< Jérémie 9 >

1 Oh! ma tête, que n’est-elle des eaux, et mes yeux, une fontaine de larmes! et je pleurerais jour et nuit les blessés à mort de la fille de mon peuple!
Da ma kaina maɓulɓulan ruwa ne idanuna kuma maɓulɓulan hawaye! Da sai in yi kuka dare da rana saboda mutanena da aka kashe.
2 Oh! qui me donnera dans le désert une cabane de voyageur! et j’abandonnerais mon peuple et je m’en irais d’avec eux; car ils sont tous des adultères, une assemblée de perfides.
Da ma a hamada ina da wurin da matafiye za su sauka, don in bar mutanena in tafi in bar su; gama dukansu mazinata ne, taron mutane marasa aminci.
3 Et ils bandent leur langue, leur arc de mensonge, et ils ne sont pas vaillants dans le pays pour la fidélité; car ils passent d’iniquité en iniquité, et ne me connaissent pas, dit l’Éternel.
“Sun tanƙwasa harshensu kamar baka, don su harba ƙarya; ba da gaskiya ba ne suke nasara a cikin ƙasar. Sukan tashi daga wannan zunubi zuwa wancan; ba su san ni ba,” in ji Ubangiji.
4 Gardez-vous chacun de son ami, et ne vous confiez en aucun frère; car tout frère ne fera que supplanter, et tout ami marche dans la calomnie.
“Ka yi hankali da abokanka; kada ka amince da’yan’uwanka. Gama kowane ɗan’uwa munafuki ne, kowane aboki kuma mai kushe ne.
5 Et chacun d’eux trompe son ami, et ne dit pas la vérité; ils ont enseigné leur langue à dire le mensonge, ils se fatiguent à faire le mal.
Aboki kan ruɗi aboki, ba mai faɗar gaskiya. Sun koya wa harshensu faɗar ƙarya; sun gajiyar da kansu da yin zunubi.
6 Ton habitation est au milieu de la tromperie; à cause de la tromperie ils refusent de me connaître, dit l’Éternel.
Kai kana zama a tsakiyar ruɗu; cikin ruɗunsu sun ƙi su san ni,” in ji Ubangiji.
7 C’est pourquoi, ainsi dit l’Éternel des armées: Voici, je vais les affiner et les éprouver; car comment agirais-je à l’égard de la fille de mon peuple?
Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi zan tace in kuma gwada su, gama me kuwa zan yi saboda zunubin mutanena?
8 Leur langue est une flèche mortelle, elle profère la tromperie; de sa bouche il parle de paix avec son ami, mais au-dedans il lui dresse des embûches.
Harshensu kibiya ce mai dafi; yana magana da ruɗu. Da bakinsa kowa yana maganar alheri da maƙwabcinsa, amma a zuciyarsa ya sa masa tarko.
9 Ne les punirais-je pas à cause de ces choses? dit l’Éternel; mon âme ne se vengerait-elle pas d’une nation comme celle-là?
Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in ɗau fansa a kan irin al’umma kamar wannan ba?”
10 J’élèverai une voix de pleurs et une lamentation sur les montagnes, et une complainte sur les pâturages du désert, car ils sont brûlés, de sorte que personne n’y passe et qu’on n’y entend pas la voix des troupeaux; tant les oiseaux des cieux que les bêtes ont fui; ils s’en sont allés.
Zan yi kuka in yi kururuwa saboda duwatsu in kuma yi makoki game da wuraren kiwon hamada. Sun zama kango ba wanda yake bi cikinta, ba a kuma jin kukan shanu. Tsuntsaye sararin sama sun gudu namun jeji ma duk sun watse.
11 Et je ferai de Jérusalem des monceaux [de ruines], un repaire de chacals; et des villes de Juda, j’en ferai une désolation, de sorte qu’il n’y aura plus d’habitant.
“Zan mai da Urushalima tsibin kufai, wurin zaman diloli; zan kuma lalace garuruwan Yahuda saboda haka ba wanda zai zauna a can.”
12 Qui est l’homme sage? qu’il comprenne cela. Et celui à qui la bouche de l’Éternel a parlé, qu’il le déclare! Pourquoi le pays périt-il, [et] est-il brûlé comme un désert, de sorte que personne n’y passe?
Wane mutum ne yana da isashiyar hikimar fahimtar wannan? Wa Ubangiji ya umarta da zai iya yin bayani? Me ya sa aka lalace ƙasar ta zama kufai kamar hamada da ba wanda zai iya ratsa ta?
13 Et l’Éternel dit: Parce qu’ils ont abandonné ma loi que j’avais mise devant eux, et qu’ils n’ont pas écouté ma voix, et parce qu’ils n’ont pas marché en elle,
Ubangiji ya ce, “Domin sun bar dokata, wadda na sa a gabansu; ba su yi biyayya da ni ko su bi dokata ba.
