< 2 Samuel 23 >
1 Et ce sont ici les dernières paroles de David. David, le fils d’Isaï, a dit, et l’homme haut placé, l’oint du Dieu de Jacob, et le doux psalmiste d’Israël, a dit:
Waɗannan su ne kalmomin Dawuda na ƙarshe. “Abubuwan da Dawuda ɗan Yesse ya yi magana a kai, abubuwan da mutumin da Mafi Ɗaukaka ya girmama. Mutumin da Allah na Yaƙub ya zaɓa yă zama sarki, wanda kuma yake mawaƙi waƙoƙin Isra’ila.
2 L’Esprit de l’Éternel a parlé en moi, et sa parole a été sur ma langue.
“Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina; maganarsa tana a harshena.
3 Le Dieu d’Israël a dit, le Rocher d’Israël m’a parlé: Celui qui domine parmi les hommes sera juste, dominant en la crainte de Dieu,
Allah na Isra’ila ya yi magana, Dutsen Isra’ila ya ce mini, ‘Sa’ad da wani ya yi mulkin mutane da adalci, sa’ad da ya yi mulki da tsoron Allah,
4 et il sera comme la lumière du matin, quand le soleil se lève, un matin sans nuages: par sa clarté l’herbe tendre [germe] de la terre après la pluie.
yana kama da hasken safiya a safiya marar girgije, kamar haske bayan ruwan sama da yakan sa ciyawa ta tsiro daga ƙasa.’
5 Quoique ma maison ne soit pas ainsi avec Dieu, cependant il a établi avec moi une alliance éternelle, à tous égards bien ordonnée et assurée, car c’est là tout mon salut et tout mon plaisir, quoiqu’il ne la fasse pas germer.
“Ashe, gidana bai daidaita da Allah ba? Ashe, Allah bai yi madawwamiyar yarjejjeniya da ni shiryayye da ɗaurarre a kowane sashi ba? Ba zai kawo ga cikar cetona yă kuma biya duk bukatuna ba?
6 Mais [les fils de] Bélial sont tous comme des épines qu’on jette loin, car on ne les prend pas avec la main,
Amma za a jefar da masu mugunta duka kamar ƙayayyuwan da ba a tattara da hannu.
7 Et l’homme qui les touche se munit d’un fer ou d’un bois de lance; et ils seront entièrement brûlés par le feu sur le lieu même.
Duk wanda ya taɓa ƙaya yakan yi amfani da wani ƙarfe ne ko sandar māshi; akan ƙone su inda suke a zube.”
8 Ce sont ici les noms des hommes forts qu’avait David: Josheb-Bashébeth, Thacmonite, chef des principaux capitaines; c’était Adino, l’Etsnite, qui eut le dessus sur 800 hommes, qu’il tua en une fois.
Waɗannan su ne sunayen jarumawan Dawuda. Yosheb-Basshebet, mutumin Takemon ɗaya daga cikin shugabanni Uku; ya ɗaga māshinsa ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci guda.
9 Et après lui, Éléazar, fils de Dodo, fils d’un Akhokhite; il était l’un des trois hommes forts qui étaient avec David, lorsqu’ils avaient défié les Philistins qui s’étaient assemblés là pour combattre, et que les hommes d’Israël étaient montés.
Na biye da shi a matsayi cikin jarumawa ukun nan, shi ne Eleyazar ɗan Dodo, mutumin Aho. Eleyazar ya kasance tare da Dawuda sa’ad da suka fuskanci Filistiyawa waɗanda suka taru a Fas Dammim don yaƙi. Mutanen Isra’ila suka gudu,
10 Il se leva, et frappa les Philistins, jusqu’à ce que sa main fut lasse et que sa main demeura attachée à l’épée; et l’Éternel opéra une grande délivrance ce jour-là; et le peuple revint après [Éléazar], seulement pour piller.
amma ya yi tsayi daka, ya bugi Filistiyawa sai da hannunsa ya gaji har ya liƙe wa māshinsa. Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara a ranar. Sauran sojoji suka komo wurin Eleyazar, don kawai su washe ganima.
