< Isaïe 41 >

1 Faites silence devant moi, îles; et que les peuples renouvellent leur force! Qu’ils s’approchent; … alors, qu’ils parlent! Approchons ensemble en jugement!
“Ku yi shiru a gabana, ku tsibirai! Bari al’ummai su sabunta ƙarfinsu! Bari su zo gaba su yi magana; bari mu sadu a wurin shari’a.
2 Qui, du levant, réveilla [celui] dont la justice accompagne les pas? Il livra les nations devant lui, et lui soumit les rois; il les livra à son épée comme de la poussière, et à son arc comme du chaume chassé [par le vent].
“Wa ya zuga wannan daga gabas, yana kiransa cikin adalci ga yin hidima? Ya miƙa masa al’ummai ya kuma yi nasara da sarakuna a gabansa. Ya mai da su ƙura da takobinsa, zuwa inda iska ke hurawa ta wurin bugun da ya yi musu.
3 Il les poursuivit; il passa en sûreté par un chemin où il n’était pas allé de ses pieds.
Ya fafare su ya kuma yi tafiyarsa lafiya ƙalau, a hanyar da ƙafafunsa ba su taɓa bi ba.
4 Qui a opéré et fait [cela], appelant les générations dès le commencement? Moi, l’Éternel, le premier; et, avec les derniers, je suis le Même.
Wane ne ya taɓa yin haka ya kuma sa ya faru, yana kira ga tsararraki daga farko? Ni, Ubangiji ina can tun farkonsu ni kuma ina can har ƙarshe, Ni ne shi.”
5 Les îles le virent et eurent peur, les bouts de la terre tremblèrent: ils s’approchèrent et vinrent;
Tsibirai sun gan shi suka kuma ji tsoro; iyakokin duniya sun yi rawar jiki. Suka kusato suka kuma zo gaba;
6 ils s’entraidèrent l’un l’autre, et [chacun] dit à son frère: Sois fort.
kowa na taimakon wani yana ce wa ɗan’uwansa, “Ka ƙarfafa!”
7 Et l’ouvrier fortifiait le fondeur; celui qui polit au marteau [fortifiait] celui qui frappe sur l’enclume, disant de la soudure: Elle est bonne; … et il l’a affermi avec des clous, afin qu’il ne branle pas.
Masassaƙi yakan ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma shi mai gyara da guduma ya yi sumul yakan ƙarfafa mai harhaɗawa. Ya ce game da haɗin, “Ya yi kyau.” Yakan buga ƙusoshi su riƙe gunkin don kada yă fāɗi.
8 Et toi, Israël, mon serviteur, Jacob, que j’ai choisi, semence d’Abraham mon ami,
“Amma kai, ya Isra’ila, bawana, Yaƙub, wanda na zaɓa, zuriyar Ibrahim abokina,
9 toi que j’ai pris des bouts de la terre et appelé de ses extrémités, et à qui j’ai dit: Tu es mon serviteur, je t’ai choisi et je ne t’ai pas rejeté; …
na ɗauke ka daga iyakar duniya, daga kusurwoyi masu nesa na kira ka. Na ce, ‘Kai bawana ne’; na zaɓe ka ban kuwa ƙi ka ba.
10 ne crains point, car je suis avec toi; ne sois pas inquiet, car moi je suis ton Dieu. Je te fortifierai; oui, je t’aiderai; oui, je te soutiendrai par la droite de ma justice.
Saboda haka kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; kada ka karai, gama ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka in kuma taimake ka; zan riƙe ka da hannun damana mai adalci.
11 Voici, tous ceux qui s’irritent contre toi, seront honteux et confondus; ils seront comme un rien, et les hommes qui contestent contre toi périront.
“Duk wanda ya yi fushi da kai tabbatacce zai sha kunya da ƙasƙanci; waɗanda suka yi hamayya da kai za su zama kamar ba kome ba su kuma hallaka.
12 Tu les chercheras, et tu ne les trouveras pas, les hommes qui ont querelle avec toi; ils seront comme un rien et comme néant, les hommes qui te font la guerre.
Ko ka nemi abokan gābanka, ba za ka same su ba. Waɗanda suke yaƙi da kai za su zama kamar ba kome ba.
13 Car moi, l’Éternel, ton Dieu, je tiens ta droite, [moi] qui te dis: Ne crains point, moi je t’aiderai.
Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
14 Ne crains point, toi Jacob, vermisseau! [et vous], hommes d’Israël! Moi je t’aiderai, dit l’Éternel, et ton rédempteur, le Saint d’Israël.
Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub marar ƙarfi, ya ƙaramin Isra’ila, gama ni kaina zan taimake ka,” in ji Ubangiji, Mai Fansarka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
15 Voici, j’ai fait de toi un traîneau à battre, tranchant, neuf, à doubles dents: tu battras les montagnes et tu les réduiras en poussière, et tu rendras les collines comme de la balle;
“Duba, zan sa ka cikin abin sussuka, saboda kuma mai kaifi mai haƙora da yawa. Za ka yi sussukar duwatsu ka ragargaza su, ka kuma farfashe tuddai su zama kamar yayi.
