< Job 13 >

1 Voici, tout cela, mon œil l’a vu, mon oreille l’a entendu et l’a compris.
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 Ce que vous connaissez, moi aussi je le connais; je ne vous suis pas inférieur.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 Mais je parlerai au Tout-puissant, et mon plaisir sera de raisonner avec Dieu;
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 Mais pour vous, vous êtes des forgeurs de mensonges, des médecins de néant, vous tous!
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 Oh! si seulement vous demeuriez dans le silence! et ce serait votre sagesse.
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Écoutez donc mon plaidoyer, et prêtez attention aux arguments de mes lèvres.
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 Est-ce pour Dieu que vous direz des choses iniques? Et pour lui, direz-vous ce qui est faux?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 Ferez-vous acception de sa personne? Plaiderez-vous pour Dieu?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 Vous est-il agréable qu’il vous sonde? Vous moquerez-vous de lui comme on se moque d’un mortel?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 Certainement il vous reprendra, si en secret vous faites acception de personnes.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 Sa majesté ne vous troublera-t-elle pas? Et sa frayeur ne tombera-t-elle pas sur vous?
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 Vos discours sentencieux sont des proverbes de cendre, vos retranchements sont des défenses de boue.
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 Gardez le silence, laissez-moi, et moi je parlerai, quoi qu’il m’arrive.
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 Pourquoi prendrais-je ma chair entre mes dents, et mettrais-je ma vie dans ma main?
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 Voici, qu’il me tue, j’espérerai en lui; seulement, je défendrai mes voies devant lui.
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 Ce sera même ma délivrance, qu’un impie n’entre pas devant sa face.
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 Écoutez, écoutez mon discours, et que ma déclaration [pénètre] dans vos oreilles!
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 Voyez, j’exposerai [ma] juste cause: je sais que je serai justifié.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 Qui est celui qui contestera avec moi? Car maintenant, si je me taisais, j’expirerais.
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 Seulement ne fais pas deux choses à mon égard; alors je ne me cacherai pas loin de ta face:
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 Éloigne ta main de dessus moi, et que ta terreur ne me trouble pas.
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 Et appelle, et moi je répondrai, ou bien je parlerai, et toi, réponds-moi!
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 Quel est le nombre de mes iniquités et de mes péchés? Fais-moi connaître ma transgression et mon péché!
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 Pourquoi caches-tu ta face, et me tiens-tu pour ton ennemi?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 Veux-tu épouvanter une feuille chassée [par le vent], et poursuivre du chaume sec?
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 Car tu écris des choses amères contre moi, et tu me fais hériter des iniquités de ma jeunesse;
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 Et tu mets mes pieds dans les ceps, et tu observes tous mes sentiers; tu as tracé une ligne autour des plantes de mes pieds;
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 Et celui [que tu poursuis] dépérit comme une chose pourrie, comme un vêtement que la teigne a rongé.
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.

< Job 13 >