11 Et après lui, Shamma, fils d’Agué, Hararite: les Philistins s’étaient assemblés en troupe; et il y avait là une portion de champ pleine de lentilles, et le peuple avait fui devant les Philistins:
Na biye da Agiyi a matsayi, shi ne Shamma ɗan Agi, mutumin Harar. Sa’ad da Filistiyawa suka taru a wani wurin da take gona cike da waken barewa, sai rundunar Isra’ila suka gudu daga Filistiyawa.
12 et il se plaça au milieu du champ, et le sauva, et frappa les Philistins; et l’Éternel opéra une grande délivrance.
Amma Shamma ya yi tsayi daka a tsakiyar gonar. Ya kāre ta, ya kuma bugi Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara.
13 Et trois des trente chefs descendirent et vinrent au temps de la moisson vers David, dans la caverne d’Adullam, comme une troupe de Philistins était campée dans la vallée des Rephaïm.
A lokacin girbi, uku daga cikin shugabanni talatin suka gangaro zuwa wurin Dawuda a kogon Adullam. A lokacin kuwa sojojin Filistiyawa sun kafa sansani a Kwarin Refayim.
14 Et David était alors dans le lieu fort, et il y avait alors un poste des Philistins à Bethléhem.
Dawuda kuwa yana a mafaka. Wata ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuma suna Betlehem.
15 Et David convoita, et dit: Qui me fera boire de l’eau du puits de Bethléhem, qui est près de la porte?
Dawuda ya ji ƙishirwa, sai ya ce, “Kash, da a ce wani yă samo mini ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem mana!”
16 Et les trois hommes forts forcèrent le passage à travers le camp des Philistins, et puisèrent de l’eau du puits de Bethléhem, qui est près de la porte, et la prirent et l’apportèrent à David; et il ne voulut pas la boire, mais il en fit une libation à l’Éternel.
Sai jarumawa ukun nan suka yi kukan ƙura, suka sheƙa a guje suka ratsa cikin sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem, suka kawo wa Dawuda. Amma Dawuda ya ƙi yă sha; a maimako sai ya zuba shi a gaban Ubangiji.
17 Et il dit: Loin de moi, Éternel, que je fasse cela! N’est-ce pas le sang des hommes qui sont allés au péril de leur vie? Et il ne voulut pas la boire. Ces trois hommes forts firent cela.
Sai ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe, in yi sha! Ba jinin mutanen da suka tafi a bakin ransu ba ne?” Dawuda kuwa bai sha ruwan ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
18 Et Abishaï, frère de Joab, fils de Tseruïa, était chef de trois; il leva sa lance contre 300 hommes, qu’il tua. Et il eut un nom parmi les trois.
Abishai, ɗan’uwan Yowab, ɗan Zeruhiya shi shugaban Ukun nan. Ya ɗauki māshinsa ya kashe mutane ɗari uku, ta haka ya zama sananne kamar Ukun nan.
19 Ne fut-il pas le plus honoré des trois? Et il fut leur chef; mais il n’atteignit pas les trois [premiers].
Ashe, ba a girmama shi fiye da Ukun ba? Ya zama komandansu, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
20 Et Benaïa, fils de Jehoïada, fils d’un homme vaillant, de Kabtseël, grand en exploits, lui, frappa deux lions de Moab; et il descendit, et frappa le lion dans une fosse, par un jour de neige.
Benahiya, ɗan Yehohiyada mutumin Kabzeyel shi ma jarumi ne sosai, ya yi nasarori masu yawa. Ya bugi ƙwararrun jarumawan Mowab guda biyu. Ya kuma shiga rami wata ranar da ake ƙanƙara, ya kashe zaki.
