< Job 31 >
1 J’ai fait alliance avec mes yeux: et comment aurais-je arrêté mes regards sur une vierge?
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 Et quelle aurait été d’en haut [ma] portion de la part de Dieu, et, des hauts lieux, [mon] héritage de la part du Tout-puissant?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 La calamité n’est-elle pas pour l’inique, et le malheur pour ceux qui pratiquent le mal?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 Lui, ne voit-il pas mon chemin, et ne compte-t-il point tous mes pas?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 Si j’ai marché avec fausseté, si mes pieds se sont hâtés vers la fraude,
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 Qu’il me pèse dans la balance de justice, et Dieu reconnaîtra ma perfection.
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 Si mon pas s’est détourné du chemin, et si mon cœur a suivi mes yeux, et si quelque souillure s’est attachée à ma main,
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 Que je sème et qu’un autre mange, et que mes rejetons soient déracinés!…
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 Si mon cœur s’est laissé attirer vers une femme et que j’aie fait le guet à la porte de mon prochain,
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 Que ma femme tourne la meule pour un autre, et que d’autres se penchent sur elle;
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 Car c’est là une infamie, et une iniquité punissable par les juges:
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 Car c’est un feu qui dévore jusque dans l’abîme et qui détruirait par la racine tout mon revenu…
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 Si j’ai méprisé le droit de mon serviteur ou de ma servante quand ils contestaient avec moi,
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 Que ferais-je quand Dieu se lèverait? et s’il me visitait, que lui répondrais-je?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 Celui qui m’a fait dans le sein de ma mère, ne les a-t-il pas faits [eux aussi], et un seul et même [Dieu] ne nous a-t-il pas formés dans la matrice?…
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 Si j’ai refusé aux misérables leur désir, si j’ai fait défaillir les yeux de la veuve;
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 Si j’ai mangé seul mon morceau, et que l’orphelin n’en ait pas mangé; –
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 Car dès ma jeunesse il m’a honoré comme un père, et dès le ventre de ma mère j’ai soutenu la [veuve]; …
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 Si j’ai vu quelqu’un périr faute de vêtement, et le pauvre manquer de couverture;
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 Si ses reins ne m’ont pas béni, et qu’il ne se soit pas réchauffé avec la toison de mes agneaux;
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 Si j’ai secoué ma main contre un orphelin, parce que je voyais mon appui dans la porte:
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 Que mon épaule se démette de sa jointure, et que mon bras cassé se détache de l’os!
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 Car la calamité de la part de Dieu m’était une frayeur, et devant sa grandeur je ne pouvais rien…
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 Si j’ai mis ma confiance dans l’or, si j’ai dit à l’or fin: C’est à toi que je me fie;
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 Si je me suis réjoui de ce que mes biens étaient grands, et de ce que ma main avait beaucoup acquis;
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 Si j’ai vu le soleil quand il brillait, et la lune quand elle marchait dans sa splendeur,
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 Et que mon cœur ait été séduit en secret, et que ma bouche ait embrassé ma main, –
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 Cela aussi serait une iniquité punissable par le juge, car j’aurais renié le Dieu qui est en haut; …
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 Si je me suis réjoui dans la calamité de celui qui me haïssait, si j’ai été ému de joie lorsque le malheur l’a trouvé; –
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 Même je n’ai pas permis à ma bouche de pécher, de demander sa vie par une exécration; …
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 Si les gens de ma tente n’ont pas dit: Qui trouvera quelqu’un qui n’ait pas été rassasié de la chair de ses bêtes? –
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 L’étranger ne passait pas la nuit dehors, j’ouvrais ma porte sur le chemin; …
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 Si j’ai couvert ma transgression comme Adam, en cachant mon iniquité dans mon sein,
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 Parce que je craignais la grande multitude, et que le mépris des familles me faisait peur, et que je sois resté dans le silence et ne sois pas sorti de ma porte…
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 Oh! si j’avais quelqu’un pour m’écouter! Voici ma signature. Que le Tout-puissant me réponde, et que ma partie adverse fasse un écrit!
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 Ne le porterais-je pas sur mon épaule? Ne le lierais-je pas sur moi comme une couronne?
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 Je lui déclarerais le nombre de mes pas; comme un prince je m’approcherais de lui…
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 Si ma terre crie contre moi, et que ses sillons pleurent ensemble,
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 Si j’en ai mangé le revenu sans argent, et que j’aie tourmenté à mort l’âme de ses possesseurs,
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 Que les épines croissent au lieu de froment, et l’ivraie au lieu d’orge! Les paroles de Job sont finies.
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.