16 tu les vanneras, et le vent les emportera, et le tourbillon les dispersera; et toi, tu t’égaieras en l’Éternel, tu te glorifieras dans le Saint d’Israël.
Za ka tankaɗe su, iska kuma ta kwashe su, guguwa kuma za tă warwatsa su. Amma za ka yi farin ciki a cikin Ubangiji ka kuma ɗaukaka a cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
17 Les affligés et les nécessiteux chercheront de l’eau, et il n’y en a pas, leur langue est desséchée par la soif: moi, l’Éternel, je leur répondrai, [moi], le Dieu d’Israël, je ne les abandonnerai pas.
“Matalauta da mabukata suna neman ruwa, amma babu kome; harsunansu sun bushe saboda ƙishi. Amma Ni Ubangiji zan amsa musu; Ni, Allah na Isra’ila, ba zan yashe su ba.
18 Je ferai couler des rivières sur les hauteurs, et des fontaines au milieu des vallées; je changerai le désert en un étang d’eau, et la terre aride en des sources jaillissantes.
Zan sa koguna su malalo a ƙeƙasassun tuddai, maɓulɓulan ruwa kuma a kwaruruka. Zan mai da hamada tafkunan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓulɓulan ruwa.
19 Je ferai croître dans le désert le cèdre, l’acacia, et le myrte, et l’olivier; je mettrai dans le lieu stérile le cyprès, le pin et le buis ensemble;
Zan sa a hamada ta tsiro da al’ul da itacen ƙirya, da itacen ci-zaƙi, da zaitun. Zan sa itace mai girma a ƙasashe masu sanyi ya tsiro a ƙeƙasasshiyar ƙasa, tare da fir da kuma saifires,
20 afin qu’ils voient, et qu’ils sachent, et qu’ils considèrent, et qu’ils comprennent tous ensemble, que la main de l’Éternel a fait cela, et que le Saint d’Israël l’a créé.
don mutane su gani su kuma sani, su lura su kuma fahimci, cewa hannun Ubangiji ne ya aikata haka, cewa Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya sa abin ya faru.
21 Produisez votre cause, dit l’Éternel; apportez ici vos arguments, dit le roi de Jacob.
“Ka gabatar da damuwarka,” in ji Ubangiji. “Ka kawo gardandaminka,” in ji Sarki na Yaƙub.
22 Qu’ils les apportent, et qu’ils nous déclarent ce qui arrivera. Déclarez les premières choses, ce qu’elles sont, afin que nous [y] fassions attention, et que nous en connaissions le résultat; ou faites-nous savoir celles qui viendront;
“Ka shigar da gumakanka don su faɗa mana abin da zai faru. Faɗa mana abubuwan da suka riga suka faru, domin mu lura da su mu kuma san abin da zai faru a ƙarshe. Ko kuwa ku furta mana abubuwan da za su faru,
23 – déclarez les choses qui vont arriver dans la suite, et nous saurons que vous êtes des dieux; oui, faites du bien et faites du mal, afin que nous le considérions et le voyions ensemble.
faɗa mana abin da nan gaba ta ƙunsa, don mu san cewa ku alloli ne. Ku yi wani abu, mai kyau ko mummuna, don mu ji tsoro da fargaba.
24 Voici, vous êtes moins que rien, et votre œuvre est du néant: qui vous choisit est une abomination…
Amma ku ba kome ba ne kuma ayyukanku banza da wofi ne; duk wanda ya zaɓe ku abin ƙyama ne.
25 Je l’ai réveillé du nord, et il vient, – du lever du soleil, celui qui invoquera mon nom. Et il marchera sur les princes comme sur de la boue, et comme le potier foule l’argile.
“Na zuga wani daga arewa, ya kuwa zo, wani daga inda rana ke fitowa wanda yake kira bisa sunana. Yana takawa a kan masu mulki kamar da taɓarya, sai ka ce maginin tukwane yana taka laka.
26 Qui l’a déclaré dès le commencement, afin que nous le sachions, et d’avance, afin que nous disions: C’est juste? Non, il n’y a personne qui le déclare; non, personne qui le fasse entendre; non, personne qui entende vos paroles.
Wa ya faɗi wannan tun daga farko, don mu sani, ko kafin ya faru, don mu ce, ‘Ya faɗi daidai’? Ba wanda ya faɗa wannan, ba wanda ya riga faɗe shi, ba wanda ya ji wata magana daga gare ku.
27 Le premier, [j’ai dit] à Sion: Voici, les voici! et à Jérusalem: Je donnerai un messager de bonnes nouvelles!
Ni ne na farkon da ya ce wa Sihiyona, ‘Duba, ga su nan!’ Na ba wa Urushalima saƙon labari mai daɗi.
28 Et j’ai regardé, et il n’y avait personne – même parmi eux – et point de conseiller, pour leur demander, et avoir d’eux une réponse.
Na duba amma ba kowa ba wani a cikinsu da zai ba da shawara, ba wani da zai ba da amsa sa’ad da na tambaye su.
29 Voici, tous sont la vanité, leurs œuvres sont un néant, leurs images de fonte sont le vent et le vide.
Duba, dukansu masu ƙarya ne! Ayyukansu ba su da riba; siffofinsu iska ne kawai da ruɗami.

< Isaïe 41 >