< Jérémie 43 >

1 Et lorsque Jérémie eut achevé de dire à tout le peuple toutes les paroles de l’Éternel, leur Dieu, toutes ces paroles avec lesquelles l’Éternel, leur Dieu, l’avait envoyé vers eux,
Sa’ad da Irmiya ya gama faɗa wa mutane dukan maganar Ubangiji Allahnsu, duk abin da Ubangiji ya aike shi ya faɗa musu,
2 il arriva qu’Azaria, fils de Hoshahia, et Jokhanan, fils de Karéakh, et tous les hommes orgueilleux, parlèrent à Jérémie, disant: C’est un mensonge que tu dis; l’Éternel, notre Dieu, ne t’a pas envoyé pour [nous] dire: N’allez point en Égypte pour y séjourner.
Azariya ɗan Hoshahiya da Yohanan ɗan Kareya da dukan masu ɗaga kai suka ce wa Irmiya, “Kana ƙarya ne! Ubangiji Allahnmu bai aike ka ka ce, ‘Kada ku tafi Masar don ku zauna a can.’
3 Mais Baruc, fils de Nérija, t’incite contre nous, afin de nous livrer en la main des Chaldéens, pour nous faire mourir et pour nous transporter à Babylone.
Amma Baruk ɗan Neriya yana zuga ka a kanmu don ka ba da mu ga Babiloniyawa, don su kashe mu ko su kai mu zaman bauta a Babilon.”
4 Et Jokhanan, fils de Karéakh, et tous les chefs des forces, et tout le peuple, n’écoutèrent point la voix de l’Éternel, pour habiter dans le pays de Juda.
Saboda haka Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji da dukan mutane suka yi rashin biyayya ga umarnin Ubangiji da su zauna a ƙasar Yahuda.
5 Et Jokhanan, fils de Karéakh, et tous les chefs des forces, prirent tout le reste de Juda, ceux qui, de toutes les nations parmi lesquelles ils avaient été chassés, étaient retournés pour séjourner dans le pays de Juda:
A maimako, Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji suka kwashe raguwar Yahuda waɗanda suka dawo su zauna a ƙasar Yahuda daga dukan al’umman inda aka kora su.
6 les hommes forts, et les femmes, et les petits enfants, et les filles du roi, et toutes les âmes que Nebuzaradan, chef des gardes, avait laissées avec Guedalia, fils d’Akhikam, fils de Shaphan, et Jérémie le prophète, et Baruc, fils de Nérija;
Suka kuma kwashe dukan maza, mata da yara da’ya’yan sarki mata waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari tare da Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da Irmiya annabi da kuma Baruk ɗan Neriya.
7 et ils entrèrent dans le pays d’Égypte, car ils n’avaient pas écouté la voix de l’Éternel; et ils vinrent jusqu’à Takhpanès.
Saboda haka suka shiga Masar cikin rashin biyayya ga Ubangiji suka tafi har can Tafanes.
8 Et la parole de l’Éternel vint à Jérémie, à Takhpanès, disant:
A Tafanes maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
9 Prends dans ta main de grosses pierres, et cache-les dans l’argile, dans le four à briques qui est à l’entrée de la maison du Pharaon, à Takhpanès, sous les yeux des Juifs;
“Yayinda Yahudawa suna kallo, ka ɗauki waɗansu manyan duwatsu tare da kai ka kuma binne su cikin yumɓu a tubalin dakalin ƙofar shiga fadar Fir’auna a Tafanes.
10 et dis-leur: Ainsi dit l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël: Voici, j’envoie, et je prendrai Nebucadretsar, roi de Babylone, mon serviteur; et je mettrai son trône au-dessus de ces pierres que j’ai cachées, et il étendra sur elles sa tente magnifique;
Sa’an nan ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, zan aika wa bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon, zan kuma sa kursiyinsa a kan waɗannan duwatsun da na binne a nan; zai fadada bukkar mulkinsa a bisansu.
11 et il viendra, et frappera le pays d’Égypte: qui pour la mort, à la mort, et qui pour la captivité, à la captivité, et qui pour l’épée, à l’épée.
Zai zo ya yaƙi Masar, ya kawo mutuwa ga waɗanda aka ƙaddara musu mutuwa, zaman bauta ga waɗanda aka ƙaddara musu zaman bauta, da kuma takobi ga waɗanda aka ƙaddara su mutu ta takobi.
12 Et j’allumerai un feu dans les maisons des dieux d’Égypte, et [Nebucadretsar] les brûlera, et les emmènera captifs; et il se revêtira du pays d’Égypte comme un berger se revêt de son vêtement, et il en sortira en paix.
Zai sa wuta wa haikalan allolin Masar; zai ƙone haikalansu yă kuma kwashe allolinsu bayi. Kamar yadda makiyayi yakan yafa mayafinsa kewaye da shi, haka zai yafa Masar kewaye da kansa ya kuma tashi a wurin babu abin da ya same shi.
13 Et il brisera les stèles de Beth-Shémesh, qui est dans le pays d’Égypte, et brûlera par le feu les maisons des dieux de l’Égypte.
A can cikin haikalin rana a Masar zai rushe al’amudan duwatsu yă kuma ƙone haikalan allolin Masar.’”

< Jérémie 43 >