< Ézéchiel 13 >

1 Et la parole de l’Éternel vint à moi, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils d’homme, prophétise contre les prophètes d’Israël qui prophétisent, et dis à ceux qui prophétisent d’après leur propre cœur: Écoutez la parole de l’Éternel!
“Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
3 Ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Malheur aux prophètes insensés qui suivent leur propre esprit et n’ont rien vu!
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
4 Israël, tes prophètes ont été comme des renards dans les lieux déserts.
Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
5 Vous n’êtes point montés aux brèches, et vous n’avez pas fermé l’enceinte pour la maison d’Israël, afin de tenir ferme dans la bataille, au jour de l’Éternel.
Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
6 Ils ont eu des visions de vanité et de divination de mensonge, ceux qui disent: L’Éternel a dit! et l’Éternel ne les a pas envoyés; et ils font espérer que la parole dite sera accomplie!
Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
7 N’avez-vous pas vu des visions de vanité et prononcé des divinations de mensonge, quand vous dites: L’Éternel a dit! – et je n’ai point parlé?
Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
8 C’est pourquoi, ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Parce que vous dites des choses vaines, et que vous avez eu des visions de mensonge, à cause de cela, voici, je suis contre vous, dit le Seigneur, l’Éternel.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Et ma main sera sur les prophètes qui ont des visions de vanité et qui devinent le mensonge: ils ne seront pas dans l’assemblée de mon peuple, et ils ne seront pas écrits dans le registre de la maison d’Israël, et ils n’entreront pas dans la terre d’Israël; et vous saurez que je suis le Seigneur, l’Éternel.
Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
10 Parce que, oui, parce qu’ils égarent mon peuple, disant: Paix! et il n’y a point de paix; et que, si celui-ci bâtit un mur, ceux-là l’enduisent de mauvais mortier,
“‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
11 dis à ceux qui enduisent le mur de mauvais mortier, qu’il s’écroulera: il y aura une pluie torrentielle; et vous, pierres de grêle, vous tomberez, et un vent de tempête éclatera.
saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
12 Et voici, quand le mur s’écroulera, ne vous sera-t-il pas dit: Où est l’enduit dont vous l’avez enduit?
Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
13 C’est pourquoi, ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Je ferai éclater, dans ma fureur, un vent de tempête; et, dans ma colère, il y aura une pluie torrentielle, et, dans ma fureur, des pierres de grêle, pour détruire entièrement.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
14 Et je renverserai le mur que vous avez enduit de mauvais mortier, et je le jetterai par terre, et ses fondements seront découverts, et il croulera, et vous périrez au milieu de ses ruines; et vous saurez que je suis l’Éternel.
Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Et je consommerai ma fureur contre ce mur et contre ceux qui l’enduisent de mauvais mortier; et je vous dirai: Le mur n’est plus, ni ceux qui l’enduisaient,
Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
16 les prophètes d’Israël qui prophétisent touchant Jérusalem, et qui voient pour elle une vision de paix, et il n’y a point de paix, dit le Seigneur, l’Éternel.
waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
17 Et toi, fils d’homme, tourne ta face contre les filles de ton peuple qui prophétisent d’après leur propre cœur, et prophétise contre elles,
“To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
18 et dis: Ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Malheur à celles qui cousent des coussinets pour toutes les jointures des mains, et qui font des voiles pour la tête [des gens] de toute taille, afin de prendre au piège des âmes! Voulez-vous prendre au piège les âmes de mon peuple et vous conserver la vie à vous-mêmes?
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
19 Et me profaneriez-vous auprès de mon peuple pour des poignées d’orge et pour des morceaux de pain, afin de faire mourir les âmes qui ne devaient pas mourir, et pour faire vivre les âmes qui ne devaient pas vivre, en mentant à mon peuple qui écoute le mensonge?
Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
20 C’est pourquoi, ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Voici, j’en veux à vos coussinets pour que les âmes, que par eux vous prenez au piège, s’envolent; et je les arracherai de dessus vos bras, et je ferai échapper les âmes que vous prenez au piège, les âmes, … afin qu’elles s’envolent;
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
21 et je déchirerai vos voiles, et je délivrerai mon peuple de vos mains, et ils ne seront plus en vos mains pour les prendre au piège; et vous saurez que je suis l’Éternel.
Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
22 Parce que vous avez chagriné par la fausseté le cœur du juste, que moi je n’ai pas attristé, et parce que vous avez fortifié les mains du méchant, pour qu’il ne se détourne pas de ses mauvaises voies afin de sauver sa vie,
Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
23 à cause de cela, vous n’aurez plus de visions de vanité et vous ne pratiquerez plus la divination; et je délivrerai mon peuple de vos mains, et vous saurez que je suis l’Éternel.
saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”

< Ézéchiel 13 >