< 2 Rois 9 >

1 Et Élisée, le prophète, appela un des fils des prophètes, et lui dit: Ceins tes reins, et prends cette fiole d’huile en ta main, et va-t’en à Ramoth de Galaad.
Sai Elisha ya kira wani daga cikin ƙungiyar annabawa, ya ce masa, “Ka sha ɗamara, ka ɗauki wannan kwalabar mai ka je Ramot Gileyad.
2 Et entre là, et vois-y Jéhu, fils de Josaphat, fils de Nimshi; et tu entreras, et tu le feras lever du milieu de ses frères, et tu le mèneras dans une chambre intérieure.
Da ka isa can, ka nemi Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi. Ka je wurinsa, ka ja shi gefe daga abokansa, ka shiga da shi ɗaki na ciki.
3 Et tu prendras la fiole d’huile, et tu la verseras sur sa tête, et tu diras: Ainsi dit l’Éternel: Je t’oins roi sur Israël. Et tu ouvriras la porte, et tu t’enfuiras, et tu n’attendras pas.
Sa’an nan ka ɗauki kwalabar man ka zuba a kansa, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, na naɗa ka sarkin Isra’ila.’ Sa’an nan ka buɗe ƙofa ka ruga a guje; kada ka ɓata lokaci!”
4 Et le jeune homme, le jeune prophète, s’en alla à Ramoth de Galaad.
Sai saurayin nan, annabi, ya tafi Ramot Gileyad.
5 Et il entra, et voici, les chefs de l’armée étaient assis; et il dit: Chef, j’ai une parole pour toi. Et Jéhu dit: Pour qui de nous tous? Et il dit: Pour toi, chef.
Da ya isa can, sai ya tarar da hafsoshin soji zaune a wuri guda. Sai ya ce, “Ina da saƙo dominka komanda.” Sai Yehu ya ce, “Wanne a cikinmu?” Sai ce, “Dominka, komanda.”
6 Et [Jéhu] se leva, et entra dans la maison. Et [le jeune homme] versa l’huile sur sa tête, et lui dit: Ainsi dit l’Éternel, le Dieu d’Israël: Je t’oins roi sur le peuple de l’Éternel, sur Israël;
Sai Yehu ya tashi ya shiga cikin gida. Sa’an nan annabin ya zuba wa Yehu mai a kā, ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na naɗa ka sarki a bisa jama’ar Ubangiji, wato, Isra’ila.
7 et tu frapperas la maison d’Achab, ton seigneur; et je vengerai, de la main de Jézabel, le sang de mes serviteurs les prophètes et le sang de tous les serviteurs de l’Éternel.
Za aka hallaka gidan Ahab maigidanka, zan kuma ɗauki fansar jinin bayina annabawa da kuma jinin dukan bayin Ubangiji da Yezebel ta zub da.
8 Et toute la maison d’Achab périra; et je retrancherai à Achab tous les mâles, l’homme lié et l’homme libre en Israël;
Dukan gidan Ahab zai hallaka. Zan kashe dukan’ya’yan Ahab maza a Isra’ila, bayi ko’yantattu.
9 et je rendrai la maison d’Achab semblable à la maison de Jéroboam, fils de Nebath, et à la maison de Baësha, fils d’Akhija;
Zan mai da gidan Ahab kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat da kuma kamar gidan Ba’asha ɗan Ahiya.
10 et les chiens mangeront Jézabel dans le champ de Jizreël, et il n’y aura personne qui l’enterre. Et il ouvrit la porte et s’enfuit.
Game da Yezebel kuwa, karnuka za su cinye ta a fili a Yezireyel, ba kuwa wanda zai binne ta.’” Sa’an nan ya buɗe ƙofa ya ruga a guje.
11 Et Jéhu sortit vers les serviteurs de son seigneur, et on lui dit: Tout va-t-il bien? Pourquoi ce fou est-il venu vers toi? Et il leur dit: Vous connaissez l’homme et sa pensée.
