< Isaïe 29 >

1 Malheur à Ariel, à Ariel, la cité où David demeura! Ajoutez année à année, que les fêtes se succèdent;
Kaitonki, Ariyel, Ariyel birnin da Dawuda ya zauna! Ƙara shekara ga shekara a kuma bar shagulgulanki su yi ta kewayewa.
2 mais j’enserrerai Ariel; et il y aura soupir et gémissement; et elle me sera comme un Ariel.
Duk da haka zan yi wa Ariyel kwanto za tă kuma yi kuka da makoki, za tă zama mini kamar bagaden jini.
3 Et je camperai comme un cercle contre toi, et je t’assiégerai au moyen de postes [armés], et j’élèverai contre toi des forts;
Zan kafa sansani kewaye da ke duka; zan kewaye ki da hasumiyoyi in tasar miki da ayyukan kwantona na yaƙi.
4 et, humiliée, tu parleras depuis la terre, et ta parole sortira sourdement de la poussière, et ta voix, sortant de la terre, sera comme celle d’un évocateur d’esprits; et ta parole s’élèvera de la poussière comme un murmure.
Za a ƙasƙantar da ke, za ki ƙi yin magana daga ƙasa; maganarki za tă yi ƙasa-ƙasa daga ƙura. Muryarki za tă zama kamar fatalwa daga ƙasa; daga ƙura maganarki zai fito ƙasa-ƙasa.
5 Et la multitude de tes ennemis sera comme une fine poussière, et la multitude des hommes terribles comme la balle menue qui passe; et [cela] arrivera en un moment, subitement.
Amma abokan gābanki masu yawa za su zama kamar ƙura mai laushi, sojojinsu masu firgitarwa za su yi ta tashi kamar yayin da iska ta hura. Farat ɗaya, cikin ɗan lokaci,
6 Tu seras visitée de par l’Éternel des armées avec tonnerre et tremblement de terre et une grande voix, avec tourbillon et tempête, et une flamme de feu dévorant.
Ubangiji Maɗaukaki zai zo da tsawa da rawar ƙasa da ƙara mai girma, da hadarin iska da guguwa da harshe na wuta mai ci.
7 Et la multitude de toutes les nations qui font la guerre à Ariel, et tous ceux qui combattent contre elle et contre ses remparts, et qui l’enserrent, seront comme un songe d’une vision de nuit.
Sa’an nan sojojin dukan al’umman da suka yi yaƙi da Ariyel, da suka fāɗa mata da kagararta suka kuma yi mata kwanto, za su zama kamar yadda yake da mafarki, wahayi da dare,
8 Et ce sera comme celui qui rêve ayant faim, et voici, il mange, et il se réveille, et son âme est vide, – et comme celui qui rêve ayant soif, et voici, il boit, et il se réveille, et voici, il est las et son âme est altérée: ainsi il arrivera à la multitude de toutes les nations qui font la guerre contre la montagne de Sion.
kamar sa’ad da mai yunwa yana mafarki cewa yana cin abinci, amma sai ya farka, yunwan tana nan; kamar sa’ad da mai ƙishirwa yana mafarki cewa yana shan ruwa, amma sai ya farka yana suma, da ƙishinsa. Haka zai zama da sojoji na dukan al’ummai da suka yi yaƙi da Dutsen Sihiyona.
9 Soyez étonnés et soyez stupéfaits! aveuglez-vous et soyez aveugles! Ils sont enivrés, mais non de vin; ils chancellent, mais non par la boisson forte.
Ku firgita ku kuma yi mamaki, ku makance kanku ku kuma zama a makance; ku bugu, amma ba da ruwan inabi ba, ku yi tangaɗi, amma ba daga barasa ba.
10 Car l’Éternel a répandu sur vous un esprit de profond sommeil; il a bandé vos yeux; les prophètes et vos chefs, les voyants, il les a couverts.
Ubangiji ya kawo muku barci mai nauyi, Ya rufe idanunku (annabawa); ya rufe kawunanku (masu duba).
11 Et la vision de tout vous sera comme les paroles d’un livre scellé qu’on donne à quelqu’un qui sait lire, en disant: Lis ceci, je te prie; et il dit: Je ne puis, car il est scellé;
Gare ku duk wannan wahayi ba kome ba ne sai dai maganganun da aka rufe a cikin littafi. In kuma kun ba da littafin ga wani wanda zai iya karanta, kuka kuma ce masa, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ba zan iya ba; an rufe shi.”
12 et on donne le livre à celui qui ne sait pas lire, en disant: Lis ceci, je te prie; et il dit: Je ne sais pas lire.
Ko kuwa in kun ba da littafin ga wani wanda ba zai iya karantawa ba, kuka kuma ce, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ban iya karatu ba.”
