< Actes 24 >

1 Or cinq jours après, le souverain sacrificateur Ananias descendit avec les anciens et un certain orateur [nommé] Tertulle, et ils portèrent plainte devant le gouverneur contre Paul.
Bayan kwanaki biyar, sai Ananiyas babban firist, Wasu dattawa da wani masanin shari'a mai suna Tartilus, sun tafi can. Suka kai karar Bulus gaban gwamna.
2 Et quand celui-ci eut été appelé, Tertulle se mit à l’accuser, disant: Puisque nous jouissons par ton moyen d’une grande tranquillité, et que par ta prévoyance des mesures excellentes sont prises en vue de cette nation,
Lokacin da Bulus ya tsaya gaban gwamna, Tartilus ya fara zarginsa yace wa gwamnan, “Saboda kai mun sami zaman lafiya; sa'annan hangen gabanka ya kawo gyara a kasarmu;
3 très excellent Félix, nous l’acceptons, en tout et partout, avec une entière gratitude.
don haka duk abin da ka yi mun karba da godiya, ya mai girma Filikus.
4 Mais afin de ne pas t’arrêter davantage, je te prie de nous entendre brièvement selon ta clémence;
Domin kada in wahalsheka, ina roko a yi mani nasiha don in yi magana kadan.
5 car nous avons trouvé que cet homme est une peste, et qu’il excite des séditions parmi tous les Juifs dans toute la terre habitée, et qu’il est un meneur de la secte des Nazaréens;
An iske mutumin nan yana barna irir iri, yana kuma zuga jama'ar Yahudawa a dukan duniya su yi tayarwa.
6 il a même tenté de profaner le temple: aussi l’avons-nous saisi, [et nous avons voulu le juger selon notre loi;
Har ma ya yi kokarin kazantar da haikali; saboda haka muka kama shi. [Mun so mu shari'anta masa bisa ga dokarmu.]
7 mais Lysias, le chiliarque, étant survenu, l’a emmené en l’arrachant d’entre nos mains avec une grande violence,
Amma Lisiyas jami'i ya zo ya kwace shi da karfi daga hannunmu.
8 donnant ordre que ses accusateurs viennent auprès de toi]; et par lui tu pourras toi-même, en l’interrogeant, arriver à la pleine connaissance de toutes ces choses dont nous l’accusons.
Idan ka binciki Bulus game da wadannan al'amura, kai ma, zai tabbatar maka abin da muke zarginsa a kai.
9 Et les Juifs aussi se joignirent à lui pour insister contre [Paul], affirmant que les choses étaient ainsi.
Dukan Yahudawa suna zargin Bulus cewa wadannan abubuwa gaskiya ne.
10 Et Paul, après que le gouverneur lui eut fait signe de parler, répondit: Sachant que depuis plusieurs années tu es juge de cette nation, je fais mon apologie avec plus de courage:
lokacin da gwamnan ya alamta wa Bulus ya yi magana sai yace, “Yanzu na fahimci cewar da dadewa kana mulkin kasarnan, don haka da farin ciki zan yi maka bayani.
11 car tu peux connaître qu’il ne s’est pas passé plus de douze jours depuis que je suis monté pour adorer à Jérusalem.
Zaka iya tabbatarwa cewa bai kai kwana sha biyu ba tun da nake zuwa Urushalima don yin sujada.
12 Et ils ne m’ont trouvé, ni dans le temple, disputant avec quelqu’un ou ameutant la foule, ni dans les synagogues, ni dans la ville;
Da suka same ni a haikali, ban yi jayayya ko kawo rudami a tsakanin jama'a ba.
13 et ils ne peuvent pas soutenir les choses dont ils m’accusent présentement.
Don haka ba su da tabbas akan abinda suke zargina a kansa yau.
14 Mais je te confesse bien ceci, que, selon la voie qu’ils appellent secte, ainsi je sers le Dieu de mes pères, croyant toutes les choses qui sont écrites dans la loi et dans les prophètes,
Amma na sanar da kai, bisa ga abin da suke kira darika, haka ni ma nake bautawa Allah na kakanninmu. Na yi aminci wajen kiyaye dukan abin da ke a rubuce a Attaurat da litattafan annabawa.