14 et qu’ils ont marché suivant le penchant obstiné de leur cœur et après les Baals, ce que leurs pères leur ont enseigné.
A maimako, sun bi taurin zuciyarsu; suka bi Ba’al, yadda kakanninsu suka koya musu.”
15 C’est pourquoi, ainsi dit l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël: Voici, je vais faire manger de l’absinthe à ce peuple, et je leur ferai boire de l’eau de fiel;
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Ga shi zan sa wannan mutane su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwan dafi.
16 et je les disperserai parmi les nations qu’ils n’ont pas connues, eux et leurs pères; et j’enverrai après eux l’épée, jusqu’à ce que je les aie consumés.
Zan watsar da su a cikin al’ummai da su da kakanninsu ba su sani ba, zan kuma fafare su da takobi sai na hallaka su.”
17 Ainsi dit l’Éternel des armées: Considérez, et appelez les pleureuses, et qu’elles viennent; et envoyez vers les femmes sages, et qu’elles viennent,
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku lura yanzu! Ku kira mata masu makoki su zo ku aika wa gwanaye a cikinsu su zo.
18 et qu’elles se hâtent, et qu’elles élèvent une [voix de] lamentation sur nous, et que nos yeux se fondent en larmes, et que l’eau coule de nos paupières.
Bari su zo da sauri su yi kuka a kanmu sai idanunmu sun cika da hawaye giranmu kuma su jiƙe sharkaf.
19 Car une voix de lamentation se fait entendre de Sion: Comme nous sommes détruits, [et] devenus fort honteux! car nous avons abandonné le pays, car ils ont jeté à bas nos demeures.
An ji karar kuka daga Sihiyona cewa, ‘Duba yadda muka lalace! Duba irin babban kunyar da muka sha! Dole mu bar ƙasar domin gidajenmu sun lalace.’”
20 Vous, femmes, écoutez donc la parole de l’Éternel, et que votre oreille reçoive la parole de sa bouche; et enseignez à vos filles la lamentation, et chacune à son amie la complainte.
Yanzu, ya mata, ku ji maganar Ubangiji; ku buɗe kunnuwanku ga maganar bakina. Ku koya wa’yan matanku yadda za su yi kuka; ku koya wa juna makoki.
21 Car la mort est montée par nos fenêtres, elle est entrée dans nos palais, pour retrancher de la rue les petits enfants, [et] des places, les jeunes hommes.
Mutuwa ta haura ta tagoginmu ta kuma shiga katangarmu; ta karkashe’ya’ya a tituna ta kuma karkashe samari a dandali.
22 Dis: Ainsi dit l’Éternel: Oui, le cadavre de l’homme tombera comme du fumier sur la face des champs, et comme la gerbe après le moissonneur, et il n’y a personne qui la recueille.
Ka ce, “Ga abin da Ubangiji ya furta, “‘Gawawwakin mutane za su fāɗi kamar juji a fili, kamar hatsin da aka yanka a bayan mai girbi, da ba mai tara su.’”
23 Ainsi dit l’Éternel: Que le sage ne se glorifie pas dans sa sagesse, et que l’homme vaillant ne se glorifie pas dans sa vaillance; que le riche ne se glorifie pas dans sa richesse;
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa ko mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa ko mai arziki ya yi fariya da arzikinsa,
24 mais que celui qui se glorifie, se glorifie en ceci, qu’il a de l’intelligence et qu’il me connaît; car je suis l’Éternel, qui use de bonté, de jugement et de justice sur la terre, car je trouve mes délices en ces choses-là, dit l’Éternel.
amma bari shi wanda yake taƙama ya yi taƙama da wannan, cewa ya fahimci ya kuma san ni, cewa ni ne Ubangiji, wanda yake yin alheri, gaskiya da kuma adalci a duniya, gama a waɗannan ne nake jin daɗi,” in ji Ubangiji.
25 Voici, des jours viennent, dit l’Éternel, et je punirai tous les circoncis avec les incirconcis,
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta dukan waɗanda aka yi musu kaciya kawai a jiki,
26 l’Égypte, et Juda, et Édom, et les fils d’Ammon, et Moab, et tous ceux qui coupent les coins [de leur barbe], lesquels habitent le désert; car toutes les nations sont incirconcises, et toute la maison d’Israël est incirconcise de cœur.
Masar, Yahuda, Edom, Ammon, Mowab da dukan waɗanda suke zaune a hamada a wurare masu nisa. Gama dukan waɗannan al’ummai marasa kaciya ne, har dukan gidan Isra’ila ma marasa kaciya ne a zuciya.”

< Jérémie 9 >