< Job 18 >
1 Et Bildad, le Shukhite, répondit et dit:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 Jusques à quand tendrez-vous des pièges avec vos paroles? Soyez intelligents, et puis nous parlerons.
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 Pourquoi sommes-nous considérés comme des bêtes, et sommes-nous stupides à vos yeux?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 Toi qui déchires ton âme dans ta colère, la terre sera-t-elle abandonnée à cause de toi, et le rocher sera-t-il transporté de sa place?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 Or la lumière des méchants sera éteinte, et la flamme de son feu ne luira point;
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 La lumière sera ténèbres dans sa tente, et sa lampe sera éteinte au-dessus de lui.
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 Les pas de sa force seront resserrés, et son propre conseil le renversera:
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 Car il est poussé dans le filet par ses propres pieds; et il marche sur les mailles du filet;
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 Le piège le prend par le talon, le lacet le saisit;
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 Sa corde est cachée dans la terre, et sa trappe sur le sentier.
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 De toutes parts des terreurs l’alarment et le poussent çà et là, s’attachant à ses pas.
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 Sa force est affaiblie par la faim, et la calamité est prête à son côté.
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 Le premier-né de la mort dévore les membres de son corps, il dévore ses membres.
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 Ce qui faisait sa confiance est arraché de sa tente, et il est forcé de marcher vers le roi des terreurs.
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 Ce qui n’est pas à lui habite dans sa tente, le soufre est répandu sur son habitation.
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 En bas ses racines sèchent, et en haut ses branches sont coupées.
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 Sa mémoire périt de dessus la terre, et il n’a pas de nom sur la face du pays.
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 Il est repoussé de la lumière dans les ténèbres; on le bannit du monde.
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 Il n’a pas d’enfants ni de postérité parmi son peuple, personne qui lui survive dans les lieux de son séjour.
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 Ceux qui viennent après seront étonnés de son jour, comme l’horreur s’est emparée de ceux qui [les] ont précédés.
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 Certainement, telles sont les demeures de l’inique, et tel est le lieu de celui qui ne connaît pas Dieu.
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”