< Genèse 41 >

1 Et il arriva, au bout de deux années révolues, que le Pharaon songea, et voici, il se tenait près du fleuve:
Bayan shekaru biyu cif, Fir’auna ya yi mafarki. A mafarkin, ya ga yana tsaye kusa da Nilu,
2 et voici, du fleuve montaient sept vaches, belles à voir, et grasses de chair, et elles paissaient dans les roseaux.
sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
3 Et voici, après elles, sept autres vaches montaient du fleuve, laides à voir, et pauvres de chair; et elles se tinrent à côté des vaches qui étaient sur le bord du fleuve;
Bayansu, sai ga waɗansu shanu bakwai, munana, ramammu, suka fito daga Nilu, suka tsaya kusa da waɗancan masu ƙiban, a bakin kogin.
4 et les vaches laides à voir, et pauvres de chair, mangèrent les sept vaches belles à voir, et grasses. Et le Pharaon s’éveilla.
Shanun nan da suke munana ramammu, suka cinye shanu bakwai nan masu ƙiba mulmul. Sai Fir’auna ya farka.
5 Et il s’endormit, et songea une seconde fois: et voici, sept épis gras et bons montaient sur une seule tige.
Ya sāke yin barci, sai ya yi mafarki na biyu; ya ga kawuna bakwai na dawa, ƙosassu masu kyau, suka yi girma a kara guda.
6 Et voici, sept épis pauvres et brûlés par le vent d’orient germaient après eux;
Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai na dawa, suka fito sirara waɗanda iskar gabas ta sa suka yanƙwane.
7 et les épis pauvres dévorèrent les sept épis gras et pleins. Et le Pharaon s’éveilla; et voilà, [c’était] un songe.
Siraran dawan suka haɗiye kawuna bakwai nan ƙosassu masu kyau. Sai Fir’auna ya farka, ashe, mafarki ne.
8 Et il arriva, au matin, que son esprit fut troublé; et il envoya, et appela tous les devins de l’Égypte, et tous ses sages. Et le Pharaon leur raconta ses songes; et il n’y eut personne qui les interprète au Pharaon.
Da safe sai hankalinsa ya tashi, saboda haka sai ya aika a kawo dukan masu duba da masu hikima na Masar. Fir’auna ya faɗa musu mafarkansa, amma babu wanda ya iya ba shi fassararsu.
9 Et le chef des échansons parla au Pharaon, disant: Je rappelle aujourd’hui mes fautes.
Sai shugaban masu shayarwa ya ce wa Fir’auna, “Yau an tuna mini da kāsawata.
10 Le Pharaon fut irrité contre ses serviteurs, et me mit sous garde, moi et le chef des panetiers, dans la maison du chef des gardes;
Sai ya ci gaba ya ce, Fir’auna ya taɓa husata da bayinsa, ya kuma jefa ni da shugaban masu tuya a cikin kurkuku a gidan shugaban masu tsaro.
11 et nous avons songé un songe dans une même nuit, moi et lui; nous avons songé chacun selon l’interprétation de son songe.
Kowannenmu ya yi mafarki a wani dare, kowane mafarki kuma ya kasance da ma’anarsa.
12 Et il y avait là avec nous un jeune hébreu, serviteur du chef des gardes; et nous lui avons raconté, et il nous interpréta nos songes; il donna à chacun l’interprétation selon son songe.
To, wani saurayi, mutumin Ibraniyawa ya kasance a can tare da mu, bawan shugaban masu tsaro. Sai muka faɗa masa mafarkanmu, ya kuwa fassara mana su, yana ba wa kowane mutum fassarar mafarkinsa.
13 Et il arriva que, comme il nous avait interprété, ainsi il advint: moi, [le Pharaon] me rétablit dans mon poste, et lui, il le pendit.
Abubuwan kuwa suka kasance daidai yadda ya fassara su gare mu; aka mai da ni a matsayina, ɗaya mutumin kuwa aka rataye shi.”
14 Et le Pharaon envoya, et appela Joseph; et on le fit accourir de la fosse, et il se rasa, et changea de vêtements; et il vint vers le Pharaon.
Sai Fir’auna ya aika a kawo Yusuf, aka kuwa kawo shi da sauri daga kurkuku. Sa’ad da ya yi aski, ya kuma canja tufafinsa, sai ya zo gaban Fir’auna.
