< Ézéchiel 23 >

1 Et la parole de l’Éternel vint à moi, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils d’homme, il y avait deux femmes, filles d’une même mère;
“Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
3 et elles se prostituèrent en Égypte, elles se prostituèrent dans leur jeunesse: là leurs mamelles furent froissées, là les seins de leur virginité furent pressés.
Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
4 Et leurs noms étaient: Ohola, l’aînée, et Oholiba, sa sœur; et elles étaient à moi, et elles enfantèrent des fils et des filles. Et leurs noms: Samarie est Ohola, et Jérusalem, Oholiba.
Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
5 Et Ohola, étant à moi, se prostitua et se passionna pour ses amants, pour les Assyriens, ses voisins,
“Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
6 vêtus de bleu, gouverneurs et chefs, tous beaux jeunes hommes, cavaliers montés sur des chevaux;
waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
7 et elle se livra à ses prostitutions avec eux, tous l’élite des fils d’Assur; et, avec tous ceux pour lesquels elle se passionna, avec toutes leurs idoles, elle se rendit impure.
Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
8 Et elle n’abandonna pas ses prostitutions [qui datent] de l’Égypte, car ils avaient couché avec elle dans sa jeunesse, et ils avaient pressé les seins de sa virginité, et avaient versé sur elle leur prostitution.
Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
9 C’est pourquoi je la livrai en la main de ses amants, en la main des fils d’Assur pour lesquels elle s’était passionnée.
“Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
10 Ils découvrirent sa nudité, prirent ses fils et ses filles, et la tuèrent elle-même par l’épée; et elle devint renommée parmi les femmes, et ils exécutèrent des jugements sur elle.
Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
11 Et sa sœur Oholiba vit [cela], et se corrompit plus qu’elle dans ses amours passionnées; et ses prostitutions furent plus [grandes] que les débauches de sa sœur.
“Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
12 Elle se passionna pour les fils d’Assur, gouverneurs et chefs, ses voisins, vêtus magnifiquement, cavaliers montés sur des chevaux, tous beaux jeunes hommes.
Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
13 Et je vis qu’elle s’était rendue impure: elles suivaient toutes deux la même voie.
Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
14 Et elle avait ajouté à ses prostitutions, et elle avait vu des hommes dessinés sur le mur, des images de Chaldéens tracés au vermillon,
“Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
15 portant des ceintures sur leurs reins, avec des tiares flottantes sur leurs têtes, tous ayant l’aspect de grands seigneurs, à la ressemblance des fils de Babel, de la Chaldée, pays de leur naissance;
da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
16 et elle se passionna pour eux en les voyant de ses yeux, et envoya des messagers vers eux en Chaldée.
Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
17 Et les fils de Babel vinrent vers elle dans le lit des amours, et la rendirent impure par leur prostitution, et elle se rendit impure avec eux; puis son âme se détacha d’eux.
Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
18 Et elle découvrit ses prostitutions, et elle découvrit sa nudité; et mon âme se détacha d’elle, comme mon âme s’était détachée de sa sœur.
Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
19 Et elle multiplia ses prostitutions, se souvenant des jours de sa jeunesse, où elle s’était prostituée dans le pays d’Égypte;
Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
20 et elle se passionna pour ses concubins, dont la chair est [comme] la chair des ânes, et dont le flux est [comme] le flux des chevaux.
A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
21 Tu te rappelas l’infamie de ta jeunesse, lorsque les Égyptiens pressaient tes seins à cause des mamelles de ta jeunesse.
Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
22 C’est pourquoi, Oholiba! ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Voici, je réveille contre toi tes amants, desquels ton âme s’est détachée, et je les ferai venir contre toi de tous côtés:
“Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
23 les fils de Babel, et tous les Chaldéens, Pekod et Shoa et Koa, tous les fils d’Assur avec eux, tous beaux jeunes hommes, gouverneurs et chefs, grands seigneurs et gens de renom, tous montés sur des chevaux.
Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
24 Et ils viendront contre toi avec des armes, des chars et des roues, et avec un rassemblement de peuples; ils se placeront contre toi, tout autour, avec le bouclier et l’écu et le casque; et je leur commettrai le jugement, et ils te jugeront selon leurs jugements.
Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
25 Et je mettrai ma jalousie contre toi, et ils agiront envers toi avec fureur: ils te couperont le nez et les oreilles; et ce qui restera de toi tombera par l’épée. Ils prendront tes fils et tes filles, et ce qui restera de toi sera dévoré par le feu.
Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
26 Et ils te dépouilleront de tes vêtements, et prendront les objets dont tu te pares;
Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
27 et je ferai cesser en toi ton infamie et ta prostitution [qui date] du pays d’Égypte; et tu ne lèveras plus tes yeux vers eux, et tu ne te souviendras plus de l’Égypte.
Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
28 Car ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Voici, je te livre en la main de ceux que tu hais, en la main de ceux dont ton âme s’est détachée;
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
29 et ils agiront envers toi avec haine, et prendront tout ton travail, et te laisseront nue et découverte; et la nudité de tes débauches, et ton infamie, et tes prostitutions, seront découvertes.
Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
30 Ces choses t’arriveront, parce que tu t’es prostituée après les nations, parce que tu t’es rendue impure par leurs idoles.
sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
31 Tu as marché dans le chemin de ta sœur; et j’ai mis sa coupe dans ta main.
Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
32 Ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Tu boiras la coupe de ta sœur, profonde et large; tu seras en risée et en raillerie, [car] elle contient beaucoup.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
33 Tu seras remplie d’ivresse et de chagrin; ce sera une coupe d’étonnement et de désolation, la coupe de ta sœur Samarie.
Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
34 Tu la boiras, et tu la suceras, et tu en rongeras les tessons, et tu te déchireras les seins; car j’ai parlé, dit le Seigneur, l’Éternel.
Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
35 C’est pourquoi, ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Parce que tu m’as oublié et que tu m’as jeté derrière ton dos, toi aussi porte ton infamie et tes prostitutions.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
36 Et l’Éternel me dit: Fils d’homme, jugeras-tu Ohola et Oholiba? Déclare-leur leurs abominations.
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
37 Car elles ont commis adultère, et il y a du sang à leurs mains; elles ont commis adultère avec leurs idoles; et même leurs fils qu’elles m’avaient enfantés, elles les leur ont consacrés pour être dévorés.
gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
38 Elles m’ont fait encore ceci: elles ont rendu impur mon sanctuaire en ce jour-là, et elles ont profané mes sabbats;
Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
39 quand elles avaient égorgé leurs fils à leurs idoles, elles venaient ce même jour dans mon sanctuaire, pour le profaner; et voici, elles ont fait ainsi au milieu de ma maison.
A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
40 Et bien plus, elles ont envoyé vers des hommes venant de loin, auxquels un messager avait été envoyé; et voici, ils sont venus, ceux pour lesquels tu t’es lavée, tu as peint tes yeux et tu t’es parée d’ornements;
“Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
41 et tu t’es assise sur un lit somptueux devant lequel était dressée une table, et tu as placé sur elle mon encens et mon huile.
Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
42 Et il y avait en elle le bruit d’une multitude à l’aise; et, vers la foule des hommes, on fit venir du désert des buveurs, qui leur mirent des bracelets aux mains et une couronne de beauté sur la tête.
“Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
43 Et j’ai dit de celle qui était usée par l’adultère: Maintenant commettra -t-elle ses prostitutions, elle aussi?
Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
44 Et on est venu vers elle comme on vient vers une femme prostituée. Ainsi ils sont venus vers Ohola et vers Oholiba, femmes criminelles.
Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
45 Et des hommes justes, eux, les jugeront du jugement des femmes adultères et du jugement de celles qui versent le sang; car elles sont adultères, et il y a du sang à leurs mains.
Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
46 Car ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: On fera monter contre elles un rassemblement [d’hommes], et on les livrera à la vexation et au pillage;
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
47 et le rassemblement les lapidera avec des pierres, et ils les transperceront avec leurs épées; ils tueront leurs fils et leurs filles, et ils brûleront leurs maisons par le feu.
Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
48 Et je ferai cesser l’infamie dans le pays; et toutes les femmes seront enseignées, et ne feront pas selon votre infamie.
“Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
49 Et ils mettront vos infamies sur vous, et vous porterez les péchés de vos idoles; et vous saurez que je suis le Seigneur, l’Éternel.
Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ézéchiel 23 >