< Habacuc 3 >

1 Prière de Habakuk, le prophète. Sur Shiguionoth.
Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
2 Ô Éternel, j’ai entendu ce que tu as déclaré, [et] j’ai eu peur. Éternel, ravive ton œuvre au milieu des années; au milieu des années, fais-la connaître. Dans la colère, souviens-toi de la miséricorde!
Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
3 Dieu vint de Théman, et le Saint, de la montagne de Paran. (Sélah) Sa magnificence couvre les cieux, et sa louange remplit la terre;
Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
4 Et sa splendeur était comme la lumière: des rayons lui jaillissaient de la main; et là se cachait sa force.
Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
5 La peste marchait devant lui, et une flamme ardente sortait sous ses pas.
Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
6 Il se tint là et mesura la terre, il regarda et mit en déroute les nations; Et les montagnes antiques furent brisées en éclats, les collines éternelles s’affaissèrent. Ses voies sont éternelles.
Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
7 Je vis les tentes de Cushan dans l’affliction; les tentures du pays de Madian tremblèrent.
Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
8 Est-ce contre les rivières que s’irrita l’Éternel? ou contre les rivières que fut ta colère? contre la mer, ta fureur, que tu sois monté sur tes chevaux, [sur] tes chars de salut?
Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
9 Ton arc était mis à nu, … les verges [de jugement] jurées par [ta] parole. (Sélah) Tu fendis la terre par des rivières.
Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
10 Les montagnes te virent, elles tremblèrent; des torrents d’eau passèrent, l’abîme fit retentir sa voix; il leva ses mains en haut.
duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
11 Le soleil, la lune, s’arrêtèrent dans leur demeure à la lumière de tes flèches qui volaient, à la splendeur de l’éclair de ta lance.
Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
12 Tu parcourus le pays avec indignation, tu foulas les nations avec colère.
Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
13 Tu sortis pour le salut de ton peuple, pour le salut de ton oint; tu brisas le faîte de la maison du méchant, mettant à nu les fondements jusqu’au cou. (Sélah)
Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
14 Tu transperças de ses propres traits la tête de ses chefs: ils arrivaient comme un tourbillon pour me disperser, leur joie était comme de dévorer l’affligé en secret.
Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
15 Tu traversas la mer avec tes chevaux, l’amas de grandes eaux.
Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
16 J’entendis, et mes entrailles tremblèrent; à la voix [que j’entendis] mes lèvres frémirent, la pourriture entra dans mes os, et je tremblai sous moi-même, pour que j’aie du repos au jour de la détresse, quand montera contre le peuple celui qui l’assaillira.
Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
17 Car le figuier ne fleurira pas, et il n’y aura point de produit dans les vignes; le travail de l’olivier mentira, et les campagnes ne produiront pas de nourriture; les brebis manqueront dans le parc, et il n’y aura pas de bœufs dans les étables;
Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
18 Mais moi, je me réjouirai en l’Éternel, je m’égaierai dans le Dieu de mon salut.
duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
19 L’Éternel, le Seigneur, est ma force; il rendra mes pieds pareils à ceux des biches, et il me fera marcher sur mes lieux élevés. Au chef de musique. Sur Neguinoth.
Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi. Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata.

< Habacuc 3 >