< 2 Rois 16 >
1 La dix -septième année de Pékakh, fils de Remalia, Achaz, fils de Jotham, roi de Juda, commença de régner.
A shekara ta goma sha bakwai ta mulkin Feka ɗan Remaliya, Ahaz ɗan Yotam sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Achaz était âgé de 20 ans lorsqu’il commença de régner; et il régna 16 ans à Jérusalem. Et il ne fit pas ce qui est droit aux yeux de l’Éternel, son Dieu, comme [avait fait] David, son père;
Ahaz ya zama sarki yana da shekara ashirin, ya kuma yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima ba kamar Dawuda mahaifinsa ba. Ahaz bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji Allahnsa ba.
3 mais il marcha dans la voie des rois d’Israël, et même il fit passer son fils par le feu, selon les abominations des nations que l’Éternel avait dépossédées devant les fils d’Israël.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila har ya miƙa ɗansa hadaya a wuta, yana bin hanyoyin banƙyama na al’ummai da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
4 Et il sacrifiait et faisait fumer de l’encens sur les hauts lieux, et sur les collines, et sous tout arbre vert.
Ya miƙa hadaya, ya kuma ƙona turare a masujadan tudu, da kan tuddai, da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
5 Alors Retsin, roi de Syrie, et Pékakh, fils de Remalia, roi d’Israël, montèrent à Jérusalem pour lui faire la guerre; et ils assiégèrent Achaz; mais ils ne purent pas le vaincre.
Sai Rezin sarkin Aram, da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su kai wa Urushalima hari, suka kuma kewaye Ahaz, amma ba su iya shan ƙarfinsa ba.
6 En ce temps-là, Retsin, roi de Syrie, recouvra Élath pour la Syrie; et il expulsa d’Élath les Juifs; et les Syriens entrèrent à Élath, et ils y ont habité jusqu’à ce jour.
A wannan lokaci, Rezin sarkin Aram ya sāke ƙwato Elat wa Aram ta wurin korar Yahuda. Sa’an nan mutanen Edom suka mamaye Elat suna kuwa zaune a can har yau.
7 Et Achaz envoya des messagers à Tiglath-Piléser, roi d’Assyrie, disant: Je suis ton serviteur et ton fils; monte, et sauve-moi de la main du roi de Syrie et de la main du roi d’Israël qui s’élèvent contre moi.
Ahaz ya aika a faɗa wa Tiglat-Fileser sarkin Assuriya cewa, “Ni abokin tarayyarka ne kuma mai dogara da kai. Ka haura ka cece ni daga hannun sarkin Aram da hannun sarkin Isra’ila waɗanda suke kawo mini hari.”
8 Et Achaz prit l’argent et l’or, ce qui s’en trouva dans la maison de l’Éternel et dans les trésors de la maison du roi, et l’envoya en présent au roi d’Assyrie.
Ahaz ya ɗauki azurfa da zinariyar da suke a haikalin Ubangiji da suke kuma a ma’ajin fada ya aika wa sarkin Assuriya kyauta.
9 Et le roi d’Assyrie l’écouta; et le roi d’Assyrie monta à Damas, et la prit, et en transporta [les habitants] à Kir, et fit mourir Retsin.
Sai sarkin Assuriya ya ji roƙonsa. Ya tashi ya fāɗa wa Damaskus da hari ya kuma kame ta. Ya kwashi mazaunanta zuwa Kir, ya kuma kashe Rezin.
10 Et le roi Achaz s’en alla à la rencontre de Tiglath-Piléser, roi d’Assyrie, à Damas; et il vit l’autel qui était à Damas; et le roi Achaz envoya à Urie, le sacrificateur, la forme de l’autel et son modèle, selon toute sa façon.
Sa’an nan sarki Ahaz ya tafi Damaskus don yă sadu da Tiglat-Fileser sarkin Assuriya. Da ya kai can sai ya ga wani bagade a Damaskus, sai ya aika wa Uriya firist, da siffar bagaden, da fasalinsa, da cikakken bayanin bagaden.
