< Ézéchiel 43 >

1 Et il me conduisit à la porte, la porte qui regardait vers l’orient.
Sai mutumin ya kawo ni ƙofar da take fuskantar gabas,
2 Et voici, la gloire du Dieu d’Israël venait du côté de l’orient; et sa voix était comme une voix de grandes eaux, et la terre était illuminée par sa gloire.
sai na ga ɗaukakar Allah na Isra’ila tana tahowa daga gabas. Muryarsa ta yi kamar rurin ruwaye masu gudu, ƙasa kuma ta haskaka da ɗaukakarsa.
3 Et l’aspect de la vision que je voyais était comme la vision que j’avais vue quand je vins pour détruire la ville; et les visions étaient comme la vision que je vis près du fleuve Kebar; et je tombai sur ma face.
Wahayin da na gani ya yi kamar wahayin da na gani sa’ad da ya zo don yă hallaka birnin, kamar kuma wahayin da na gani kusa da Kogin Kebar, na kuwa fāɗi rubda ciki.
4 Et la gloire de l’Éternel entra dans la maison par le chemin de la porte qui regardait vers l’orient.
Ɗaukakar Ubangiji ta shiga haikali ta ƙofar da take fuskantar gabas.
5 Et l’Esprit m’enleva et m’amena dans le parvis intérieur; et voici, la gloire de l’Éternel remplissait la maison.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni cikin fili na can ciki, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
6 Et j’entendis [quelqu’un] qui me parlait depuis la maison, et un homme se tenait à côté de moi.
Yayinda mutumin yana tsaye kusa da ni, na ji wani yana magana da ni daga cikin haikalin.
7 Et il me dit: Fils d’homme, [c’est ici] le lieu de mon trône et le lieu de la plante de mes pieds, où je demeurerai au milieu des fils d’Israël à toujours. Et la maison d’Israël ne rendra plus impur mon saint nom, ni eux, ni leurs rois, par leurs prostitutions et par les cadavres de leurs rois [sur] leurs hauts lieux,
Ya ce, “Ɗan mutum, wannan shi ne kursiyina da wurin tafin ƙafafuna. A nan ne zan zauna a cikin Isra’ilawa har abada. Gidan Isra’ila ba zai ƙara ɓata sunana mai tsarki ba, ko su ko sarakunansu, ta wurin karuwanci da gumakan da ba su da rai, sarakunansu a masujadan kan tudu.
8 alors qu’ils mettaient leur seuil contre mon seuil, et leurs poteaux à côté de mes poteaux, et [qu’il y avait seulement] un mur entre moi et eux: et ils ont rendu mon saint nom impur par leurs abominations qu’ils ont commises, et je les ai consumés dans ma colère.
Sa’ad da suka sa madogarar ƙofarsu kusa da madogarar ƙofata, da katanga kawai a tsakanina da su, sun ɓata sunana mai tsarki ta wurin ayyukansu masu banƙyama. Saboda haka na hallaka su cikin fushina.
9 Maintenant, qu’ils éloignent de moi leurs prostitutions et les cadavres de leurs rois, et je demeurerai au milieu d’eux à toujours.
Yanzu bari su kawar da karuwancinsu da gumakansu waɗanda ba su da rai na sarakunansu daga gabana, zan kuwa zauna a cikinsu har abada.
10 Toi, fils d’homme, montre à la maison d’Israël la maison, afin qu’ils soient confus à cause de leurs iniquités; et qu’ils en mesurent la disposition.
“Ɗan mutum, ka bayyana haikalin ga mutanen Isra’ila, don su ji kunya saboda zunubansu. Bari su yi la’akari da fasalin,
11 Et, s’ils sont confus de tout ce qu’ils ont fait, fais-leur connaître la forme de la maison, et son arrangement, et ses issues, et ses entrées, et toutes ses formes, et toutes ses ordonnances, et toutes ses formes, et toutes ses lois; et écris-les devant leurs yeux, afin qu’ils observent toute sa forme, et toutes ses ordonnances, et qu’ils les fassent.
kuma in suka ji kunyar abubuwan da suka aikata, sai ka sanar musu fasalin haikalin da shirye-shiryensa, ƙofofinsa na shiga da fita, dukan fasalinsa da dukan ƙa’idodinsa da dokokinsa. Ka rubuta waɗannan a gabansu saboda su yi aminci da fasalinsa su kuma kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
12 C’est ici la loi de la maison: sur la cime de la montagne, toutes ses limites tout à l’entour sont un lieu très saint. Voici, telle est la loi de la maison.
“Wannan ita ce dokar haikalin. Dukan filin da yake kewaye a kan dutsen, zai zama wuri mafi tsarki. Dokar haikalin ke nan.
13 Et ce sont ici les mesures de l’autel, en coudées; la coudée est une coudée et une paume: l’embasement avait une coudée [en hauteur], et une coudée en largeur; et le rebord de son avancée, tout autour, un empan; et c’était la base de l’autel.
“Waɗannan su ne aune-aunen bagade a tsawon kamu, wannan kamu shi ne kamun tafin hannu. Zurfin magudanar ruwansa kamu ɗaya ne fāɗinsa kuma kamu ɗaya, tare da da’ira kamun tafi ɗaya kewaye da gefensa. Wannan kuma shi ne tsayin bagaden.
