< Isaïe 42 >

1 Voici mon serviteur que je soutiens, mon élu [en qui] mon âme trouve son plaisir. Je mettrai mon Esprit sur lui; il fera valoir le jugement à l’égard des nations.
“Ga bawana, wanda na ɗaukaka, zaɓaɓɓen nan nawa wanda nake jin daɗi; Zan sa Ruhuna a cikinsa zai kuwa kawo adalci ga al’ummai.
2 Il ne criera pas, et il n’élèvera pas sa voix, et il ne la fera pas entendre dans la rue.
Ba zai yi ihu ko ya tā da murya, ko ya daga muryarsa a tituna ba.
3 Il ne brisera pas le roseau froissé, et n’éteindra pas le lin qui brûle à peine. Il fera valoir le jugement en faveur de la vérité.
Iwan da ta tanƙware ba zai karye ba, ba zai kashe lagwani mai hayaƙi ba. Cikin aminci zai kawo adalci;
4 Il ne se lassera pas, et il ne se hâtera pas, jusqu’à ce qu’il ait établi le juste jugement sur la terre; et les îles s’attendront à sa loi.
ba zai kāsa ko ya karai ba sai ya kafa adalci a duniya. Cikin dokarsa tsibirai za su sa zuciya.”
5 Ainsi dit Dieu, l’Éternel, qui a créé les cieux et les a déployés, qui a étendu la terre et ses produits, qui donne la respiration au peuple [qui est] sur elle, et un esprit à ceux qui y marchent:
Ga abin da Allah Ubangiji ya ce, shi da ya halicci sammai ya kuma miƙe su, wanda ya shimfiɗa duniya da dukan abin da ya fito cikinta, wanda ya ba wa mutanenta numfashi, da rai ga waɗanda suke tafiya a kanta.
6 Moi, l’Éternel, je t’ai appelé en justice; et je tiendrai ta main; et je te garderai; et je te donnerai pour [être] une alliance du peuple, pour [être] une lumière des nations,
“Ni Ubangiji, na kira ka cikin adalci; zan riƙe hannunka. Zan kiyaye ka in kuma sa ka zama alkawari ga mutane haske kuma ga Al’ummai,
7 pour ouvrir les yeux aveugles, pour faire sortir de la prison le prisonnier, [et] du cachot ceux qui sont assis dans les ténèbres.
don ka buɗe idanun makafi ka’yantar da kamammu daga kurkuku kuma kunce ɗaurarrun kurkuku masu zama cikin duhu.
8 Je suis l’Éternel: c’est là mon nom; et je ne donnerai pas ma gloire à un autre, ni ma louange à des images taillées.
“Ni ne Ubangiji; sunana ke nan! Ba zan ba da ɗaukakata ga wani ba ko yabona ga gumaka.
9 Voici, les premières choses sont arrivées, et je déclare les choses nouvelles: avant qu’elles germent, je vous les ferai entendre.
Duba, abubuwan da sun tabbata, sababbin abubuwa kuwa nake furtawa; kafin ma su soma faruwa na sanar da su gare ku.”
10 Chantez à l’Éternel un cantique nouveau, sa louange du bout de la terre, vous qui descendez sur la mer, et ce qui la remplit, les îles et ceux qui les habitent!
Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, ku yi yabonsa daga iyakar duniya, ku da kuka gangara zuwa teku, da kome da yake cikinsa, ku tsibirai, da waɗanda suke zama a cikinsu.
11 Que le désert et ses villes élèvent [la voix], les villages qu’habite Kédar! Que les habitants du rocher exultent! Que du haut des montagnes on jette des cris!
Bari hamada da garuruwanta su tā da muryoyinsu; bari wuraren zaman da Kedar ke zama su yi farin ciki. Bari mutanen Sela su rera don farin ciki; bari su yi sowa daga ƙwanƙolin duwatsu.
12 Qu’on donne gloire à l’Éternel, et qu’on déclare sa louange dans les îles!
Bari su ɗaukaka Ubangiji su kuma yi shelar yabonsa a tsibirai.
13 L’Éternel sortira comme un homme vaillant, il éveillera la jalousie comme un homme de guerre; il criera, oui, il jettera des cris; contre ses ennemis il se montrera vaillant.
Ubangiji zai fita ya yi yaƙi kamar mai ƙarfi, kamar jarumi zai yi himma; da ihu zai tā da kirarin yaƙi zai kuma yi nasara a kan abokan gābansa.
