai qu’en cela tu n’as pas été juste, car Dieu est plus grand que l’homme.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 Pourquoi contestes-tu avec lui? car d’aucune de ses actions il ne rend compte.
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 Car Dieu parle une fois, et deux fois – [et] l’on n’y prend pas garde –
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 Dans un songe, dans une vision de nuit, quand un profond sommeil tombe sur les hommes, quand ils dorment sur leurs lits:
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 Alors il ouvre l’oreille aux hommes et scelle l’instruction qu’il leur donne,
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 Pour détourner l’homme de ce qu’il fait; et il cache l’orgueil à l’homme;
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 Il préserve son âme de la fosse, et sa vie de se jeter sur l’épée.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 Il est châtié aussi sur son lit par la douleur, et la lutte de ses os est continuelle,
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 Et sa vie prend en dégoût le pain, et son âme l’aliment qu’il aimait;
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 Sa chair est consumée et ne se voit plus, et ses os, qu’on ne voyait pas, sont mis à nu;
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 Et son âme s’approche de la fosse, et sa vie, de ceux qui font mourir.
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 S’il y a pour lui un messager, un interprète, un entre mille, pour montrer à l’homme ce qui, pour lui, est la droiture,
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 Il lui fera grâce, et il dira: Délivre-le pour qu’il ne descende pas dans la fosse: j’ai trouvé une propitiation.
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 [Alors] sa chair aura plus de fraîcheur que dans l’enfance; il reviendra aux jours de sa jeunesse;
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 Il suppliera Dieu, et [Dieu] l’aura pour agréable; et il verra sa face avec des chants de triomphe, et [Dieu] rendra à l’homme sa justice.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 Il chantera devant les hommes, et dira: J’ai péché et j’ai perverti la droiture, et il ne me l’a pas rendu;
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 Il a délivré mon âme pour qu’elle n’aille pas dans la fosse, et ma vie verra la lumière.
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 Voilà, Dieu opère toutes ces choses deux fois, trois fois, avec l’homme,
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 Pour détourner son âme de la fosse, pour qu’il soit illuminé de la lumière des vivants.
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 Sois attentif, Job, écoute-moi; tais-toi, et moi je parlerai.
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 S’il y a quelque chose à dire, réponds-moi; parle, car je désire que tu sois trouvé juste;
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 Sinon, écoute-moi; tais-toi, et je t’enseignerai la sagesse.
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”