< Jérémie 12 >
1 Éternel! tu es juste quand je conteste avec toi; toutefois je parlerai avec toi de [tes] jugements. Pourquoi la voie des méchants est-elle prospère? [Pourquoi] ceux qui agissent très perfidement sont-ils en paix?
Kullum kai mai adalci ne, ya Ubangiji, sa’ad da na kawo ƙara a gabanka. Duk da haka zan yi magana da kai game da shari’arka. Me ya sa mugaye suke nasara? Me ya sa dukan maciya amana suke zama ba damuwa?
2 Tu les as plantés, même ils prennent racine; ils progressent, même ils portent du fruit. Tu es près, dans leur bouche, mais tu es loin de leurs reins.
Ka dasa su, sun kuwa yi saiwa; sun yi girma suna ba da’ya’ya. Kullum sunanka yana a bakinsu amma kana nesa da zuciyarsu.
3 Mais toi, Éternel! tu me connais, tu m’as vu, et tu as éprouvé mon cœur à ton égard. Traîne-les comme des brebis à la tuerie, et mets-les à part pour le jour de la tuerie.
Duk da haka ka san ni, ya Ubangiji; kana ganina ka kuma gwada tunanina game da kai. Ka ja su kamar tumakin da za a yanka! Ka ware su don ranar yanka!
4 Jusques à quand le pays mènera-t-il deuil et l’herbe de tous les champs séchera-t-elle? À cause de l’iniquité de ceux qui y habitent, le bétail et les oiseaux périssent; car ils disent: Il ne verra pas notre fin.
Har yaushe ƙasar za tă kasance busasshiya ciyawar kowane fili ta bushe? Domin waɗanda suke zaune cikinta mugaye ne, dabbobi da tsuntsaye sun hallaka. Ban da haka ma, mutane suna cewa, “Ba zai ga abin da yake faruwa da mu ba.”
5 Si tu as couru avec les piétons, et qu’ils t’aient lassé, comment rivaliseras-tu avec les chevaux? Et si, dans une terre de paix, tu te crois en sécurité, que feras-tu quand le Jourdain sera enflé?
“In ka yi tsere da mutane a ƙafa suka kuma gajiyar da kai, yaya za ka yi gasa da dawakai? In ka yi tuntuɓe a lafiyayyiyar ƙasa, ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?
6 Car tes frères aussi et la maison de ton père, eux aussi ont agi perfidement envers toi, eux aussi ont crié après toi à plein gosier. Ne les crois point, même s’ils te disent de bonnes [paroles].
’Yan’uwanka, iyalinka har su ma sun bashe ka; sun tā da kuka mai ƙarfi a kanka. Kada ka amince da su, ko da yake suna faɗa maganganu masu kyau game da kai.
7 J’ai abandonné ma maison, j’ai délaissé mon héritage, j’ai livré le bien-aimé de mon âme en la main de ses ennemis.
“Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.
8 Mon héritage m’est devenu comme un lion dans la forêt; il a fait retentir sa voix contre moi, c’est pourquoi je l’ai haï.
Gādona ya zama mini kamar zaki a kurmi. Yana mini ruri; saboda haka na ƙi shi.
9 Mon héritage m’est comme un oiseau de proie tacheté; les oiseaux de proie sont contre lui, tout à l’entour. Venez, assemblez toutes les bêtes des champs, faites-les venir pour dévorer.
Ashe, gādona bai zama mini kamar dabbare dabbaren tsuntsu mai cin nama da sauran tsuntsaye masu cin nama suka kewaye shi da faɗa ba? Tafi ka tattaro dukan namun jeji; ka kawo su su ci.
10 Plusieurs pasteurs ont gâté ma vigne, ils ont foulé mon lot, ils ont réduit le lot de mon désir en un désert aride;
Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.
11 on en a fait une désolation; tout désolé, il mène deuil devant moi; toute la terre est dévastée, car personne ne la prend à cœur.
Za tă zama kango, busasshiya da kuma kango a gabana; ƙasar duka za tă zama kango domin ba wanda ya kula.
12 Sur toutes les hauteurs dans le désert sont venus les destructeurs; car l’épée de l’Éternel dévore depuis un bout du pays jusqu’à l’autre bout du pays: il n’y a de paix pour aucune chair.
A kan dukan tsaunukan nan na hamada masu hallakarwa za su zo, gama takobin Ubangiji zai ci daga wannan iyaka ƙasa zuwa wancan; ba wanda zai zauna lafiya.
13 Ils ont semé du froment, et ils moissonnent des épines; ils se sont tourmentés, [et] ils n’en ont pas eu de profit: soyez confus du rapport de vos [champs], à cause de l’ardeur de la colère de l’Éternel.
Za su shuka alkama, su girbe ƙayayyuwa; za su gajiyar da kansu, ba za su kuwa sami kome ba. Saboda haka ku sha kunyar abin da kuka girbe saboda zafin fushin Ubangiji.”
14 Ainsi dit l’Éternel contre tous mes mauvais voisins qui mettent la main sur l’héritage que j’ai fait hériter à mon peuple, à Israël: Voici, je les arracherai de dessus leur sol, et j’arracherai la maison de Juda du milieu d’eux.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
15 Et il arrivera qu’après que je les aurai arrachés, je leur ferai de nouveau miséricorde et je les ferai retourner chacun à son héritage et chacun dans son pays.
Amma bayan na tumɓuke su, zan sāke jin tausayi in komo da kowannensu zuwa gādonsa da kuma ƙasarsa.
16 Et il arrivera que, s’ils apprennent diligemment les voies de mon peuple, pour jurer par mon nom: L’Éternel est vivant! comme ils ont enseigné à mon peuple à jurer par Baal, ils seront édifiés au milieu de mon peuple.
In kuma suka koyi al’amuran mutanena sosai suka kuma yi rantsuwa da sunana, suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye’ kamar yadda sun taɓa koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za su kahu a cikin jama’ata.
17 Et s’ils n’écoutent pas, j’arracherai entièrement cette nation-là et je la ferai périr, dit l’Éternel.
Amma duk al’ummar da ba tă saurara ba, zan tumɓuke ta ɗungum in kuma hallaka ta,” in ji Ubangiji.