15 Et le Pharaon dit à Joseph: J’ai songé un songe, et il n’y a personne pour l’interpréter; et j’ai entendu dire de toi que tu comprends un songe pour l’interpréter.
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Na yi mafarki, kuma babu wanda ya iya fassara shi. Amma na ji an ce sa’ad da ka ji mafarki, kana iya fassara shi.”
16 Et Joseph répondit au Pharaon, disant: Cela n’est pas à moi; Dieu donnera une réponse de paix au Pharaon.
Yusuf ya amsa wa Fir’auna ya ce, “Ba ni ne da iyawar ba, Allah zai iya ba wa Fir’auna amsar da yake nema.”
17 Et le Pharaon dit à Joseph: Dans mon songe, voici, je me tenais sur le bord du fleuve;
Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “A cikin mafarkina, na ga ina tsaye a bakin Nilu,
18 et voici, du fleuve montaient sept vaches grasses de chair, et belles à voir, et elles paissaient dans les roseaux.
sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
19 Et voici, sept autres vaches montaient après elles, chétives, et très laides à voir, et maigres de chair: je n’en ai pas vu de semblables en laideur dans tout le pays d’Égypte.
Bayansu kuma, sai ga waɗansu shanu bakwai suka fito ƙanjamammu, munana, ramammu. Ban taɓa ganin irin munanan shanu haka a cikin dukan ƙasar Masar ba.
20 Et les vaches maigres et laides mangèrent les sept premières vaches, les grasses:
Ramammun shanun nan munana, suka cinye shanun nan bakwai masu ƙiba da suka fito da fari.
21 elles entrèrent dans leur ventre, et il ne paraissait point qu’elles soient entrées dans leur ventre, et leur aspect était aussi laid qu’au commencement. Et je m’éveillai.
Amma ko bayan da suka cinye su, babu wanda zai iya faɗa cewa sun yi haka; suna nan dai munana kamar yadda suke a dā. Sai na farka.
22 Et je vis dans mon songe; et voici, sept épis montaient sur une seule tige, pleins et bons;
“Har yanzu kuma, a cikin mafarkina na ga kawuna bakwai na dawa ƙosassu masu kyau, suna girma a kara guda.
23 et voici, sept épis desséchés, pauvres, brûlés par le vent d’orient, germaient après eux;
Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai suka fito, yanƙwananne sirara waɗanda iskar gabas ta yanƙwane.
24 et les épis pauvres dévorèrent les sept bons épis. Et je l’ai dit aux devins; et il n’y a eu personne qui me l’explique.
Siraran kawunan dawan nan suka haɗiye kawuna bakwai nan masu kyau. Na faɗa wannan wa masu duba, amma ba wanda ya iya fassara mini shi.”
25 Et Joseph dit au Pharaon: Le songe du Pharaon est un: Dieu a déclaré au Pharaon ce qu’il va faire.
Sai Yusuf ya ce wa Fir’auna, “Mafarkan Fir’auna, ɗaya ne. Allah ya bayyana wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
26 Les sept bonnes vaches, ce sont sept années; et les sept bons épis, ce sont sept années: c’est un seul songe.
Shanu masu kyau nan, shekaru bakwai ne, kawunan dawa bakwai ƙosassun nan kuwa shekaru bakwai ne; mafarkan iri ɗaya ne.
27 Et les sept vaches maigres et laides qui montaient après elles, ce sont sept années; et les sept épis vides, brûlés par le vent d’orient, ce sont sept années de famine.
Shanun nan ramammu, munana, da suka zo daga baya, shekaru bakwai ne, haka ma kawuna dawan nan shanyayyu da iskar gabas ta yanƙwane. Shekaru ne bakwai na yunwa.
28 C’est la parole que je dis au Pharaon; ce que Dieu va faire, il le montre au Pharaon.
“Haka yake kamar yadda na faɗa wa Fir’auna cewa Allah ya nuna wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
29 Voici, sept années de grande abondance viennent dans tout le pays d’Égypte;
Shekaru bakwai na yalwar abinci suna zuwa a dukan ƙasar Masar,
30 et sept années de famine se lèveront après elles; et toute l’abondance sera oubliée dans le pays d’Égypte, et la famine consumera le pays;
amma shekaru bakwai na yunwa za su biyo bayansu. Tsananin yunwar za tă sa a manta da dukan isashen abincin da aka samu a ƙasar Masar, yunwa kuwa za tă rufe dukan ƙasar.
31 et l’abondance ne sera plus connue dans le pays, à cause de cette famine [qui viendra] après; car elle sera très intense.