11 Et Urie, le sacrificateur, bâtit l’autel selon tout ce que le roi Achaz avait envoyé de Damas; Urie, le sacrificateur, le fit ainsi, en attendant que le roi Achaz revienne de Damas.
Saboda haka Uriya firist ya gina bagaden bisa ga tsarin da Sarki Ahaz ya aika masa daga Damaskus, ya kuma gama shi kafin Sarki Ahaz yă dawo.
12 Et le roi revint de Damas, et le roi vit l’autel, et le roi s’approcha de l’autel, et y offrit;
Da sarki ya dawo daga Damaskus ya ga bagaden, sai ya tafi kusa da shi ya kuma miƙa hadaya a bisansa.
13 et il fit fumer sur l’autel son holocauste et son offrande de gâteau, et versa sa libation, et fit aspersion du sang de ses sacrifices de prospérités.
Ya miƙa hadayarsa ta ƙonawa da ta hatsi, ya zuba hadayarsa ta sha, ya kuma yayyafa jinin hadayunsa ta zumunci a bisa bagaden.
14 Et quant à l’autel d’airain qui était devant l’Éternel, il le fit avancer de devant la maison, d’entre [son] autel et la maison de l’Éternel, et le mit à côté de [son] autel, vers le nord.
Sai ya cire bagaden tagulla wanda aka keɓe ga Ubangiji, ya sa shi a gaban haikalin wato, tsakanin ƙofar shiga haikalin Ubangiji da sabon bagaden. Ya ajiye shi a gefen arewa na sabon bagaden.
15 Et le roi Achaz commanda à Urie, le sacrificateur, disant: Fais fumer sur le grand autel l’holocauste du matin et l’offrande de gâteau du soir, et l’holocauste du roi et son offrande de gâteau, et l’holocauste de tout le peuple du pays, et leur offrande de gâteau, et leurs libations; et tu feras aspersion de tout le sang des holocaustes et de tout le sang des sacrifices sur cet autel; et l’autel d’airain sera pour moi, afin d’y consulter.
Sarkin Ahaz ya umarci Uriya cewa, “A kan babban sabon bagade, ka miƙa hadayar ƙonawa ta safe, da hadayar hatsi ta yamma, da hadayar sarki ta ƙonawa da hadayarsa ta hatsi, da hadaya ta dukan jama’ar ƙasar, tare da hadayan hatsinsu da kuma ta sha. Ka yayyafa jinin hadayun ƙonawa a kan bagade. Amma zan yi amfani da bagaden tagulla don neman bishewa.”
16 Et Urie, le sacrificateur, fit selon tout ce que le roi Achaz avait commandé.
Uriya firist kuwa ya yi duk abin da Sarki Ahaz ya umarta.
17 Et le roi Achaz enleva les panneaux des bases, et ôta les cuves qui étaient dessus; et il fit descendre la mer de dessus les bœufs d’airain qui étaient sous elle, et la mit sur un pavé de pierre.
Sarkin Ahaz ya kawar da katakon ya kuma ɗauke tasoshin daga mazauninsu da ake iya matsarwa. Ya ɗauke ƙaton kwano mai suna Teku daga kan bijiman tagullar da ya tallafe su ya ajiye a kan mazaunin dutse.
18 Et il changea, dans la maison de l’Éternel, le portique du sabbat, qu’on avait bâti dans la maison, et l’entrée extérieure du roi, à cause du roi d’Assyrie.
Ya kawar da rumfa Asabbacin da aka gina a haikalin, ya kuma kawar da mashigin sarki na waje da haikalin Ubangiji, duk dai don yă gamshi sarkin Assuriya.
19 Et le reste des actes d’Achaz, ce qu’il fit, cela n’est-il pas écrit dans le livre des chroniques des rois de Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Ahaz, abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
20 Et Achaz s’endormit avec ses pères, et fut enterré avec ses pères dans la ville de David; et Ézéchias, son fils, régna à sa place.
Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi da su a Birnin Dawuda. Hezekiya ɗansa kuma ya gāje shi.