14 Dès longtemps je suis resté tranquille, je me suis tu, je me suis contenu. Je crierai comme une femme qui enfante, je soufflerai et je serai haletant à la fois.
“Na daɗe ina shiru, na yi shiru na kuma ƙame kaina. Amma yanzu, kamar mace mai naƙuda, na yi ƙara, ina nishi ina kuma haki.
15 Je dévasterai les montagnes et les collines, et je dessécherai toute leur verdure; je changerai les rivières en îles, et je mettrai à sec les étangs;
Zan lalatar da duwatsu da tuddai in busar da dukan itatuwansu; zan mai da koguna su zama tsibirai in kuma busar da tafkuna.
16 et je ferai marcher les aveugles par un chemin qu’ils n’ont pas connu, par des sentiers qu’ils n’ont pas connus je les conduirai. Je changerai les ténèbres en lumière devant eux, et les chemins tortueux en ce qui est droit. Je leur ferai ces choses, et je ne les abandonnerai pas.
Zan yi wa makafi jagora a hanyoyin da ba su taɓa sani ba, a hanyoyin da ba a saba ba zan bishe su; zan mai da duhu ya zama haske a gabansu in kuma mai da ƙasa mai kururrumai ta zama sumul. Abubuwan da zan yi ke nan; ba zan yashe su ba.
17 Ils se retireront en arrière, ils seront couverts de honte, ceux qui mettent leur confiance en une image taillée, qui disent à une image de fonte: Vous êtes nos dieux.
Amma waɗanda suka dogara ga gumaka, waɗanda suke ce wa siffofi, ‘Ku ne allolinmu,’ za a mai da su baya da kunya.
18 Écoutez, sourds, et vous, aveugles, regardez pour voir.
“Ka ji, kai kurma; duba, kai makaho, ka kuma gani!
19 Qui est aveugle, si ce n’est mon serviteur, et sourd, comme mon messager que j’ai envoyé? Qui est aveugle comme celui en qui je me confie, et aveugle comme le serviteur de l’Éternel,
Wane ne makaho in ba bawana ba, da kuma kurma in ba ɗan aikan da na aika ba? Wane ne makaho kamar wanda ya miƙa kai gare ni, makaho kamar bawan Ubangiji?
20 pour voir bien des choses et ne pas y faire attention? Les oreilles ouvertes, il n’entend pas.
Kun ga abubuwa masu yawa, amma ba ku kula ba; kunnuwanku suna a buɗe, amma ba kwa jin wani abu.”
21 L’Éternel a pris plaisir [en lui] à cause de sa justice: il a rendu la loi grande et honorable.
Yakan gamsar da Ubangiji saboda adalcinsa ya sa dokarsa ta zama mai girma da kuma mai ɗaukaka.
22 Mais c’est ici un peuple pillé et dépouillé; ils sont tous liés dans des fosses, et ils sont cachés dans des prisons; ils sont devenus un butin, et il n’y a personne qui délivre, – une proie, et il n’y a personne qui dise: Restitue!
Amma ga mutanen da aka washe aka kuma kwashe ganima, an yi wa dukansu tarko a cikin rammuka ko kuma an ɓoye su cikin kurkuku. Sun zama ganima, babu wani da zai kuɓutar da su; an mai da su ganima, ba wanda zai ce, “Mayar da su.”
23 Qui parmi vous prêtera l’oreille à cela? Qui fera attention, et écoutera ce qui est à venir?
Wane ne a cikinku zai saurari wannan ko ya kasa kunne sosai a cikin kwanaki masu zuwa?
24 Qui a livré Jacob pour être une proie, et Israël à ceux qui le pillent? N’est-ce pas l’Éternel, celui contre qui nous avons péché? Et ils n’ont pas voulu marcher dans ses voies, et ils n’ont pas écouté sa loi;
Wa ya ba da Yaƙub don yă zama ganima Isra’ila kuma ga masu kwasar ganima? Ba Ubangiji ba ne, wanda kuka yi wa zunubi? Gama ba su bi hanyoyinsa ba; ba su yi biyayya da dokarsa ba.
25 et il a versé sur lui l’ardeur de sa colère et la force de la guerre: et elle l’a embrasé de tous côtés, et il ne l’a pas su; et elle l’a brûlé, et il ne l’a pas pris à cœur.
Saboda haka ya zuba musu zafin fushinsa, yaƙi mai tsanani. Ya rufe su cikin harsunan wuta, duk da haka ba su gane ba; ya cinye su, amma ba su koyi kome ba.

< Isaïe 42 >