< Ézéchiel 22 >

1 Et la parole de l’Éternel vint à moi, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Et toi, fils d’homme, jugeras-tu, jugeras-tu la ville de sang? et lui feras-tu connaître toutes ses abominations?
“Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
3 Tu diras: Ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Ville, qui verses le sang au milieu de toi, afin que ton temps vienne, et qui as fait des idoles chez toi pour te rendre impure,
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
4 tu t’es rendue coupable par ton sang que tu as versé, et tu t’es rendue impure par tes idoles que tu as faites, et tu as fait approcher tes jours, et tu es parvenue à tes années: c’est pourquoi je t’ai livrée à l’opprobre des nations et à la raillerie de tous les pays.
kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
5 Ceux qui sont près et ceux qui sont loin de toi se moqueront de toi, qui es impure de renommée, [et] pleine de trouble.
Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
6 Voici, les princes d’Israël étaient au-dedans de toi pour verser le sang, chacun selon son pouvoir.
“‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
7 Ils ont méprisé père et mère au-dedans de toi; ils ont agi oppressivement envers l’étranger au milieu de toi; ils ont foulé l’orphelin et la veuve au-dedans de toi.
A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
8 Tu as méprisé mes choses saintes, et tu as profané mes sabbats.
Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
9 Il y a eu au-dedans de toi des hommes calomniateurs pour verser le sang; et au-dedans de toi ils ont mangé sur les montagnes; ils ont commis des infamies au milieu de toi;
A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
10 au-dedans de toi ils ont découvert la nudité d’un père; au-dedans de toi ils ont humilié la femme séparée à cause de ses mois.
A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
11 Et l’un a commis une abomination avec la femme de son prochain, et l’autre a rendu impure sa belle-fille par une infamie, et un autre, au-dedans de toi, a humilié sa sœur, fille de son père.
A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
12 Au-dedans de toi, ils ont reçu des présents pour verser le sang; tu as pris intérêt et usure, et tu as fait par l’extorsion un gain déshonnête aux dépens de ton prochain; et tu m’as oublié, dit le Seigneur, l’Éternel.
A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 Et voici, j’ai frappé des mains contre ton gain déshonnête que tu as fait, et contre le sang qui est versé au milieu de toi.
“‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
14 Ton cœur tiendra-t-il ferme, ou tes mains seront-elles fortes, aux jours où j’agirai contre toi? Moi, l’Éternel, j’ai parlé, et je le ferai.
Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
15 Et je te disperserai parmi les nations, et je te disséminerai dans les pays, et je consumerai du milieu de toi ton impureté.
Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
16 Et tu seras profanée par toi-même aux yeux des nations, et tu sauras que je suis l’Éternel.
Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
17 Et la parole de l’Éternel vint à moi, disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 Fils d’homme, la maison d’Israël est devenue pour moi des scories; eux tous sont de l’airain, et de l’étain, et du fer, et du plomb, au milieu du fourneau; ils sont devenus des scories d’argent.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
19 C’est pourquoi, ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Parce que vous êtes tous devenus des scories, à cause de cela, voici, je vous rassemble au milieu de Jérusalem.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
20 [Comme] on rassemble l’argent, et l’airain, et le fer, et le plomb, et l’étain, au milieu d’un fourneau, pour souffler le feu dessus afin de les fondre, ainsi je vous rassemblerai dans ma colère et dans ma fureur, et je vous laisserai [là], et je vous fondrai.
Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
21 Et je vous assemblerai, et je soufflerai contre vous le feu de mon courroux, et vous serez fondus au milieu de Jérusalem.
Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
22 Comme l’argent est fondu au milieu du fourneau, ainsi vous serez fondus au milieu d’elle; et vous saurez que moi, l’Éternel, j’ai versé ma fureur sur vous.
Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
23 Et la parole de l’Éternel vint à moi, disant:
Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
24 Fils d’homme, dis-lui: Tu es un pays qui n’est pas purifié, qui n’est pas arrosé de pluie au jour de l’indignation.
“Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
25 Il y a une conjuration de ses prophètes au milieu d’elle, comme un lion rugissant qui déchire la proie; ils dévorent les âmes, ils enlèvent les richesses et les choses précieuses; ils multiplient ses veuves au milieu d’elle.
Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
26 Ses sacrificateurs font violence à ma loi et profanent mes choses saintes; ils ne font pas de différence entre ce qui est saint et ce qui est profane, et ils ne font pas connaître la différence entre ce qui est impur et ce qui est pur; et ils cachent leurs yeux de mes sabbats, et je suis profané au milieu d’eux.
Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
27 Ses princes, au milieu d’elle, sont comme des loups qui déchirent la proie, pour verser le sang, pour détruire les âmes, afin de faire un gain déshonnête.
Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
28 Et ses prophètes leur ont fait des enduits de mauvais mortier, ayant des visions de vanité et devinant pour eux le mensonge, disant: Ainsi dit le Seigneur, l’Éternel; – et l’Éternel n’a point parlé.
Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
29 Le peuple du pays pratique l’extorsion et commet la rapine, et foule l’affligé et le pauvre; et ils oppriment l’étranger contrairement à tout droit.
Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
30 Et j’ai cherché parmi eux un homme qui ferme l’enceinte, et qui se tienne à la brèche devant moi pour le pays, afin que je ne le détruise pas; mais je n’en ai point trouvé.
“Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
31 Et je verserai sur eux mon indignation; dans le feu de mon courroux je les consumerai, je ferai retomber leur voie sur leur tête, dit le Seigneur, l’Éternel.
Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ézéchiel 22 >