< Isaïe 3 >

1 Car voici, le Seigneur, l’Éternel des armées, ôte de Jérusalem et de Juda le soutien et l’appui, tout soutien de pain et tout soutien d’eau,
Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
2 l’homme fort et l’homme de guerre, le juge et le prophète, le devin et l’ancien,
jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
3 le chef de cinquantaine, et l’homme considéré, et le conseiller, et l’habile ouvrier, et celui qui s’entend aux enchantements.
shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
4 Et je leur donnerai des jeunes gens pour être leurs princes, et de petits enfants domineront sur eux;
“Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
5 et le peuple sera opprimé, l’homme par l’homme, et chacun par son voisin; le jeune garçon usera d’insolence contre le vieillard, et l’homme de néant contre l’homme honorable.
Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
6 Alors, si un homme saisit son frère, dans la maison de son père, [disant]: Tu as un manteau, tu seras notre chef, et cette ruine sera sous ta main,
Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
7 il jurera en ce jour-là, disant: Je ne puis être un médecin, et dans ma maison il n’y a pas de pain et il n’y a pas de manteau; vous ne me ferez pas chef du peuple.
Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
8 Car Jérusalem bronche, et Juda tombe; parce que leur langue et leurs actions sont contre l’Éternel, pour braver les yeux de sa gloire.
Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
9 L’aspect de leur visage témoigne contre eux, et ils annoncent leur péché comme Sodome; ils ne le cachent pas. Malheur à leur âme! car ils ont fait venir le mal sur eux-mêmes.
Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
10 Dites au juste que le bien [lui arrivera], car ils mangeront le fruit de leurs actions.
Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
11 Malheur au méchant! [il lui arrivera] du mal, car l’œuvre de ses mains lui sera rendue.
Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
12 Quant à mon peuple, des enfants l’oppriment, et des femmes le gouvernent. Mon peuple! ceux qui te conduisent te fourvoient, et détruisent le chemin de tes sentiers.
Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
13 L’Éternel se tient là pour plaider, et il est debout pour juger les peuples.
Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
14 L’Éternel entrera en jugement avec les anciens de son peuple et avec ses princes, [disant]: Et vous, vous avez brouté la vigne; la dépouille du pauvre est dans vos maisons.
Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
15 Qu’avez-vous à faire de fouler mon peuple, et de broyer la face des pauvres? dit le Seigneur, l’Éternel des armées.
Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
16 Et l’Éternel dit: Parce que les filles de Sion sont hautaines, et qu’elles marchent le cou tendu et les regards pleins de convoitise, et qu’elles marchent allant à petits pas, faisant résonner leurs pieds,
Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
17 le Seigneur rendra chauve le sommet de la tête des filles de Sion, et l’Éternel exposera leur nudité.
Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
18 En ce jour-là, le Seigneur ôtera l’ornement des anneaux de pieds, et les petits soleils, et les petites lunes;
A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
19 les pendeloques de perles, et les bracelets, et les voiles;
’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
20 les diadèmes, et les chaînettes des pieds, et les ceintures, et les boîtes de senteur, et les amulettes;
kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
21 les bagues, et les anneaux de nez;
da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
22 les vêtements de fête, et les tuniques, et les manteaux, et les bourses;
tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
23 et les miroirs, et les chemises, et les turbans, et les voiles de gaze.
da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
24 Et il arrivera qu’au lieu de parfum il y aura pourriture; et au lieu de ceinture, une corde; et au lieu de cheveux artistement tressés, une tête chauve; et au lieu d’une robe d’apparat, un sarrau de toile à sac; flétrissure, au lieu de beauté. –
A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
25 Tes hommes tomberont par l’épée, et tes hommes forts, dans la guerre.
Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
26 Et ses portes se lamenteront et mèneront deuil; et, désolée, elle s’assiéra sur la terre.
Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.

< Isaïe 3 >