< 2 Rois 3 >

1 Et Joram, fils d’Achab, commença de régner sur Israël à Samarie la dix-huitième année de Josaphat, roi de Juda; et il régna douze ans.
Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
2 Et il fit ce qui est mauvais aux yeux de l’Éternel, non pas toutefois comme son père et sa mère; et il ôta la stèle de Baal que son père avait faite.
Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
3 Seulement il s’attacha aux péchés de Jéroboam, fils de Nebath, par lesquels il avait fait pécher Israël; il ne s’en détourna point.
Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
4 Or Mésha, roi de Moab, possédait des troupeaux, et payait au roi d’Israël 100 000 agneaux et 100 000 béliers avec leur laine.
Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
5 Et il arriva, à la mort d’Achab, que le roi de Moab se rebella contre le roi d’Israël.
Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
6 Et le roi Joram sortit en ce temps-là de Samarie, et passa en revue tout Israël.
To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
7 Et il s’en alla, et envoya vers Josaphat, roi de Juda, disant: Le roi de Moab s’est rebellé contre moi; viendras-tu avec moi à la guerre contre Moab? Et il dit: J’y monterai; moi je suis comme toi, mon peuple comme ton peuple, mes chevaux comme tes chevaux.
Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
8 Et il dit: Par quel chemin monterons-nous? Et il dit: Par le chemin du désert d’Édom.
Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
9 Et le roi d’Israël, et le roi de Juda, et le roi d’Édom, partirent; et ils firent un circuit de sept jours de chemin. Et il n’y avait pas d’eau pour l’armée et pour le bétail qui les suivaient.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
10 Et le roi d’Israël dit: Hélas! l’Éternel a appelé ces trois rois pour les livrer en la main de Moab.
Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
11 Et Josaphat dit: N’y a-t-il point ici un prophète de l’Éternel, afin que nous consultions l’Éternel par lui? Et un des serviteurs du roi d’Israël répondit et dit: Il y a ici Élisée, fils de Shaphath, qui versait l’eau sur les mains d’Élie.
Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
12 Et Josaphat dit: La parole de l’Éternel est avec lui. Et le roi d’Israël, et Josaphat, et le roi d’Édom, descendirent vers lui.
Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
13 Et Élisée dit au roi d’Israël: Qu’y a-t-il entre moi et toi? Va vers les prophètes de ton père et vers les prophètes de ta mère. Et le roi d’Israël lui dit: Non; car l’Éternel a appelé ces trois rois pour les livrer en la main de Moab.
Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
14 Et Élisée dit: L’Éternel des armées, devant qui je me tiens, est vivant, que si je n’avais égard à la personne de Josaphat, roi de Juda, je ne te regarderais pas, et je ne te verrais pas.
Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
15 Et maintenant amenez-moi un joueur de harpe. Et il arriva, comme le joueur de harpe jouait, que la main de l’Éternel fut sur Élisée.
Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
16 Et il dit: Ainsi dit l’Éternel: Qu’on remplisse de fosses cette vallée.
ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
17 Car ainsi dit l’Éternel: Vous ne verrez pas de vent, et vous ne verrez pas de pluie, et cette vallée sera remplie d’eau, et vous boirez, vous et vos troupeaux et votre bétail.
Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
18 Et cela est peu de chose aux yeux de l’Éternel: il livrera aussi Moab entre vos mains;
Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
19 et vous frapperez toutes les villes fortes et toutes les villes principales, et vous abattrez tous les bons arbres, et vous boucherez toutes les sources d’eau, et vous ruinerez avec des pierres toutes les bonnes portions [de terre].
Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
20 Et il arriva, au matin, à l’heure d’offrir l’offrande, que voici, des eaux vinrent du chemin d’Édom, et le pays fut rempli d’eau.
Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
21 Et tout Moab apprit que ces rois étaient montés pour leur faire la guerre, et ils convoquèrent tout homme qui était [en âge] de ceindre une ceinture, – et au-dessus; et ils se tinrent sur la frontière.
To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
22 Et ils se levèrent de bon matin; et le soleil se levait sur les eaux, et Moab vit en face [de lui] les eaux rouges comme du sang.
Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
23 Et ils dirent: C’est du sang! Ces rois se sont certainement détruits et se sont frappés l’un l’autre; et maintenant, Moab, au butin!
Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
24 Et ils vinrent au camp d’Israël, et les Israélites se levèrent et frappèrent les Moabites, qui s’enfuirent devant eux. Et ils entrèrent dans [le pays], et frappèrent Moab;
Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
25 et ils détruisirent les villes; et ils jetèrent chacun sa pierre dans toutes les bonnes portions [de terre], et les en remplirent; et ils bouchèrent toutes les sources d’eau et abattirent tous les bons arbres, … jusqu’à ne laisser à Kir-Haréseth que ses pierres: les frondeurs l’environnèrent et la frappèrent.
Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
26 Et le roi de Moab vit que la bataille devenait trop forte pour lui, et il prit avec lui 700 hommes tirant l’épée, pour se frayer un chemin jusqu’au roi d’Édom; mais ils ne purent pas.
Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
27 Et il prit son fils, le premier-né, qui devait régner à sa place, et il l’offrit en holocauste sur la muraille. Et il y eut une grande indignation contre Israël; et ils se retirèrent de lui, et s’en retournèrent dans leur pays.
Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.

< 2 Rois 3 >