< Genèse 33 >
1 Et Jacob leva ses yeux, et regarda; et voici, Ésaü venait, et 400 hommes avec lui. Et il partagea les enfants entre Léa et Rachel et les deux servantes.
Yaƙub ya ɗaga ido ke nan, sai ga Isuwa yana zuwa tare da mutanensa ɗari huɗu; saboda haka sai ya rarraba’ya’yan wa Liyatu, Rahila da kuma matan nan biyu masu hidima.
2 Et il mit à la tête les servantes et leurs enfants, et puis Léa et ses enfants, et puis Rachel et Joseph.
Ya sa matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu a gaba, Liyatu da’ya’yanta biye, sa’an nan Rahila da Yusuf a baya.
3 Et il passa devant eux, et se prosterna en terre par sept fois, jusqu’à ce qu’il soit proche de son frère.
Shi kansa ya sha gabansu, ya rusuna har ƙasa sau bakwai, kafin ya kai kusa da inda ɗan’uwansa Isuwa yake.
4 Et Ésaü courut à sa rencontre, et l’embrassa, et se jeta à son cou, et lui donna un baiser; et ils pleurèrent.
Amma Isuwa ya ruga a guje ya sadu da Yaƙub ya rungume shi; ya faɗa a wuyansa ya sumbace shi. Suka kuma yi kuka.
5 Et il leva ses yeux, et vit les femmes et les enfants, et dit: Que te sont-ils, ceux-là? Et il dit: Ce sont les enfants que Dieu a donnés à ton serviteur.
Sa’an nan Isuwa ya ɗaga ido ya ga mata da’ya’ya. Ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan tare da kai?” Yaƙub ya amsa, “Su ne’ya’yan da Allah cikin alheri ya ba bawanka.”
6 Et les servantes s’approchèrent, elles et leurs enfants, et se prosternèrent.
Sai matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu suka matso kusa suka durƙusa.
7 Et Léa aussi s’approcha avec ses enfants, et ils se prosternèrent; et ensuite Joseph et Rachel s’approchèrent, et se prosternèrent.
Biye da su, Liyatu da’ya’yanta suka zo suka rusuna. A ƙarshe duka, sai Yusuf da Rahila suka zo, su ma suka rusuna.
8 Et il dit: Que veux-tu avec tout ce camp que j’ai rencontré? Et il dit: C’est pour trouver grâce aux yeux de mon seigneur.
Isuwa ya yi tambaya, “Me kake nufi da dukan abubuwan nan da na sadu da su ana korarsu?” Sai Yaƙub ya ce, “Don in sami tagomashi a idanunka ne, ranka yă daɗe.”
9 Et Ésaü dit: J’ai [de tout] en abondance, mon frère; que ce qui est à toi soit à toi.
Amma Isuwa ya ce, “Na riga na sami abin da ya ishe ni, ɗan’uwana. Riƙe abin da kake da shi don kanka.”
10 Et Jacob dit: Non, je te prie; si j’ai trouvé grâce à tes yeux, prends mon présent de ma main, car c’est pour cela que j’ai vu ta face comme si j’avais vu la face de Dieu, et que tu m’as accueilli favorablement.
Sai Yaƙub ya ce, “A’a, ina roƙonka, in na sami tagomashi a idanunka, sai ka karɓi wannan kyautai daga gare ni. Gama ganin fuskarka kamar ganin fuskar Allah ne, yanzu da ka karɓe ni da farin ciki.
11 Prends, je te prie, mon présent qui t’a été amené; car Dieu a usé de grâce envers moi, et j’ai de tout. Et il le pressa, et il le prit.
Ina roƙonka ka karɓi kyautar da aka kawo maka, gama Allah ya yi mini alheri kuma ina da kome da nake bukata.” Ganin yadda Yaƙub ya nace, sai Isuwa ya karɓa.
12 Et [Ésaü] dit: Partons et allons-nous-en, et je marcherai devant toi.
Sa’an nan Isuwa ya ce, “Bari mu tafi, zan yi maka rakiya.”
13 Et [Jacob] lui dit: Mon seigneur sait que les enfants sont délicats, et que je suis chargé de menu et de gros bétail qui allaite; et si on les presse un seul jour, ils mourront – tout le troupeau.
Amma Yaƙub ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ka san cewa’ya’yan ƙanana ne, dole in lura da tumaki da shanun da suke shayar da jariransu. In aka kore su da gaggawa a rana guda kaɗai, dukan dabbobin za su mutu.
14 Que mon seigneur, je te prie, passe devant son serviteur; et moi je cheminerai tout doucement au pas de ce bétail qui est devant moi, et au pas des enfants, jusqu’à ce que j’arrive auprès de mon seigneur, à Séhir.
Saboda haka bari ranka yă daɗe yă sha gaban bawansa, ni kuma in tafi a hankali bisa ga saurin abin da ake kora a gabana da kuma saurin’ya’yan, sai na iso wurinka ranka yă daɗe, a Seyir.”
15 Et Ésaü dit: Je te prie, que je laisse avec toi quelques-uns des gens qui sont avec moi. Et il dit: Pourquoi cela? Que je trouve grâce aux yeux de mon seigneur!
Sai Isuwa ya ce, “To, bari in bar waɗansu mutanena tare da kai.” Yaƙub ya ce, “Amma me ya sa za ka yi haka? Bari dai in sami tagomashi a idanunka ranka yă daɗe.”
16 Et Ésaü s’en retourna ce jour-là, par son chemin, à Séhir.
Saboda haka a wannan rana Isuwa ya kama hanyar komawa zuwa Seyir.
17 Et Jacob s’en alla à Succoth, et bâtit une maison pour lui, et fit des cabanes pour son bétail: c’est pourquoi on appela le nom du lieu Succoth.
Yaƙub kuwa, ya tafi Sukkot, inda ya gina wuri domin kansa, ya kuma yi bukkoki domin dabbobinsa. Shi ya sa aka kira wurin Sukkot.
18 Et Jacob arriva en paix à la ville de Sichem, qui est dans le pays de Canaan, comme il venait de Paddan-Aram; et il campa en face de la ville.
Bayan Yaƙub ya zo daga Faddan Aram, ya iso lafiya a birnin Shekem a Kan’ana, ya kuma kafa sansani a ƙofar birni.
19 Et il acheta de la main des fils de Hamor, père de Sichem, pour 100 kesitas, la portion du champ où il avait dressé sa tente;
Ya sayi fili daga’ya’yan Hamor maza, mahaifin Shekem inda ya kafa tentinsa, a bakin azurfa ɗari.
20 et il dressa là un autel et l’appela El-Élohé-Israël.
A can ya kafa bagade ya kuma kira shi El Elohe Isra’ila.