< Exode 1 >

1 Et ce sont ici les noms des fils d’Israël qui entrèrent en Égypte; ils y entrèrent avec Jacob, chacun avec sa famille:
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
2 Ruben, Siméon, Lévi et Juda;
Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
3 Issacar, Zabulon et Benjamin;
Issakar, Zebulun da Benyamin;
4 Dan et Nephthali; Gad et Aser.
Dan da Naftali; Gad da Asher.
5 Et toutes les âmes issues des reins de Jacob étaient 70 âmes; or Joseph était en Égypte.
Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
6 Et Joseph mourut, et tous ses frères, et toute cette génération-là.
Yanzu Yusuf da dukan’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
7 Et les fils d’Israël fructifièrent et foisonnèrent, et multiplièrent, et devinrent extrêmement forts; et le pays en fut rempli.
amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
8 Et un nouveau roi se leva sur l’Égypte, qui n’avait point connu Joseph.
Sai wani sabon sarki wanda bai san Yusuf ba, ya hau sarautar Masar.
9 Et il dit à son peuple: Voici, le peuple des fils d’Israël est plus nombreux et plus fort que nous.
Ya ce wa mutanensa, “Duba Isra’ilawa sun yi yawa, sun fi ƙarfinmu.
10 Allons, soyons prudents à son égard, de peur qu’il ne se multiplie, et que, s’il arrivait une guerre, il ne se joigne, lui aussi, à nos ennemis, et ne fasse la guerre contre nous, et ne monte hors du pays.
Ku zo, mu yi dabara a kansu, in ba haka ba za su ƙaru fiye da haka, in kuwa yaƙi ya tashi tsakaninmu da abokan gāba, za su iya haɗa kai da abokan gāba, su yaƙe mu, su bar ƙasar.”
11 Et ils établirent sur lui des chefs de corvées pour l’opprimer par leurs fardeaux. Et il bâtit pour le Pharaon des villes à greniers, Pithom et Ramsès.
Saboda haka sai suka naɗa shugabannin gandu a kansu don su wahalshe su, su kuma bauta musu, suka sa su suka gina biranen Fitom da Rameses su zama biranen ajiya, domin Fir’auna.
12 Et selon qu’ils l’opprimaient, il multipliait et croissait; et ils eurent peur des fils d’Israël.
Amma duk da wannan ƙarin wulaƙancin da ake yi musu, su kuwa sai daɗa riɓaɓɓanya suke ta yi. Sai tsoron Isra’ilawa ya ƙaru a zuciyar Masarawa,
13 Et les Égyptiens firent servir les fils d’Israël avec dureté,
ganin haka sai Masarawa suka ƙara musu wahala.
14 et ils leur rendirent la vie amère par un dur service, en argile, et en briques, et par toute sorte de service aux champs: tout le service dans lequel on les faisait servir était avec dureté.
Suka baƙanta wa Isra’ilawa rai da bauta mai wuya, ta wurin sa su yin tubali da yumɓu, da kuma kowace irin bauta a gonaki. A cikin dukan ayyukansu, Masarawa ba su ji tausayinsu ba ko kaɗan.
15 Et le roi d’Égypte parla aux sages-femmes hébreues, dont l’une avait nom Shiphra et la seconde se nommait Pua,
Sai Sarkin Masar ya gaya wa ungozomomin matan Ibraniyawa, wato, su Shofra da Fuwa ya ce,
16 et il dit: Quand vous accoucherez les femmes hébreues et que vous les verrez sur les sièges, si c’est un fils, vous le ferez mourir, et si c’est une fille, elle vivra.
“Sa’ad da kuke taimakon matan Ibraniyawa lokacin haihuwa, in jaririn namiji ne ku kashe shi, amma in ta mace ce, ku bar ta da rai.”
17 Mais les sages-femmes craignirent Dieu, et ne firent pas comme le roi d’Égypte leur avait dit; et elles laissèrent vivre les enfants mâles.
Amma ungozomomin nan masu tsoron Allah ne, ba su kuwa aikata abin da sarkin Masar ya gaya musu ba; suka bar jarirai maza su rayu.
18 Et le roi d’Égypte appela les sages-femmes, et leur dit: Pourquoi avez-vous fait cela, et avez-vous laissé vivre les enfants mâles?
Sai sarkin Masar ya kira ungozomomin, ya tambaye su ya ce, “Don me kuka yi haka? Don me kuka bar jarirai maza su rayu?”
19 Et les sages-femmes dirent au Pharaon: Parce que les femmes hébreues ne sont pas comme les Égyptiennes; car elles sont vigoureuses: avant que la sage-femme vienne vers elles, elles ont enfanté.
Ungozoman suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Ai, matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gwarzaye ne, sukan haihu kafin ungozomomin su kai wurinsu.”
20 Et Dieu fit du bien aux sages-femmes; et le peuple multiplia, et devint très fort.
Saboda haka Allah ya nuna alheri wa ungozomomin, Isra’ilawa kuwa suka yi yawa fiye da dā.
21 Et il arriva, parce que les sages-femmes craignirent Dieu, qu’il leur fit des maisons.
Saboda ungozomomin suna tsoron Allah, sai Allah ya ba su iyalan kansu.
22 Et le Pharaon commanda à tout son peuple, disant: Tout fils qui naîtra, jetez-le dans le fleuve; mais toute fille, laissez-la vivre.
Sai Fir’auna ya ba da umarni wa mutanensa ya ce, “Duk yaron da yake namijin da haka haifa, dole ku jefa shi cikin kogi, amma ku bar yara mata su rayu.”

< Exode 1 >