< Osée 10 >

1 Israël est une vigne branchue; il porte du fruit pour lui-même. Selon l’abondance de son fruit, il a multiplié les autels; selon la beauté de son pays, il a rendu belles ses statues.
Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
2 Leur cœur est flatteur; maintenant ils seront tenus pour coupables. Il abattra leurs autels, il détruira leurs statues;
Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
3 car maintenant ils diront: Nous n’avons pas de roi, car nous n’avons pas craint l’Éternel; et un roi, que ferait-il pour nous?
Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
4 Ils prononcent des paroles, ils jurent faussement, [et] ils concluent une alliance; aussi le jugement poussera comme une plante vénéneuse dans les sillons des champs.
Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
5 L’habitant de Samarie a peur pour le veau de Beth-Aven; car son peuple mènera deuil sur lui, et ses Camarim trembleront à cause de lui, pour sa gloire, car elle a été transportée d’auprès de lui;
Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
6 on le porte à l’Assyrie, comme présent au roi Jareb. Éphraïm est saisi de honte, et Israël aura honte de son conseil.
Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
7 Samarie [est détruite], son roi a péri, comme un fétu sur la face des eaux;
Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
8 et les hauts lieux d’Aven, le péché d’Israël, seront détruits. L’épine et la ronce monteront sur leurs autels; et ils diront aux montagnes: Couvrez-nous! et aux collines: Tombez sur nous!
Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
9 Dès les jours de Guibha, tu as péché, Israël: là ils sont restés; la guerre contre les fils d’iniquité ne les atteignit pas à Guibha.
“Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
10 Selon mon bon plaisir, je les châtierai; et les peuples seront rassemblés contre eux, quand ils seront liés pour leurs deux iniquités.
Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
11 Et Éphraïm est une génisse dressée, qui aime à fouler le blé; et j’ai passé sur son beau cou: je ferai tirer le chariot à Éphraïm; Juda labourera, et Jacob hersera.
Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
12 Semez pour vous en justice, moissonnez selon la piété. Défrichez pour vous un terrain neuf; [c’est] le temps pour chercher l’Éternel, jusqu’à ce qu’il vienne et qu’il fasse pleuvoir sur vous la justice.
Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
13 Vous avez labouré la méchanceté, moissonné l’iniquité, mangé le fruit du mensonge; car tu as eu confiance en ta voie, en la multitude de tes hommes forts.
Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
14 Et un tumulte s’élèvera parmi tes peuples, et toutes tes forteresses seront détruites, comme Shalman détruisit Beth-Arbel, au jour de la guerre: la mère fut écrasée avec les fils.
hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
15 Béthel vous fera de même, à cause de la méchanceté de votre méchanceté: à l’aube du jour, le roi d’Israël aura entièrement cessé d’être.
Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.

< Osée 10 >