Ba za a tuna da isashen abincin da aka samu a ƙasar ba, domin yunwar da za tă biyo baya za tă zama da tsanani ƙwarai.
32 Et que le songe ait été répété deux fois au Pharaon, c’est que la chose est arrêtée de la part de Dieu, et que Dieu se hâte de la faire.
Dalilin da aka ba wa Fir’auna mafarkan nan kashi biyu kuwa shi ne cewa Allah ya riga ya ƙaddara al’amarin. Allah zai aikata shi, ba da daɗewa ba.
33 Et maintenant, que le Pharaon se cherche un homme intelligent et sage, et qu’il l’établisse sur le pays d’Égypte.
“Yanzu fa, bari Fir’auna yă nemi mutum mai basira da kuma hikima, yă sa shi yă shugabanci ƙasar Masar.
34 Que le Pharaon fasse [cela], et qu’il prépose des commissaires sur le pays, et qu’il lève le cinquième du pays d’Égypte pendant les sept années d’abondance;
Bari Fir’auna yă naɗa komishinoni a kan ƙasar don su karɓi kashi ɗaya bisa biyar na girbin Masar a lokacin shekaru bakwai na yalwar abinci.
35 et qu’ils rassemblent tous les vivres de ces bonnes années qui viennent, et qu’ils amassent le blé sous la main du Pharaon pour nourriture dans les villes, et qu’ils le gardent.
Ya kamata su tara dukan abincin waɗannan shekaru masu kyau da suke zuwa, su yi ajiyar hatsin a ƙarƙashin ikon Fir’auna, don a ajiye a birane don abinci.
36 Et les vivres seront une réserve pour le pays, pour les sept années de famine qui seront dans le pays d’Égypte, et le pays ne sera pas détruit par la famine.
Ya kamata a adana abincin nan don ƙasar, kāriya shekaru bakwai na yunwa, domin a yi amfani da shi a lokacin shekarun yunwan da za su zo wa Masar, saboda kada ƙasar ta lalace da yunwa.”
37 Et la chose fut bonne aux yeux du Pharaon et aux yeux de tous ses serviteurs.
Shirin ya yi wa Fir’auna da kuma dukan hafsoshinsa kyau.
38 Et le Pharaon dit à ses serviteurs: Trouverons-nous un homme semblable à celui-ci, en qui est l’esprit des dieux?
Saboda haka Fir’auna ya tambaye su, “Za mu iya samun wani kamar wannan mutum, wannan wanda Ruhun Allah yake cikinsa?”
39 Et le Pharaon dit à Joseph: Puisque Dieu t’a fait connaître tout cela, personne n’est intelligent et sage comme toi.
Sai Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Da yake Allah ya ba ka sanin dukan waɗannan, babu wani mai basira da kuma hikima kamar ka.
40 Toi, tu seras sur ma maison, et tout mon peuple se dirigera d’après ton commandement; seulement quant au trône, je serai plus grand que toi.
Za ka shugabanci fadata, kuma dukan mutanena za su zama a ƙarƙashinka. Da sarauta kaɗai zan fi ka girma.”
41 Et le Pharaon dit à Joseph: Vois, je t’ai établi sur tout le pays d’Égypte.
Saboda haka Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ga shi na sa ka zama shugaban dukan ƙasar Masar.”
42 Et le Pharaon ôta son anneau de sa main, et le mit à la main de Joseph, et il le revêtit de vêtements de byssus, et mit un collier d’or à son cou;
Sa’an nan Fir’auna ya zare zoben sarauta daga yatsarsa, ya sa shi a yatsan Yusuf. Ya sanya masa rigar lallausan lilin, ya kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa.
43 et il le fit monter sur le second char qui était à lui; et on criait devant lui: Abrec! Et il l’établit sur tout le pays d’Égypte.
Ya sa shi ya hau keken yaƙi a matsayi mai binsa na biyu, mutane kuwa suka yi shela a gabansa suna cewa, “A ba da hanya!” Ta haka ya sa shi shugaba a kan dukan ƙasar Masar.
44 Et le Pharaon dit à Joseph: Moi je suis le Pharaon: sans toi nul ne lèvera la main ni le pied dans tout le pays d’Égypte.
Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ni ne Fir’auna, amma in ba tare da umarninka ba, ba wanda zai ɗaga hannu ko ƙafa a cikin dukan Masar.”