Da Yehu ya koma wurin sauran hafsoshin sai ɗaya daga cikinsu ya tambaye shi, “Lafiya? Me ya kawo wannan mahaukaci a wurinka?” Sai Yehu ya ce, “Ka san mahaukacin nan da irin maganganunsa.”
12 Et ils dirent: Mensonge! Dis-le-nous donc. Et il dit: Il m’a parlé de telle et telle manière, disant: Ainsi dit l’Éternel: Je t’ai oint roi sur Israël.
Suka ce masa, “Ba gaskiya ba ne, ka dai faɗa mana.” Yehu ya ce, “Ga abin da ya ce mini, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, na naɗa ka sarki a bisa Isra’ila.’”
13 Et ils se hâtèrent, et prirent chacun son vêtement, et les mirent sous lui sur les degrés mêmes; et ils sonnèrent de la trompette, et dirent: Jéhu est roi!
Sai suka yi sauri suka ɗauki rigunansu suka shimfiɗa a ƙasa, suka busa kakaki, suka yi ihu, suka ce, “Yehu ne sarki.”
14 Et Jéhu, fils de Josaphat, fils de Nimshi, conspira contre Joram. (Et Joram gardait Ramoth de Galaad, lui et tout Israël, à cause de Hazaël, roi de Syrie.
Saboda haka, Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi, ya ƙulla wa Yoram maƙarƙashiya (To, Yoram da dukan Isra’ila suna kāre Ramot Gileyad daga Hazayel sarkin Aram,
15 Et le roi Joram s’en était retourné à Jizreël pour se faire guérir des blessures que les Syriens lui avaient faites lorsqu’il combattait contre Hazaël, roi de Syrie.) Et Jéhu dit: Si c’est votre pensée, que personne ne s’échappe de la ville et ne sorte pour aller raconter [la nouvelle] à Jizreël.
amma Sarki Yoram ya koma Yezireyel don yă farfaɗo daga raunukan da Arameyawa suka ji masa a wata gabzawar da ya yi da Hazayel sarkin Aram.) Yehu ya ce, “In haka kuke ji, kada ku bar wani yă sulluɓe daga birnin yă kai labarin Yezireyel.”
16 Et Jéhu monta en char, et s’en alla à Jizreël, car Joram y était alité; et Achazia, roi de Juda, était descendu pour voir Joram.
Sai ya tashi ya ɗauki keken yaƙinsa ya tafi Yezireyel gama Yoram yana hutawa a can. Ga kuma Ahaziya sarkin Yahuda ya je don yă gan shi.
17 Et la sentinelle se tenait sur la tour à Jizreël, et vit la troupe de Jéhu, comme il arrivait, et dit: Je vois une troupe [de gens]. Et Joram dit: Prends un cavalier, et envoie-le à leur rencontre, et qu’il dise: Est-ce la paix?
Mai tsaro kuwa yana tsaye a kan hasumiya a Yezireyel, sai ya hangi rundunar Yehu sa’ad da yake zuwa. Ya ce, “Na ga wata runduna.” Sai Yoram ya umarta, “Nemi mahayin doki a aike shi yă tarye su, yă kuma tambaye su, ‘Lafiya?’”
18 Et l’homme à cheval partit à sa rencontre, et dit: Ainsi a dit le roi: Est-ce la paix? Et Jéhu dit: Qu’as-tu à faire de la paix? Tourne, [et passe] derrière moi. Et la sentinelle annonça, disant: Le messager est venu jusqu’à eux, et il ne revient pas.
Sai mahayin dokin ya hau, ya ruga, ya taryi Yehu, ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Sai Yehu ya ce masa, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.” Sai mai tsaron ya ce wa sarki, “Ɗan saƙon ya kai wurinsu, amma ba ya dawowa.”