14 Et depuis l’embasement sur le sol jusqu’à la banquette inférieure il y avait deux coudées, et une coudée en largeur; et depuis la petite banquette jusqu’à la grande banquette, quatre coudées, et une coudée en largeur.
Daga lambatun da yake a ƙasa har zuwa ƙaramin mahaɗin da yake ƙasa wanda ya kewaye bagade, tsayinsa kamu biyu ne, fāɗinsa kuma kamu guda. Daga ƙaramin mahaɗi zuwa babban mahaɗin wanda ya kewaye bagade, zai zama kamu huɗu, fāɗinsa kuwa kamu ɗaya.
15 Et la montagne de Dieu avait quatre coudées, et, depuis le lion de Dieu en haut, les quatre cornes.
Murhun bagaden kamu huɗu ne, akwai ƙahoni guda huɗu sun miƙe sama daga murhun.
16 Et le lion de Dieu avait douze [coudées] de longueur, sur douze de largeur, en carré, sur ses quatre côtés;
Murhun bagaden murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha biyu, fāɗinsa kuma kamu goma sha biyu.
17 et la banquette, 14 [coudées] de longueur, sur 14 de largeur, sur ses quatre côtés; et le rebord qui l’entourait, une demi-coudée, et son embasement une coudée à l’entour; et ses degrés regardaient vers l’orient.
Gefen bisa ma murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha huɗu fāɗinsa kuma kamu goma huɗu, da da’ira da yake da fāɗin rabin kamu da magudanan ruwa kamu guda kewaye. Matakan bagaden suna fuskantar gabas.”
18 Et il me dit: Fils d’homme, ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Ce sont ici les ordonnances de l’autel, au jour où il sera fait, pour y offrir des holocaustes et pour faire aspersion du sang sur lui.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa waɗannan su ne za su zama ƙa’idodi don yin hadaya ta ƙonawa da yayyafawar jini a kan bagaden sa’ad da aka gina shi.
19 Et aux sacrificateurs Lévites, qui sont de la semence de Tsadok, qui s’approchent de moi, pour faire mon service, dit le Seigneur, l’Éternel, tu donneras un jeune taureau comme sacrifice pour le péché.
Za ka ba da ɗan bijimi a matsayin hadaya ta ƙonawa ga firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, na iyalin Zadok, waɗanda suke zuwa kusa don hidima a gabana, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 Et tu prendras de son sang, et tu le mettras sur les quatre cornes de [l’autel], et sur les quatre coins de la banquette, et sur le rebord, tout à l’entour; et tu le purifieras, et tu feras propitiation pour lui.
Za ka ɗibi jininsa ka zuba shi a ƙahoni huɗu na bagaden a gefen bisa da kuma kewaye da da’irar, ta haka za ka tsarkake bagaden ka kuma yi kafara dominsa.
21 Et tu prendras le taureau du sacrifice pour le péché, et on le brûlera dans le lieu de la maison, désigné [pour cela], en dehors du sanctuaire.
Za ka ɗauki bijimi na hadaya don zunubi ka ƙone shi a sashen da aka shirya na haikalin a wani wuri waje da wuri mai tsarki.
22 Et le second jour, tu présenteras un bouc sans défaut, comme sacrifice pour le péché; et on purifiera l’autel comme on l’avait purifié par le taureau.
“A rana ta biyu za ka miƙa bunsuru marar lahani domin hadaya don zunubi, za a kuma tsarkake bagaden yadda aka yi da bijimin.
23 Quand tu auras achevé de purifier [l’autel], tu présenteras un jeune taureau sans défaut, et un bélier du menu bétail, sans défaut;
Sa’ad da ka gama tsarkake shi, sai ka miƙa ɗan bijimi da kuma rago daga cikin garke, dukansu marasa lahani.
24 et tu les présenteras devant l’Éternel, et les sacrificateurs jetteront du sel sur eux, et les offriront en holocauste à l’Éternel.
Za ka miƙa su a gaban Ubangiji, firistoci kuma za su barbaɗe gishiri a kansu su kuma miƙa su kamar hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
25 Pendant sept jours, tu offriras un bouc en sacrifice pour le péché, chaque jour; et on offrira un jeune taureau et un bélier du menu bétail, sans défaut.
“Kwana bakwai za ka tanada bunsuru kullum domin hadaya don zunubi; za ka kuma tanada ɗan bijimi da rago daga garke, dukansu marasa lahani.
26 Pendant sept jours, on fera propitiation pour l’autel, et on le purifiera, et on le consacrera.
Kwana bakwai za su yi kafara saboda bagaden su kuma tsarkake shi; ta haka za su keɓe shi.
27 Et quand les jours seront achevés, il arrivera que, dès le huitième jour et ensuite, les sacrificateurs offriront sur l’autel vos holocaustes et vos sacrifices de prospérités; et je vous aurai pour agréables, dit le Seigneur, l’Éternel.
A ƙarshen waɗannan kwanaki, daga rana ta takwas zuwa gaba, firistoci za su miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kan bagade. Sa’an nan zan karɓe ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ézéchiel 43 >