< Job 16 >

1 Et Job répondit et dit:
Sai Ayuba ya amsa,
2 J’ai entendu bien des choses comme celles-là; vous êtes tous des consolateurs fâcheux.
“Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
3 Y aura-t-il une fin à [ces] paroles de vent? Qu’est-ce qui t’irrite, que tu répondes?
Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
4 Moi aussi, je pourrais parler comme vous; si votre âme était à la place de mon âme, je pourrais entasser des paroles contre vous et secouer ma tête contre vous!
Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
5 [Mais] je vous fortifierais de ma bouche, et la consolation de mes lèvres allégerait [vos douleurs].
Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
6 Si je parle, ma douleur n’est pas allégée; et si je me tais, s’éloignera-t-elle de moi?
“Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
7 Mais maintenant, il m’a fatigué…: tu as dévasté toute ma famille;
Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
8 Tu m’as étreint, c’est un témoignage, et ma maigreur se lève contre moi, elle dépose, à ma face, contre moi.
Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
9 Sa colère me déchire et me poursuit; il grince des dents contre moi; [comme] mon adversaire, il aiguise contre moi ses yeux.
Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
10 Ils ouvrent contre moi leur bouche, ils me frappent les joues avec mépris; ils s’attroupent contre moi.
Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
11 Dieu m’a livré à l’inique, et m’a jeté entre les mains des méchants.
Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
12 J’étais en paix, et il m’a brisé; il m’a saisi par la nuque et m’a broyé, et m’a dressé pour lui servir de but.
Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
13 Ses archers m’ont environné; il me perce les reins et ne m’épargne pas; il répand mon fiel sur la terre.
maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
14 Il fait brèche en moi, brèche sur brèche; il court sur moi comme un homme fort.
Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
15 J’ai cousu un sac sur ma peau, et j’ai dégradé ma corne dans la poussière.
“Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
16 Mon visage est enflammé à force de pleurer, et sur mes paupières est l’ombre de la mort,
Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
17 Quoiqu’il n’y ait pas de violence dans mes mains, et que ma prière soit pure.
duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
18 Ô terre, ne recouvre pas mon sang, et qu’il n’y ait pas de place pour mon cri!
“Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
19 Maintenant aussi, voici, mon témoin est dans les cieux, et celui qui témoigne pour moi est dans les lieux élevés.
Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
20 Mes amis se moquent de moi… vers Dieu pleurent mes yeux.
Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
21 Que n’y a-t-il un arbitre pour l’homme auprès de Dieu, et pour un fils d’homme vis-à-vis de son ami!
a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
22 Car les années s’écoulent dont on peut compter le nombre, et je m’en vais dans le chemin [d’où] je ne reviendrai pas.
“Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.

< Job 16 >