45 Et le Pharaon appela le nom de Joseph Tsaphnath-Pahnéakh; et il lui donna pour femme Asnath, fille de Poti-Phéra, sacrificateur d’On. Et Joseph parcourut le pays d’Égypte.
Fir’auna ya ba wa Yusuf suna Zafenat-Faneya, ya kuma ba shi Asenat’yar Fotifera firist na On, ta zama matarsa. Yusuf kuwa ya zaga dukan ƙasar Masar.
46 Et Joseph était âgé de 30 ans lorsqu’il se tint devant le Pharaon, le roi d’Égypte; et Joseph sortit de devant le Pharaon, et passa par tout le pays d’Égypte.
Yusuf yana zuwa shekara talatin sa’ad da ya shiga hidimar Fir’auna sarkin Masar. Yusuf kuwa ya fita daga gaban Fir’auna, ya zaga ko’ina a Masar.
47 Et la terre rapporta à pleines mains pendant les sept années d’abondance.
A shekaru bakwai na yalwa, ƙasar ta ba da amfani mai yawa.
48 Et [Joseph] rassembla tous les vivres des sept années qui furent dans le pays d’Égypte, et mit les vivres dans les villes; il mit dans chaque ville les vivres [provenant] des champs qui étaient autour d’elle.
Yusuf ya tattara dukan abincin da aka samu a waɗannan shekaru bakwai na yalwa a Masar, ya kuma yi ajiyarsu a cikin birane. A kowane birni, ya sa abincin da aka nome a kewayensa.
49 Et Joseph amassa du blé, comme le sable de la mer, une immense quantité, jusqu’à ce qu’on cessa de compter, parce qu’il était sans nombre.
Sai Yusuf ya tara hatsi da yawan gaske, kamar yashi a bakin teku, har sai da ya kāsa iya auna shi, gama ba a iya aunawa.
50 Et, avant que vienne l’année de la famine, il naquit à Joseph deux fils, qu’Asnath, fille de Poti-Phéra, sacrificateur d’On, lui enfanta.
Kafin shekarun yunwa su zo, Asenat’yar Fotifera, firist na On, ta haifa wa Yusuf’ya’ya maza biyu.
51 Et Joseph appela le nom du premier-né Manassé: car Dieu m’a fait oublier toute ma peine, et toute la maison de mon père.
Yusuf ya ba wa ɗansa na fari suna Manasse ya ce, “Gama Allah ya sa na mance dukan wahalata da dukan gidan mahaifina.”
52 Et il appela le nom du second Éphraïm: car Dieu m’a fait fructifier dans le pays de mon affliction.
Ya ba wa ɗansa na biyu suna Efraim ya ce, “Gama Allah ya wadata ni cikin wahalata.”
53 Et les sept années de l’abondance qui avait été dans le pays d’Égypte finirent;
Shekaru bakwai na yalwa a Masar suka zo ga ƙarshe,
54 et les sept années de la famine commencèrent à venir, comme Joseph avait dit. Et il y eut famine dans tous les pays; mais dans tout le pays d’Égypte il y avait du pain.
sai shekaru bakwai na yunwa suka soma shigowa, kamar yadda Yusuf ya faɗa. Aka yi yunwa ko’ina amma ban da ƙasar Masar. Don akwai abinci.
55 Et tout le pays d’Égypte eut faim, et le peuple cria au Pharaon pour du pain; et le Pharaon dit à tous les Égyptiens: Allez à Joseph; faites ce qu’il vous dira.
Sa’ad da dukan Masar ta fara jin yunwa, sai mutane suka yi wa Fir’auna kuka don abinci. Sai Fir’auna ya ce wa dukan Masarawa, “Ku tafi wurin Yusuf, ku kuma yi abin da ya faɗa muku.”
56 Et la famine était sur toute la face de la terre; et Joseph ouvrit tous les lieux de dépôt, et vendit du blé aux Égyptiens; et la famine sévissait dans le pays d’Égypte.
Sa’ad da yunwa ta bazu a dukan ƙasar, sai Yusuf ya buɗe gidajen ajiya, ya kuma sayar da hatsi ga Masarawa, gama yunwa ta yi tsanani a dukan Masar.
57 Et de toute la terre on venait en Égypte, vers Joseph, pour acheter du blé; car la famine sévissait sur toute la terre.
Dukan ƙasashe kuwa suka zo Masar don saya hatsi daga Yusuf, gama yunwa ta yi tsanani a dukan duniya.

< Genèse 41 >