19 Et il envoya un second homme à cheval; et il vint à eux, et dit: Ainsi dit le roi: Est-ce la paix? Et Jéhu dit: Qu’as-tu à faire de la paix? Tourne, [et passe] derrière moi.
Saboda haka sarki ya sāke aika mahayin doki na biyu. Sa’ad da ya isa wurinsu sai ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Yehu ya ce, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.”
20 Et la sentinelle annonça, disant: Il est venu jusqu’à eux, et ne revient pas. Et la manière de conduire est celle de Jéhu, fils de Nimshi; car il conduit avec furie.
Mai tsaro ya sāke cewa, “Ya kai wurinsu, amma shi ma ba ya dawowa. Ina ganin sukuwar kamar irin ta Yehu, jikan Nimshi, gama yakan yi sukuwa kamar mahaukaci.”
21 Et Joram dit: Qu’on attelle. Et on attela son char. Et Joram, roi d’Israël, sortit, et Achazia, roi de Juda, chacun dans son char; et ils sortirent à la rencontre de Jéhu, et le trouvèrent dans le champ de Naboth, Jizreélite.
Yoram ya umarta, “Haɗa mini keken yaƙi!” Da aka haɗa, sai Yoram sarkin Isra’ila, da Ahaziya sarkin Yahuda, suka hau suka tafi, kowa a keken yaƙinsa, don su taryi Yehu. Suka sadu da shi a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel.
22 Et il arriva que, quand Joram vit Jéhu, il dit: Est-ce la paix, Jéhu? Et il dit: Quelle paix, … aussi longtemps que les prostitutions de Jézabel, ta mère, et ses enchantements sont en si grand nombre?
Sa’ad da Yoram ya ga Yehu sai ya tambaye shi, “Lafiya kuwa ka zo, Yehu?” Yehu ya ce, “Ina kuwa lafiya, da yake dukan bautar gumaka da bokancin mahaifiyarka Yezebel sun bazu ko’ina?”
23 Et Joram tourna sa main, et s’enfuit, et dit à Achazia: Trahison, Achazia!
Yoram ya juya, ya gudu, yana ce wa Ahaziya, “Cin amana, Ahaziya!”
24 Et Jéhu prit son arc en main, et frappa Joram entre les bras, et la flèche sortit au travers de son cœur; et il s’affaissa dans son char.
Sai Yehu ya ja bakansa ya harbi Yoram a tsakanin kafaɗunsa. Kibiyar ta same shi a zuciyarsa sai ya fāɗi a cikin keken yaƙinsa.
25 Et [Jéhu] dit à Bidkar, son lieutenant: Prends-le, [et] jette-le dans la portion de champ de Naboth, le Jizreélite; car souviens-toi que, quand moi et toi, nous étions en char tous les deux, à la suite d’Achab, son père, l’Éternel prononça cet oracle contre lui:
Yehu ya ce wa Bidkar, hafsan keken yaƙinsa, “Ka ɗauke shi ka jefar a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel. Ka tuna yadda ni da kai muke a kekunan yaƙi a bayan Ahab mahaifinsa sa’ad da Ubangiji ya yi wannan annabci game da shi,
26 N’ai-je pas vu hier le sang de Naboth et le sang de ses fils, dit l’Éternel? et je te le rendrai dans ce champ-ci, dit l’Éternel. Et maintenant, prends-le [et] jette-le dans le champ, selon la parole de l’Éternel.
‘Jiya na ga jinin Nabot da jinin’ya’yansa, in ji Ubangiji, kuma ba shakka zan ɗauki fansa a wannan fili, in ji Ubangiji.’ Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar da shi a bisa wannan fegi, bisa ga faɗin Ubangiji. Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar a filin, in ji Ubangiji.”
27 Et Achazia, roi de Juda, vit [cela], et s’enfuit par le chemin de la maison du jardin; et Jéhu le poursuivit, et dit: Frappez-le, lui aussi, sur le char. [Ils le frappèrent] à la montée de Gur, qui est près de Jibleam; et il s’enfuit à Meguiddo, et y mourut.