15 ayant espérance en Dieu, – [espérance] que ceux-ci nourrissent aussi eux-mêmes, – qu’il y aura une résurrection, tant des justes que des injustes.
Ina sa bege ga Allah, kamar yadda za a yi tashin matattu, masu adalci da miyagu;
16 À cause de cela, moi aussi je m’exerce à avoir toujours une conscience sans reproche devant Dieu et devant les hommes.
a kan haka kuma, nake kokarin zama mara abin zargi a gaban Allah da mutane ina yin haka cikin dukan al'amura.
17 Or, après plusieurs années, je suis venu pour faire des aumônes à ma nation et des offrandes.
Bayan wadansu shekaru na zo in kawo wasu sadakoki da baikon yardar rai.
18 Sur ces entrefaites, ils me trouvèrent purifié dans le temple, sans attroupement et sans tumulte.
Cikin kudurin yin haka, sai wasu Yahudawa daga kasar Asiya suka iske ni a cikin ka'idodin tsarkakewa a haikali, ba da taro ko ta da hargitsi ba.
19 Or c’étaient certains Juifs d’Asie, qui auraient dû être ici devant toi et m’accuser, s’ils avaient quelque chose contre moi;
Yakamata wadannan mutanen su zo gabarka a yau, har idan suna da wani zargi a kai na.
20 ou bien, que ceux-ci eux-mêmes disent quelle injustice ils ont trouvée en moi, quand j’ai été devant le sanhédrin,
In kuwa ba haka ba bari mutanennan su fada in sun taba iske ni da wani aibu a duk lokacin da na gurfana a gaban majalisar Yahudawa;
21 si ce n’est ce seul cri que je fis entendre, étant au milieu d’eux: C’est pour la résurrection des morts que je suis aujourd’hui mis en jugement par vous.
sai dai ko a kan abu daya da na fada da babbar murya sa'adda na tsaya a gabansu, 'Wato batun tashin matattu wanda ake tuhumata ake neman yi mani hukunci yau.'”
22 Mais Félix, ayant plus exactement connaissance de ce qui regardait la voie, les ajourna, disant: Quand le chiliarque Lysias sera descendu, je prendrai connaissance de votre affaire,
Filikus yana da cikakken sanin tafarkin Hanyar, shi yasa ya daga shari'ar. Yace da su, “Duk sa'anda Lisiyas mai ba da umarni ya zo daga Urushalima, zan yanke hukunci.”
23 – ordonnant au centurion que [Paul] soit gardé, et qu’il ait [quelque] liberté, et qu’on n’empêche aucun des siens de le servir.
Sa'annan ya umarci jarumin ya lura da Bulus, amma ya yi sassauci, kada ya hana abokansa su ziyarce shi ko su taimake shi.
24 Or quelques jours après, Félix étant venu avec Drusille sa femme qui était Juive, fit venir Paul et l’entendit sur la foi en Christ.
Bayan wadansu kwanaki, Filikus da mai dakinsa Druskila, ita Bayahudiya ce, ya kuma aika a kira Bulus ya saurare shi game da bangaskiya cikin Kristi Yesu.
25 Et comme il discourait sur la justice et sur la tempérance et sur le jugement à venir, Félix tout effrayé répondit: Pour le présent va-t’en; quand je trouverai un moment convenable, je te ferai appeler,
Amma sa'adda Bulus yake bayyana zancen adalci, kamunkai, da hukunci mai zuwa, Filikus ya firgita ya ce, “Yanzu ka tafi. Amma idan na sami zarafi an jima, zan sake neman ka.”
26 – espérant en même temps que Paul lui donnerait quelque argent; c’est pourquoi aussi il le faisait venir souvent et s’entretenait avec lui.
A wannan lokacin, yasa zuciya Bulus zai bashi kudi, yayi ta nemansa akai-akai domin yayi magana da shi.
27 Or, quand deux ans furent accomplis, Félix eut pour successeur Porcius Festus; et, voulant gagner la faveur des Juifs, Félix laissa Paul prisonnier.
Bayan shekaru biyu, Borkiyas Festas ya zama gwamna bayan Filikus, domin neman farin jini a wurin Yahudawa, ya ci gaba da tsaron Bulus a gidan yari.

< Actes 24 >