21 Et c’est lui qui frappa un homme égyptien qui était de grande apparence, et l’Égyptien avait en sa main une lance; et il descendit vers lui avec un bâton, et arracha la lance de la main de l’Égyptien, et le tua avec sa propre lance.
Ya kuma buge wani jibgaggen mutumin Masar. Duk da māshin da mutumin Masar yana riƙe a hannunsa, Benahiya ya kai masa hari da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannunsa, ya kuma kashe shi da māshin.
22 Voilà ce que fit Benaïa, fils de Jehoïada; et il eut un nom parmi les trois hommes forts:
Irin nasarorin da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma jarumi ne sosai kamar jarumawan nan uku.
23 il fut plus honoré que les trente, mais il n’atteignit pas les trois [premiers]. Et David lui donna une place dans ses audiences privées.
Aka fi ba shi girma fiye da talatin ɗin nan, amma ba ya cikin ukun. Dawuda ya sa shi yă zama ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa.
24 Asçaël, frère de Joab, était des trente; Elkhanan, fils de Dodo, de Bethléhem;
Cikin talatin ɗin kuwa akwai, Asahel, ɗan’uwan Yowab, Elhanan, ɗan Dodo mutumin Betlehem,
25 Shamma, le Harodite; Élika, le Harodite;
Shamma, mutumin Harod, Elika, mutumin Harod,
26 Hélets, le Paltite; Ira, fils d’Ikkesh, le Thekohite;
Helez, mutumin Falti, Ira, ɗan Ikkesh mutumin Tekowa,
27 Abiézer, l’Anathothite; Mebunnaï, le Hushathite;
Abiyezer, mutumin Anatot, da Mebunnai, mutumin Husha,
28 Tsalmon, l’Akhokhite; Maharaï, le Netophathite;
Zalmon, mutumin Aho, da Maharai, mutumin Netofa,
29 Héleb, fils de Baana, le Netophathite; Itthaï, fils de Ribaï, de Guibha des fils de Benjamin;
Heleb, ɗan Ba’ana daga Netofa, Ittai, ɗan Ribai mutumin Gibeya a Benyamin,
30 Benaïa, le Pirhathonite; Hiddaï, des torrents de Gaash;
Benahiya, mutumin Firaton, da Hiddai, daga rafuffukan Ga’ash,
31 Abi-Albon, l’Arbathite; Azmaveth, le Barkhumite;
Abi-Albon, mutumin Arba, da Azmawet, mutumin Bahurim,
32 Éliakhba, le Shaalbonite; Bené-Jashen; Jonathan;
Eliyaba, mutumin Sha’albo,’Ya’yan Yashen, Yonatan,
33 Shamma, l’Hararite; Akhiam, fils de Sharar, l’Ararite;
ɗan Shamma mutumin Harar, da Ahiyam, ɗan Sharar mutumin Harod.
34 Éliphéleth, fils d’Akhasbaï, fils d’un Maacathien; Éliam, fils d’Akhitophel, le Guilonite;
Elifelet, ɗan Ahasbai mutumin Ma’aka, Eliyam, ɗan Ahitofel mutumin Gilo,
35 Hetsraï, le Carmélite; Paaraï, l’Arbite;
Hezro, mutumin Karmel, Fa’arai, mutumin Arbi,
36 Jighal, fils de Nathan, de Tsoba; Bani, le Gadite;
Igal, ɗan Natan mutumin Zoba, ɗan Hagiri,
37 Tsélek, l’Ammonite; Nakharaï, le Beérothien, qui portait les armes de Joab, fils de Tseruïa;
Zelek, mutumin Ammon Naharai, mutumin Beyerot mai ɗaukan wa Yowab, ɗan Zeruhiya makamai,
38 Ira, le Jéthrien; Gareb, le Jéthrien;
Ira, mutumin Itra. Gareb, mutumin Itra,
39 Urie, le Héthien: en tout, 37.
da kuma Uriya, mutumin Hitti. Su talatin da bakwai ne duka.