Sa’ad da Ahaziya sarkin Yahuda ya ga abin da ya faru, sai ya haura hanyar Bet Haggan a guje. Yehu ya bi shi yana ihu, “A kashe shi, shi ma!” Suka ji masa rauni a keken yaƙinsa a hanya zuwa Gur, kusa da Ibileyam amma ya tsere zuwa Megiddo ya mutu a can.
28 Et ses serviteurs le transportèrent sur un char à Jérusalem, et l’enterrèrent dans son sépulcre, avec ses pères, dans la ville de David.
Barorinsa suka ɗauke shi cikin keken yaƙi zuwa Urushalima suka binne shi a kabarinsa tare da kakanninsa a birnin Dawuda.
29 Or la onzième année de Joram, fils d’Achab, Achazia avait commencé de régner sur Juda.
(A shekara ta goma sha ɗaya ta Yoram ɗan Ahab, Ahaziya ya zama sarkin Yahuda.)
30 Et Jéhu vint à Jizreël; et Jézabel l’apprit, et mit du fard à ses yeux, et orna sa tête, et regarda par la fenêtre.
Sa’an nan Yehu ya je Yezireyel. Sa’ad da Yezebel ta sami labari, sai ta sha kwalliya ta gyara gashin kanta, ta zauna tana kallo daga taga.
31 Et Jéhu entra dans la porte, et elle dit: Est-ce la paix, Zimri, assassin de son seigneur?
Yayinda Yehu ya shiga ƙofa, sai ta ce, “Lafiya, kai Zimri, mai kashe maigidansa?”
32 Et il leva sa face vers la fenêtre, et dit: Qui est pour moi? Qui? Et deux ou trois eunuques regardèrent vers lui.
Sai ya ɗaga ido ya dubi tagan ya ce, “Wa yake gefena? Wane ne?” Sai bābānni biyu ko uku suka leƙo suka dube shi.
33 Et il dit: Jetez-la en bas. Et ils la jetèrent, et il rejaillit de son sang contre la muraille et contre les chevaux; et il la foula aux pieds.
Yehu ya ce musu, “Ku jefa ta ƙasa!” Sai suka jefar da ita, jininta ya fantsama a jikin bango da kuma a jikin dawakai yayinda suke tattaka ta.
34 Et il entra, et mangea et but; et il dit: Allez donc voir cette maudite, et enterrez-la, car elle est fille de roi.
Yehu ya shiga ya ci, ya kuma sha. Ya ce, “Ku san yadda za ku yi da la’ananniyan nan, ku binne ta, gama’yar sarki ce.”
35 Et ils s’en allèrent pour l’enterrer, mais ils ne trouvèrent rien d’elle que le crâne, et les pieds, et les paumes des mains.
Amma sa’ad da suka je don su binne ta, ba su sami kome ba sai ƙoƙon kanta, ƙafafunta da kuma hannuwanta.
36 Et ils revinrent et le lui rapportèrent; et il dit: C’est la parole de l’Éternel, qu’il a dite par son serviteur Élie, le Thishbite, disant: Dans le champ de Jizreël, les chiens mangeront la chair de Jézabel;
Suka komo suka faɗa wa Yehu, wanda ya ce, “Wannan ita ce maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin bawansa Iliya mutumin Tishbe. A fili, a Yezireyel, karnuka za su cinye naman Yezebel.
37 et le cadavre de Jézabel sera comme du fumier sur la face des champs, dans le champ de Jizreël, en sorte qu’on ne dira pas: C’est ici Jézabel.
Gawar Yezebel zai zama kamar juji a ƙasa, a fili, a Yezireyel, har ba wanda zai iya cewa, ‘Wannan Yezebel ce.’”

< 2 Rois 9 >