13 Et le Seigneur dit: Parce que ce peuple s’approche de moi de sa bouche, et qu’ils m’honorent de leurs lèvres, et que leur cœur est éloigné de moi, et que leur crainte de moi est un commandement d’hommes enseigné,
Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane sun zo kusa da ni da bakinsu suka kuma girmama ni da leɓunansu, amma zukatansu suna nesa daga gare ni. Sujadar da suke mini cike take da dokokin da mutane suka koyar.
14 c’est pourquoi, voici, j’agirai encore merveilleusement, et je ferai une œuvre merveilleuse envers ce peuple: la sagesse de ses sages périra, et l’intelligence de ses intelligents se cachera.
Saboda haka zan firgita waɗannan mutane sau ɗaya da abubuwan banmamaki a kan abubuwan banmamaki; hikimar masu hikima za tă lalace, azancin masu azanci zai ɓace.”
15 Malheur à ceux qui cachent profond, loin de l’Éternel, [leur] conseil, et dont les actions sont dans les ténèbres, et qui disent: Qui nous voit, et qui nous connaît?
Kaiton waɗanda suke zuwa manyan zurfafa don su ɓoye shirye-shiryensu daga Ubangiji, waɗanda suke aikinsu cikin duhu su yi tunani, “Wa yake ganinmu? Wa zai sani?”
16 Vos perversités!… Le potier sera-t-il estimé comme l’argile, pour que la chose faite dise de celui qui l’a faite: Il ne m’a pas faite? et que ce qui est formé dise de celui qui l’a formé: Il n’a pas d’intelligence?
Kuna birkitar abubuwa, sai ka ce an mayar da mai ginin tukwane ya zama yumɓu! Abin da aka yi zai ce wa wanda ya yi shi, “Ba shi ne ya yi ni ba”? Tukunya za tă iya ce wa mai ginin tukwane, “Ba ka san kome ba”?
17 N’y a-t-il pas encore très peu de temps, et le Liban sera converti en un champ fertile, et le champ fertile sera réputé une forêt?
Cikin ɗan lokaci, za a mai da Lebanon gona mai taƙi kuma gona mai taƙi za tă zama kamar kurmi?
18 Et en ce jour-là les sourds entendront les paroles du livre, et les yeux des aveugles, [délivrés] de l’obscurité et des ténèbres, verront;
A wannan rana kurame za su ji maganganun littafi, daga duruduru da duhu kuma idanun makafi za su gani.
19 et les débonnaires augmenteront leur joie en l’Éternel, et les pauvres d’entre les hommes s’égaieront dans le Saint d’Israël.
Masu tawali’u za su sāke yin farin ciki a cikin Ubangiji; mabukata za su yi farin ciki cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
20 Car l’homme violent ne sera plus, et le moqueur aura pris fin; et tous ceux qui veillent pour l’iniquité seront retranchés,
Masu zalunci za su ƙare, masu ba’a za su ɓace, kuma dukan waɗanda suke da ido don mugunta za su hallaka,
21 [ceux] qui tiennent un homme coupable pour un mot, qui tendent des pièges à ceux qui reprennent à la porte, et qui font fléchir [le droit] du juste par des choses futiles.
waɗanda ta magana kawai sukan mai da mutum mai laifi, waɗanda suke kafa tarko wa mai ba da kāriya a ɗakin shari’a da shaidar ƙarya kuma su hana marar laifi samun shari’ar adalci.
22 C’est pourquoi, ainsi dit à la maison de Jacob l’Éternel qui racheta Abraham: Maintenant Jacob ne sera plus honteux, et maintenant sa face ne sera plus pâle;
Saboda haka ga abin da Ubangiji wanda ya fanshi Ibrahim, ya ce wa gidan Yaƙub, “Ba za a ƙara kunyata Yaƙub ba; fuskokinsu kuma ba za su ƙara yanƙwanewa ba.
23 car quand il verra ses enfants, l’œuvre de mes mains au milieu de lui, ils sanctifieront mon nom, et ils sanctifieront le Saint de Jacob, et ils craindront le Dieu d’Israël;
Sa’ad da suka ga’ya’yansu a tsakiyarsu, aikin hannuwansu, za su kiyaye sunana da tsarki; za su san tsarkin Mai Tsarkin nan na Yaƙub, za su kuma ji tsoron Allah na Isra’ila.
24 et ceux qui errent en esprit auront de l’intelligence, et les désobéissants apprendront la bonne doctrine.
Su da suke marasa azanci a ruhu za su sami fahimtar; waɗanda suke gunaguni za su yarda da koyarwa.”

< Isaïe 29 >