< Job 26 >

1 Et Job répondit et dit:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Comme tu as aidé celui qui n’avait pas de puissance! Comme tu as délivré le bras qui était sans force!
“Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
3 Quel conseil tu as donné à celui qui n’avait pas de sagesse! et quelle abondance d’intelligence tu as montrée!
Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
4 Pour qui as-tu prononcé des paroles, et de qui est le souffle qui est sorti de toi?
Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
5 Les trépassés tremblent au-dessous des eaux et de ceux qui les habitent.
“Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
6 Le shéol est à nu devant lui, et l’abîme n’a pas de voile. (Sheol h7585)
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol h7585)
7 Il étend le nord sur le vide, il suspend la terre sur le néant.
Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
8 Il serre les eaux dans ses nuages, et la nuée ne se fend pas sous elles;
Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
9 Il couvre la face de son trône et étend ses nuées par-dessus.
Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
10 Il a tracé un cercle fixe sur la face des eaux, jusqu’à la limite extrême où la lumière confine aux ténèbres.
ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
11 Les colonnes des cieux branlent et s’étonnent à sa menace.
Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
12 Il soulève la mer par sa puissance, et, par son intelligence, il brise Rahab.
Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
13 Par son Esprit le ciel est beau; sa main a formé le serpent fuyard.
Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
14 Voici, ces choses sont les bords de ses voies, et combien faible est le murmure que nous en avons entendu! Et le tonnerre de sa force, qui peut le comprendre?
Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”

< Job 26 >