< Isaïe 19 >

1 L’oracle touchant l’Égypte. Voici, l’Éternel, porté sur une nuée rapide, vient en Égypte, et les idoles de l’Égypte sont agitées à cause de sa présence, et le cœur de l’Égypte se fond au-dedans d’elle.
Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
2 Et j’exciterai l’Égyptien contre l’Égyptien; et ils feront la guerre chacun contre son frère et chacun contre son compagnon, ville contre ville, royaume contre royaume.
“Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
3 Et l’esprit de l’Égypte s’en ira, au milieu d’elle, et je détruirai son conseil; et ils s’enquerront auprès des idoles, et auprès des nécromanciens et des évocateurs d’esprits et des diseurs de bonne aventure.
Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
4 Et je livrerai l’Égypte en la main d’un seigneur dur, et un roi cruel dominera sur eux, dit le Seigneur, l’Éternel des armées.
Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
5 Et les eaux manqueront à la mer, et la rivière tarira et se desséchera,
Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
6 et les rivières deviendront puantes; les fleuves de l’Égypte seront diminués et tariront, les roseaux et les joncs se flétriront.
Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
7 Les prairies sur le Nil, sur le bord du Nil, et tout ce qui est ensemencé le long du Nil, [tout] se desséchera, se réduira en poussière et ne sera plus.
haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
8 Et les pêcheurs gémiront; et tous ceux qui jettent un hameçon dans le Nil mèneront deuil, et ceux qui étendent un filet sur la face des eaux languiront.
Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
9 Et ceux qui travaillent le lin peigné seront honteux, et ceux qui tissent le coton.
Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
10 Et les colonnes [du pays] sont brisées; tous ceux qui gagnent un salaire ont l’âme attristée.
Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
11 Ils ne sont que des fous, les princes de Tsoan, les sages conseillers du Pharaon; [leur] conseil est devenu stupide. Comment dites-vous au Pharaon: Je suis un fils des sages, le fils d’anciens rois?
Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
12 Où sont-ils donc, tes sages? Qu’ils te déclarent, je te prie, et te fassent savoir ce que l’Éternel des armées a résolu contre l’Égypte.
Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
13 Les princes de Tsoan sont devenus fous, les princes de Noph sont trompés, et les chefs de ses tribus ont fait errer l’Égypte;
Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
14 l’Éternel a versé au milieu d’elle un esprit de perversité; et ils ont fait errer l’Égypte dans tout ce qu’elle fait, comme chancelle dans son vomissement celui qui est ivre;
Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
15 et il n’y aura pas pour l’Égypte une œuvre que puisse faire tête ou queue, branche de palmier ou jonc.
Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
16 En ce jour-là, l’Égypte sera comme des femmes; et elle tremblera et aura peur devant le secouement de la main de l’Éternel des armées, qu’il secoue contre elle.
A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
17 Et la terre de Juda sera pour l’Égypte une terreur: quiconque se la rappellera aura peur, à cause du conseil de l’Éternel des armées, que, lui, il a pris contre elle.
Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
18 En ce jour-là, il y aura cinq villes dans le pays d’Égypte qui parleront la langue de Canaan et jureront par l’Éternel des armées; l’une sera appelée Ir-ha-Hérès.
A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
19 En ce jour-là, il y aura un autel [élevé] à l’Éternel au milieu du pays d’Égypte, et, à la frontière même, une colonne [dédiée] à l’Éternel;
A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
20 et ce sera un signe et un témoignage à l’Éternel des armées dans le pays d’Égypte. Car ils crieront à l’Éternel à cause des oppresseurs, et il leur enverra un sauveur et un défenseur, et il les délivrera.
Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
21 Et l’Éternel se fera connaître des Égyptiens, et les Égyptiens connaîtront l’Éternel, en ce jour-là; et ils serviront avec un sacrifice et une offrande, et ils voueront un vœu à l’Éternel et l’accompliront.
Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
22 Et l’Éternel frappera l’Égypte; il frappera, et il guérira; et ils se tourneront vers l’Éternel, et il leur sera propice et les guérira.
Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
23 En ce jour-là, il y aura un chemin battu de l’Égypte à l’Assyrie; et l’Assyrie viendra en Égypte, et l’Égypte en Assyrie; et l’Égypte servira avec l’Assyrie.
A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
24 En ce jour-là, Israël sera le troisième, avec l’Égypte et avec l’Assyrie, une bénédiction au milieu de la terre;
A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
25 car l’Éternel des armées le bénira, disant: Béni soit l’Égypte, mon peuple, et l’Assyrie, l’ouvrage de mes mains, et Israël, mon héritage.
Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”

< Isaïe 19 >