< Amos 5 >
1 Écoutez cette parole, une complainte que j’élève sur vous, maison d’Israël!
Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
2 Elle est tombée, elle ne se relèvera pas, la vierge d’Israël; elle est étendue sur sa terre, il n’y a personne qui la relève.
“Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
3 Car ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: La ville qui allait en campagne avec 1 000, en aura 100 de reste; et celle qui allait en campagne avec 100, en aura dix de reste, pour la maison d’Israël.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
4 Car ainsi dit l’Éternel à la maison d’Israël: Cherchez-moi, et vous vivrez;
Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
5 et ne cherchez pas Béthel, et n’allez pas à Guilgal, et ne passez pas à Beër-Shéba; car Guilgal ira certainement en captivité, et Béthel sera réduite à rien.
kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
6 Cherchez l’Éternel, et vous vivrez, de peur qu’il n’envahisse comme le feu la maison de Joseph, et ne la dévore, et qu’il n’y ait personne à Béthel qui éteigne.
Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
7 Vous qui changez en absinthe le droit, et qui couchez par terre la justice,
Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
8 [cherchez-le], lui qui a fait les Pléiades et Orion; qui change en matin l’ombre de la mort, et transforme le jour en ténèbres de la nuit; qui appelle les eaux de la mer, et les verse sur la face de la terre: l’Éternel est son nom.
(Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
9 Il fait lever subitement la destruction sur le fort, et la destruction vient sur la forteresse.
yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
10 Ils haïssent celui qui reprend à la porte, et ont en abomination celui qui parle avec intégrité.
Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
11 C’est pourquoi, parce que vous foulez aux pieds le pauvre, et que vous prenez de lui des charges de blé: vous avez bâti des maisons de pierres de taille, mais vous n’y habiterez pas; vous avez planté des vignes excellentes, et vous n’en boirez pas le vin;
Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
12 car je connais vos nombreuses transgressions et vos grands péchés: ils oppriment le juste, prennent des présents, et font fléchir à la porte le droit des pauvres.
Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
13 C’est pourquoi, en ce temps-ci, le sage gardera le silence, car c’est un temps mauvais.
Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
14 Recherchez le bien, et non le mal, afin que vous viviez; et ainsi l’Éternel, le Dieu des armées, sera avec vous, comme vous le dites.
Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
15 Haïssez le mal, et aimez le bien, et établissez dans la porte le juste jugement; peut-être l’Éternel, le Dieu des armées, usera-t-il de grâce envers le reste de Joseph.
Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
16 C’est pourquoi, ainsi dit l’Éternel, le Dieu des armées, le Seigneur: Dans toutes les places, la lamentation! et dans toutes les rues, on dira: Hélas, hélas! Et on appellera le laboureur au deuil, et à la lamentation ceux qui s’entendent aux chants de douleur.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
17 Et dans toutes les vignes, la lamentation! car je passerai au milieu de toi, dit l’Éternel.
Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
18 Malheur à vous qui désirez le jour de l’Éternel! À quoi vous [servira] le jour de l’Éternel? Il sera ténèbres, et non lumière,
Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
19 comme si un homme s’enfuyait de devant un lion, et qu’un ours le rencontre; ou qu’il entre dans la maison et appuie sa main contre le mur, et qu’un serpent le morde.
Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
20 Le jour de l’Éternel n’est-il pas ténèbres, et non lumière? et profonde obscurité, et non splendeur?
Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
21 Je hais, je méprise vos fêtes, et je ne flairerai pas [de bonne odeur] dans vos assemblées solennelles;
“Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
22 si vous m’offrez des holocaustes et vos offrandes de gâteau, je ne les agréerai pas, et je ne regarderai pas le sacrifice de prospérités de vos bêtes grasses.
Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
23 Ôte de devant moi le bruit de tes cantiques; et la musique de tes luths, je ne l’écouterai pas.
Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
24 Mais que le jugement roule comme des eaux, et la justice comme un fleuve qui ne tarit pas!
Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
25 M’avez-vous offert des sacrifices et des offrandes dans le désert, pendant 40 ans, maison d’Israël?
“Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
26 Mais vous avez porté le tabernacle de votre Moloc, et le Kiun de vos images, l’étoile de votre dieu, que vous vous êtes fait;
Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
27 et je vous transporterai au-delà de Damas, dit l’Éternel; son nom est le Dieu des armées.
Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.