< 2 Samuel 22 >
1 Et David adressa à l’Éternel les paroles de ce cantique, le jour où l’Éternel l’eut délivré de la main de tous ses ennemis et de la main de Saül.
Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
2 Et il dit: L’Éternel est mon rocher et mon lieu fort, et celui qui me délivre.
Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
3 Dieu est mon rocher, je me confierai en lui, mon bouclier et la corne de mon salut, ma haute retraite et mon refuge. Mon Sauveur, tu me sauveras de la violence!
Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
4 Je crierai à l’Éternel, qui est digne d’être loué, et je serai sauvé de mes ennemis.
“Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
5 Car les vagues de la mort m’ont environné, les torrents de Bélial m’ont fait peur;
Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
6 Les cordeaux du shéol m’ont entouré, les filets de la mort m’ont surpris: (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol )
7 Dans ma détresse, j’ai invoqué l’Éternel, et j’ai appelé mon Dieu, et, de son temple, il a entendu ma voix, et mon cri est [parvenu] à ses oreilles.
“A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
8 Alors la terre fut ébranlée et trembla; les fondements des cieux furent secoués et furent ébranlés, parce qu’il était irrité.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
9 Une fumée montait de ses narines, et un feu sortant de sa bouche dévorait; des charbons en jaillissaient embrasés.
Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
10 Et il abaissa les cieux, et descendit; et il y avait une obscurité profonde sous ses pieds.
Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
11 Et il était monté sur un chérubin, et volait, et il parut sur les ailes du vent.
Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
12 Et il mit autour de lui les ténèbres pour tente, des amas d’eaux, d’épaisses nuées de l’air.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
13 De la splendeur qui était devant lui jaillissaient, embrasés, des charbons de feu.
Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
14 L’Éternel tonna des cieux, et le Très-haut fit retentir sa voix.
Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
15 Et il tira des flèches et dispersa [mes ennemis]; [il lança] l’éclair, et les mit en déroute.
Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
16 Alors les lits de la mer parurent, les fondements du monde furent mis à découvert, quand l’Éternel les tançait par le souffle du vent de ses narines.
Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
17 D’en haut, il étendit [sa main], il me prit, il me tira des grandes eaux;
“Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
18 Il me délivra de mon puissant ennemi, de ceux qui me haïssaient; car ils étaient plus forts que moi.
Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
19 Ils m’avaient surpris au jour de ma calamité, mais l’Éternel fut mon appui.
Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
20 Et il me fit sortir au large, il me délivra, parce qu’il prenait son plaisir en moi.
Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
21 L’Éternel m’a récompensé selon ma justice, il m’a rendu selon la pureté de mes mains;
“Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
22 Car j’ai gardé les voies de l’Éternel, et je ne me suis point méchamment détourné de mon Dieu;
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
23 Car toutes ses ordonnances ont été devant moi; et de ses statuts, je ne me suis pas écarté;
Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
24 Et j’ai été parfait envers lui, et je me suis gardé de mon iniquité.
Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
25 Et l’Éternel m’a rendu selon ma justice, selon ma pureté devant ses yeux.
Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
26 Avec celui qui use de grâce, tu uses de grâce; avec l’homme parfait, tu te montres parfait;
“Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
27 Avec celui qui est pur, tu te montres pur; et avec le pervers, tu es roide.
ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
28 Et tu sauveras le peuple affligé, et tes yeux sont sur les hautains, [et] tu les abaisses.
Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
29 Car toi, Éternel! tu es ma lampe; et l’Éternel fait resplendir mes ténèbres.
Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
30 Car, par toi, je courrai au travers d’une troupe; par mon Dieu, je franchirai une muraille.
Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
31 Quant à Dieu, sa voie est parfaite; la parole de l’Éternel est affinée; il est un bouclier à tous ceux qui se confient en lui.
“Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
32 Car qui est Dieu, hormis l’Éternel? et qui est un rocher, hormis notre Dieu?
Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
33 Dieu est ma puissante forteresse, et il aplanit parfaitement ma voie.
Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
34 Il rend mes pieds pareils à ceux des biches, et me fait tenir debout sur mes lieux élevés.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
35 Il enseigne mes mains à combattre; et mes bras bandent un arc d’airain.
Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
36 Et tu m’as donné le bouclier de ton salut, et ta débonnaireté m’a agrandi.
Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
37 Tu as mis au large mes pas sous moi, et les chevilles de mes pieds n’ont pas chancelé.
Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
38 J’ai poursuivi mes ennemis, et je les ai détruits; et je ne m’en suis pas retourné que je ne les aie consumés.
“Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
39 Et je les ai consumés, je les ai transpercés, et ils ne se sont pas relevés, mais ils sont tombés sous mes pieds.
Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
40 Et tu m’as ceint de force pour le combat; tu as courbé sous moi ceux qui s’élevaient contre moi.
Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
41 Et tu as fait que mes ennemis m’ont tourné le dos; et ceux qui me haïssaient, je les ai détruits.
Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
42 Ils regardaient, et il n’y avait point de sauveur; [ils regardaient] vers l’Éternel, et il ne leur a pas répondu.
Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
43 Et je les ai brisés menu comme la poussière de la terre; comme la boue des rues, je les ai écrasés, je les ai foulés.
Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
44 Et tu m’as délivré des débats de mon peuple; tu m’as gardé pour être le chef des nations; un peuple que je ne connaissais pas me servira.
“Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
45 Les fils de l’étranger se sont soumis à moi en dissimulant; dès qu’ils ont entendu de leur oreille, ils m’ont obéi.
baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
46 Les fils de l’étranger ont dépéri, et ils sont sortis en tremblant de leurs lieux cachés.
Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
47 L’Éternel est vivant; et que mon Rocher soit béni! Et que Dieu, le rocher de mon salut, soit exalté,
“Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
48 Le Dieu qui m’a donné des vengeances, et qui a amené les peuples sous moi,
Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
49 Et qui m’a fait sortir du milieu de mes ennemis. Tu m’as élevé au-dessus de ceux qui s’élèvent contre moi, tu m’as délivré de l’homme violent.
wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
50 C’est pourquoi, Éternel! je te célébrerai parmi les nations, et je chanterai des cantiques à [la gloire de] ton nom.
Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
51 [C’est lui] qui a donné de grandes délivrances à son roi, et qui use de bonté envers son oint, envers David, et envers sa semence, à toujours.
“Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”